Showing 66001 words to 69000 words out of 261814 words
gaba idanuwansa na Neman sauyawa Amma ya Hana hakan sbd dawowa ko shigowa mansion din seelahs wani abune dabai taba tinanin zai sake ba har abada idan ba yanzu da Dan uwansa Dake tsananin buqatansa ba.
Sedai abinda Basu saniba shine kaman yanda yayi alkawarin duk ranar Daya Sako kafarsa ya dawo musu Saiya tabbatarda sun rasa komai to tabbas tinda ya Sako kafarsa ayau din ya dawo Saiya gyara musu komai sbd Haroon kafin suna kallo ya rabasu da komai daga ranar Daya tabbatarda Haroon ya mallaki macen dayake so fiyeda komai ayanzu.
Kai tsaye bangaren Haroon ya nufa Yana amsa sannu da zuwan da securities din gidan ke masa cikin tsananin girmamawa da mamaki me girma na sauyin Haroon din.
Yana shiga palon Haroon Kai tsaye bedroom dinsa ya wuce ya shige toilet alwala yayi ya fito yayi Sallah Yana idarwa wayar Dad na shigowa wayar Dake gefensa.
Kallan wayar yayi tareda dagawa cikin nutsuwa yayiwa Dad din gaisuwan Data Saka kirjinsa mummunan bugawa Saida yayi shiru ya sake sauraron muryan da kyau yaji sai yaji Yana Neman rudewa sai kawai yayi Watsi da abinda yaji Kai tsaye ya Bude Baki yace
"Ka sameni yanzu a office din cikin mansion din."
"Ok" kadai Jamaal yace tareda rigan Dad kashe wayan Wanda ya sake Saka Dad din mamakin halayen da Haroon ya fara sauyawa.
Saida yaci abincin da siddeeq yayi masa ordernsa daga tsadaddiyar restaurant ya koshi kafin ya shirya ya fito tareda siddeeq Wanda shine yake nuna masa hanyar da office din yake tinda Bai saniba.
Suna kaiwa kofar office din siddeeq ya tsaya daga waje Jamaal Kuma Kai tsaye ya Bude kofar a natse zai shiga sako ya shigo wayar Haroon Dake hannunsa Kuma Kai tsaye yasan Haroon dinne Dan haka ya dakata tareda duba sakon Daya bayyana akan screen din wayar inda ya rubutu masa tini tareda rokonsa akan yayi masa alkawarin ganin aurensa da Ameenatou ya tabbata kaman yanda tin farko yayi masa wannan alkawarin zai tabbatarda shi din Bai rasa macen da itace farin cikinsa ba kaman yanda shi Bai samu tasa farin cikin ba.
Lumshe fararen idanuwansa yayi da suka fara sauyawa Yana sake Tina alkawarin da yayiwa Haroon din zai tabbatarda su Dad da hannunsu sun aura masa Ameenatou kafin yabar kasar idan har auren Bai tabbataba to Allah ne yayi su din ba ma'auratan bane Kokuma Idan dayansu Baya raye wannan shine abinda mum dinsu ta roka daga Jamaal din sbd bazata so Shima Haroon dinta ya dandani irin radadin da Jamaal ke cikinsa haryanxu ba na Rasa Macen da ita kadai ya bawa zuciyarsa.
Numfashi me sanyi ya sauke ahankali mara sauti kafin Kai tsaye ya shiga batareda knocking ba kaman yanda Haroon yakeyi kafin shigan.
Yana shigowa Dad Lameenu dayake facing kofar ne ya zuba masa idanuwansa Yana kallo cikin Dan mamaki kafin Shima Dad din ya dago Yana kallