Showing 6001 words to 9000 words out of 261814 words
cikin duniya ba basusan dandanonsa ba shine dabaibaiye da zuciyoyinsu akan mahaukaciyar arzikin da suke kallan Omar dashi Wanda basajin zai taba sauka matiqar ba sune suka kasance mallakinta ba Kokuma rabinta ma.
Tafiya zaayi da Omar sbd baturen dayayi musu alkawarin Basu irin rayuwar da suke so shi da kasim kafin rasuwar kasim din Dan haka ana rufe su kasim tashin hankalin Omar ya qaru sbd Kai tsaye su mamman sukace ba zasu bisu ba su zasu zauna anan su sake samun zinariya kafin su biyosa.
Su biyar din basu taba rabuwaba tinda suke a rayuwarsu sai wannan ranar da biyunsu suka bar duniya gaba Daya sai Kuma yanzu da zaa tafi da Omar abarsu Badan sunso ba sai Dan ana son nuna musu fin karfi.
Mr Jaden da tin farko Allah ya Saka masa kasim arai sosai fiyeda kowa a Ashalawa sbd ladabinsa da nutsuwarsa data fita daban haka kawai yaji bazai iya barin Omar ba a Nan bayan rasuwar kasim Dan yariga yayi musu alkawari hakama zuciyarsa Bata yardar masa barin Omar a tsakanin mamman da lameenu ba Dan haka baiyi tsaiko a tafiyar tasu ba duk yanda Omar ke cikin tsananin tashin hankalin rabuwa dasu mamman Amma Shima yanason cika burinsu shi da kasim na rayuwar Kwanciyar hankali da nutsuwa tareda wadatar ilimi Dan haka yabi Mr Jaden din tinda su mamman din zasu biyo Daga Baya.
Mamman da lameenu tamkar tsokar jininsu ce ake yanka ana rabasu da ita sukeji a lokacinda suke kallo Omar zai tafi da tarin arzikin da suke ganin sunada cikakkiyar haqqi akanta tinda sune sukai aikin kawar da me ita din Dan haka kukansu da baqin cikinsu na tafiyar akan Hakan ne sedai zuciyoyinsu ne kadai ke kika Banda idanuwansu da suka bushe Babu komai Dake cikinsu bayan radadin Jan bacin Rai suna kallo har Mr Jaden Dake riqe da hannun Omar ya jasa suka nufi filin da helicopter din dazai daukesu yazo ya daukesu suka bar dajin Ashalawa.
##MAMUH#
#TOOTOOHOT
#JAMAAL JEEY SEELAH
#AMEENATOU SEELAH
#ZAFIN KAI
#LOVE
#DEEP
#ROM
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*_AMEENATOU_*
_Mamuhgee_
#ZafafaBiyar
#Arewabooks@Mamuhgee
5
Lagos suka Isa da Omar Wanda tini zazzabi da ciwo me karfin gaske ya rufesa Wanda idan suka so a lokacin Mr Jaden zai iya karasa illatasa ya gudu da dibbin dukiyar Amma Sam har cikin ransa bayajin zai iya Hakan Dan take kaunar Omar din ta cikesa musamman da a bayyane mutuwar Rabin jikinsa ta tabasa wadda ba zai taba mantawa har abada ba,Dan ko Babu kauna irin shaquwa da rashin rabuwarsu tin haihuwa dole kowannensu ya rabu ciki kuwa harda su mamman duk da babu Wanda yasan sune sukai kisan.
Mr Jaden na da gidan kansa Daya mallaka a cikin garin Lagos me girman gaske Dan haka ba asibiti ya nufa dashi Kai tsaye ba gidansa dayayi kama da Akira mansion suka nufo bayan yasa ankira likitan da zaizo ya duba Omar cikin gaggawa.
Isarsu Babu Bata lokaci aka shige da Omar har Daya daga cikin dakunansa Dake sama har cikin toilet take manyan yaransa biyu Ahmed da Aron suka gyare Omar din tsaf suka tsaftace sa daga datti da jinin jikinsa da duk ya bushe.
Kusan Omar din Baya hayyacinsa Dan haka suna gama gyarasa kusan gajeran wando sabo kadai suka Saka masa sai aka kwantar dashi a lafiyayyar gadon Dake dakin tareda ragewa AC karfi suka fice daidai isowar likita da nurse namiji Daya sai Mr Jaden.
Bude musu dakin Ahmed yayi Yana matsawa gefe suka shiga.
Kallansa Dr yayi ya raunikan jikinsa sai Kuma zazzabin gaske me qarfi dayake Saka jikinsa wani irin jijjiga.
Babu Bata lokaci ya fara dubasa cikin sauri sbd ganin Yana buqatan taimakon gaggawa.
Da farko akwai inda yake buqatan dinkuna sosai a jikinsa sbd deep yanka Daya samu sosai Dan haka su aka fara duk da an masa allura Amma Yana cikin azaba sosai sedai ko motsi Baya iyawa har aka dauki tsawon lokaci sosai aka gama.
Ruwa da wasu alluran akai masa tareda rubuta maganin da zai buqata Sha suka fito akan zaa daukarwa Omar din nurse me kulawa dashi.
Bayan tafiyar su Dr sai alokacin Mr Jaden ya samu kansa Shima yaje yayi wanka yaci lafiyayyar abincin da aka jere masa su a dining ya koshi ya kunna wayoyinsa ya ringa wayoyi tsawon lokaci kafin ya shige yayi Kwanciyarsa yafara baccin Hutu.
Omar Bai farfado ba sai bayan kwana Daya da wuni Wanda har hankalin Mr Jaden yafara tashi sai gashi ya farka Kuma lafiya kalau Babu zazzabi ko wani ciwon sai raunikansa da Suma zasu warke a hankali.
Kulawa dashi sosai nurse dasu Ahmed sukai harya samu damar yin wanka da kansa yayo alwala yazo Ahmed dayake musulmi Dan uwansa ya nuna masa gabas yayi ramakon sallolin dasuke kansa duk da ba wani ilimi ko sani akan Addini suke dashi sosai ba Amma dai sunsan sallah Kuma basa tsallaketa.
Ko kafin ya gama sallolinsa tini aka shigo da abinci aka jere masa su lafiyayyu masu Kara lafiya da drinks masu sanyi kadan.
Aron ne ya shigo Shima da wasu sabbin kayan sakawar bayan wainda aka kawo masa kafin ya fito wanka.
Yana idar da sallan abincin ya kalla tareda juya idanuwansa Yana sake kallan dakin dayake ciki din Wanda Basu taba sanin akwai tsari irinsa ba duk yanda suke hararo rayuwar kudi da Jin dadi Basu dauka haka abin yake ba a zahiri.
Tamkar mace haka yaji idanuwansa sun ciko da wani irin Hawaye masu tsananin zafi da radadin rashin su kasim a duniya daidai lokacinda ya kamata su ji dadi,
Bai taba sanin samuwar arzikinsu zai tafi da jini da rayuwar Yan uwansu Rabin jikinsu ba da tini ya Dena rokarwa kansa arzikin.
Su kasim sun bar duniya basa tareda shi hakama su mamman dasuke raye a yanzu basa tareda juna,tayaya zai fara rayuwa Babu su,Suma su mamman din tayaya zasuyi rayuwa Babu shi din.
Share hawayensa yayi yana daga hannuwansa yayiwa iyayensu dasu kasim adduar dacewa da Rahama Suma su mamman yayi musu adduar Allah ya Basu abinda sukai burin samu acan Ashalawa din kafin su baro.
Miqewa yayi daidai shigowar Ahmed Wanda kaman shine Mr Jaden ya bawa Ragamar kulawa da Omar yanda ya kamata tinda sune suke Addini Daya da juna.
Kallansa Ahmed keyi Yana Dan sake fuska cikin kulawa ya sanar dashi ya taso yaci abinci sbd lokacin Shan maganinsa yayi.
Ba musu Omar din ya taso sbd su Ahmed din sun girmesa sosai Dan alama Dan zasuyi shekaru talatin su zuwa sama shikuwa a lokacin ne suke shekarunsu na ashirin zuwa da Daya.
Abincin kudi Kai tsaye zai kira abinda yake kalla a gabansa da sunan abincin,
Brown basmati rice ce da aka dafa da abubuwan da bama zai iya gane me dame bane a ciki Se brown chicken breast a jere cikin wata glass bowl daban.
Ahmed ne ya basa kwari gwiwan fara cin abincin Wanda Yana fara Kai spoon na farko bakinsa idanuwansa suka ciko da Hawaye zuciyarsa na karyewa da tino Yan uwansa su mamman ko sun samu sunci abincin Daren kuwa kokuwa ma kila suna can cikin azabar duhu da zafin ramin gurin Gina.
Ahmed Dake kallansa Yana tinanin Allah me bawa Wanda yaso,
Gasunan dai sunata Fadi tashin nema Amma ga yaro qanqani kaman Omar Allah ya basa Arzikinda zasu lalace a karkashinsa gurin bauta masa kaman bayi.
Harya ci abincin ya gama Hawaye ne ke tsiyaya daga idanuwansa da sukai jajir Babu farin ciki ko kadan a ransa Dan kuwa rayuwar da zai fuskanta Babu seelahs ko Daya a cikinta bazai taba farin ciki ba duk Jin dadin dazai samu acikinta.
Bayan gamawarsa Ahmed da kansa ya kwashe kayan ya fice dasu tareda dawowa sukai sallahn ishai a tare dakin tukuna ya fito ya sauko ya barosa ya sake samun hutawa kaman yanda Mr Jaden yace abarsa ya huta sosai ya dawo daidai tukuna.
Zaune yake shiru har kusan dare sosai kafin ya kwanta bacci ya daukesa Bai farka ba sai asuba.
Bayan sallan asuba da baisan time ba yasan dai lokaci yayi
Yana idarwa sake kwantawa yayi sbd maganinsa akwai masu Saka bacci sosai Dan Mr Jaden ya sanarwa Dr Omar din kaf rayuwarsa Baya samun baccin Daya kamata musamman a wannan lokacin shiyasa aka rubuta hadda maganin bacci.
Washe gari ma haka ya sake wuni daga cin abinci sai sallah Se bacci,
Daga Ahmed Se Aron ne kadai suke Dan shigowa Dan su Dan debe masa kewa Amma Sam Babu walwala ko farin ciki a tattareda shi.
Mr Jaden baya zama kwata kwata sbd komawa da zaiyi qasarsa Poland Kuma duk yanda yaso tafiya da Omar abin bazai yiyuba a yanzu Dan haka dole zai barsa yaje ya dawo kafin can anyiwa Omar din komai da komai na id cards da sauransu.
Kafin tafiyar Mr Jaden cikin kwana biyu yayi kokarin ganin Omar yafara sakewa sosai Dan yanason inganta rayuwarsa fiyeda yanda ake tinani,
Yanason mayarda rayuwar Omar abar alfahari ga Yan uwansa Da Kuma duk Wanda zaiyi muamala dashi,
Yanason Omar ya samu ingantacciyar rayuwar da har abada bazai taba tinani ko shaawan komawa Ashalawa Koda kuwa ziyara ne bare Dan wani abin daban Dan haka Babu Bata lokaci ya nema lawyernsa na Nan Nigeria me zaman kansa qwararre Akai rubuce rubuce akan zallan tsananin dukiyar Omar wadda kusan yawanta takusa ta dukiyar Mr Jaden din Dan haka a rubuce Mr Jaden da Omar abokanan kasuwanci ne da dukiyarsu ta Hadu tareda adadin ta kowa.
Omar ya amince da Mr Jaden dari Nisa dari sbd kasim ya yarda dashi sosai da sosai kafin ya rasu Dan haka Shima ya miqa dukkanin yardarsa ga Mr Jaden batareda Jin komaiba aka basa takardu duka ya Saka thumbprint nasa aka sealing.
Kafin tafiyar Mr Jaden duk wata sutura tin daga kan underwears da singlet da qananun kaya da manya har turaruka da mayukan da Omar zaiyi amfani dasu da takarman da zai Saka da duk wani abin buqata na rayuwa Saida aka siyosu tsadaddu masu kyau da tsari aka zuba a dakinsa Wanda yake sama babba da toilet dinsa.
Abu na farko daya bari shine zasu fara da basa ilimin Daya kamata Dan haka babban Dan amanansa Ahmed da Aron sune yabarwa komai a hannunsa Dan haka bayan tafiyarsa Id cards aka fara yi masa da passport da banki da komai sai da Akai masa kafin aka tanada malamai biyu masu kyau aka daukar masa Dan karatun da aka fara Babu kama hannun yaro.
Tin tinanin Yan uwansa na dauke masa hankali Yana rabuwa gida biyu har su Ahmed suka Bude masa wuta sosai akan karatun Wanda yakejin kaman bazai iya ba sbd Bai fara ba tin Yana kankani harya zo yafara Maida hankali sosai da sosai Baji ba Gani Dan kuwa Aron Sam Baya masa da sauki akan karatun Dan Mr Jaden ya Basu tabbacin akan karatun karsu masa da sauki ko kadan sosai yake buqatan Omar ya San kansa ya tsayu da kansa.
A bangaren Addininsa ma sosai Ahmed ke taimaka masa Dan haka ya sake zaucewa akan karatun ba wasa ko kadan.
Ahankali ahankali ya fara Bude kansa sosai komai na shiya yanda ya kamata Dan kuwa tamkar hannun sojojin koyan aikin soja aka miqasa a hannunsu Aron Babu wasa ko kadan akan lamarin nasa.
Babu ranar da Baya kewansu mamman da lameenu dasu yake kwana yake tashi a ransa sedai Babu yanda zaiyi tinda baimasan ta yanda zai ji daga garesu ba bare ganinsu dole sai ranarda Mr Jaden ya dawo shine kadai yasan Wanda zai kira a ashalawa a hadasa dasu a waya suji junansu hakama shi kadai ne Wanda yasan yanda zaiyi yakaisa ashalawa din idanma ganinsu yakeson yi gashi Mr Jaden kullum sukai waya basa tabbacin bazai dawo daukansa ba sai yafara fahimtar karatu ya iya turanci Dan haka ya sake Maida hankali sosai akan karatun.
Bayan kusan watanni masu Dan yawa rayuwarsa ta sauya cikin kankanin lokacinda baiyi tsammani ba shi kansa,
Ya sauya sosai ya samu Kwanciyar hankali da nutsuwar rayuwa duk da akwai kadaici a tattareda shi sbd daga shi sai su Aron da masu aikin gidan ne suke rayuwa,
Baya muamala da mutane sbd koyaushe Yana gida sai Kuma idan sun fita yawon Shan iska ko siyayya ko kallan ball da sauransu Wanda sosai ake kokarin yin duk abinda zai sakashi Jin walwala ko makamanciyarta.
#MAMUH#
#AMEENATOU
#DEEP
#JAMAAL JEEY SEELAH
#BLACKMONEY
#LOVE
#CRAZY
#LAHOT
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*_AMEENATOU_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
6
*_ASHNA BEAUTY SKINCARE_*
Free class free class
Assalamu alaikum yar uwa kina neman inda zaki koyi sanaa wadda zaki dugara dakanki Ashna skincare and more tazu muku da garabasa ta musamman inda zata kawu muku yanda ake hada wannan abubuwan kyauta
Carwash
Airfreshner
Liquid soap
Gamasu nemana hanyar shiga zaku nemeta ta wannan number kamar haka whatsapp only 09031383058
Karku Bari wannan damar ta wuceku
*********
Babban abinda yafara sauyawa sosai a rayuwar Omar shine harshen yare,
Daga Aron har Ahmed dayake musulmi basa Jin Hausa Daman tin farko da dubaru suke magana dashi Dan haka da karfi da yaji yaren turanci ya fara kama bakinsa Dan kuwa ko Ahmed dayakewa kallan nasa ba bahaushe bane yaren igala ne da aka haifesa a Lagos ya tashi a Lagos Dan haka tini Omar ya sake ya fada yaren turanci Shima Yana cabawa.
Sabo da shakuwa dole ya shiga tsakaninsu duk da Yana girmamasu a matsayin wainda suka girmesa su Kuma suna kulawa dashi kaman jininsu Dan kuwa Babu abinda bazasu iyawa Mr Jaden ba ko Yana kasar ko bayanan Dan shine gata da rufin asirinsu da iyalansu.
Mutum ne shi Daya inganta rayuwarsu sosai yanada alheri baida rowa Sam shiyasa suka zama Yan amanansa Dan ya dade a Nigeria shekaru sosai anan yake huldodinsa da yawansu.
******Lokaci yaja Omar tini ya kwana biyu da shiga makarantar da ake kira yaqi da jahilci wadda kusan acan kansa ya qarasa budewa yanzu ba laifi Yana iya abubuwa wa kansa da da sama wainda su Ahmed suka koyar dashi da Kuma iliminsa Daya fara basa,
Shine yake zuwa da kansa yaje ya dawo da mota batareda ankaisa ba hakama Kuma Yana zuwa banki ya cire kudi da kansa batareda wani ya raka sa ba hakama siyayyar abubuwan buqatansa,
A rayuwarsa yanzu abu biyune ya rasa masu damun zuciyarsa kowanne dare shine rashinsu mamman da lameenu a tareda shi sai Kuma rashin Mr Jaden da kusan zuwansa biyu Yana komawa batareda shi ba Amma yanzu Kam da komai nasa na tafiya ya kammala haka yayi bankwana dasu Aron ya tafi yanajin kaman ya rabu da Dan uwansa na jini
Amma Ahmed dashi suka tafi sbd shi har lokacin baiyi aure ba Bai da iyali sabanin Aron yanada family Dan haka shi aka barsa da kulawa da gidan suka koma Poland kwata kwata.
Da farko yaso ganawa dasu mamman kafin tafiyarsu Amma ba lokaci Dan haka dole Mr Jaden yayi masa alkawarin zaa kawo su Suma Nan Lagos su samu Dan ilimin shigowa mutane kafin akawosu Poland inda yake su hade suyi karatu kamansa.
Wannan alkawarin ne ya kwantawar da Omar hankali Wanda har sai dayayi magana dasu mamman da waya daga can Ashalawa suka basa tabbacin suna Nan tafe Suma sun shirya tsaf.
Farin ciki da nutsuwan zuciyar Daya samu da Jin Hakan ya Sanyashi kwantar da hankalinsa daga Dan tsoron Daya shiga na samun kansa a wata qasar wata duniyar da baisan da ita ba Dan haka gaba Daya yanzu ya kwantar da hankalinsa ya Maida akan karatunsa dayake Dan cimma buri ya samu dawowa yaje dubo mahaifiyar Kasimunsa da mahaifiyar jamilu.
A bangarensu mamman kuwa wata sabuwar duniyar rayuwar Baji ba Gani suka Bude a Ashalawa Dan kuwa gasu da kananun shekaru Amma Kuma suna cikin yan lamba Daya na rashin imanin Ashalawa da bushewan zuciya.
Duk abinda suke son samu sunata samunsa da nasu da Wanda na karfin hali ne duk sun hada sun mallaka Dan haka suka Tara wata irin danyar dukiya da Suma basusan ya zasu sarrafata ba,
Jini da rayukan da suka tafi Dan Saka hannunsu sunada Dan yawa a ashalawa Dan haka sunansu ya sake habbaka duk da Babu sauran Amma sunan seelahs Kam a Ashalawa yasake samun daguwa.
Basuda niyar barin Ashalawa sbd so suke ahankali ahankali sai sunkai sune manyan Ashalawa da zasu kwantar da Wanda sukeson kwantarwa su take su kashe.,suna son sukai sune manyan da acikin Ashalawa ko digon zinari bazata fita ba batareda izininsu ba da Kuma kasonsu.
Zuciyar mamman da lameenu ta rikide daga seelahs ta koma wata abar daban da babu Wanda ke iya gane Menene a cikinta ba sai su kadai da yanzu sunfi kowa sanin zuciyoyin junansu.
Dukiyar hannun Omar Bata taba fita daga zuciyarsu ba Kona sekan Daya Dan kuwa itace har yanzu a qasan zuciyoyinsu da basajin har abada idan ba mallakarta sukai ba zasu ji abinda yake kirjinsu ya fada.
Duk wani mataki da sukeson takawa a rayuwarsu Dan mallakar dukiyar ne wadda duk yanda suke daukan Rai baa bakin komaiba yanzu suna mallakar zinariya haryanxu Basu samu abinda yayi Koda Rabin na Omar din bane Dan haka suke sake nutso a duhun zuciya.
A ranar da sukai waya da Omar ya sanar dasu kyakkyawar rayuwar dayake gudanarwa tareda nutsuwa da tarin wadata Jin sukai gabaki Daya hankalinsu ya tashi daga Ashalawa ya koma akan samarwa kansu ilimin da zai Basu ikon mallakar abubuwa da dama daga Omar din Dan haka take suka amince da tahowa inda yake din.
Abinda Basu sani ba shine Omar yariga yabar qasar Mr Jaden ya tafi dashi Poland Dan haka bayan isowarsu sunji ciwon Hakan sosai Amma dai sunsan koman Daren dadewa zasu hade dashi Kuma abinda suke son kota halin yayane sai sun mallaka Koda abubuwa da dama zasu faru.
Aron ne mutum na farko daya fara banbance halinsu Dana Omar Dan kuwa su Babu sauki ko kadan a kulawa dasu kamanshi,
Tinda suka zo yaketa iya kokarin kulawa dasu da karatunsu sedai kwata kwata Babu sauki.
Saida suka shafe watanni suna cin banza a mansion din akai musu komai kaman yanda akaiwa Omar tin daga Id cards da passport da acct suka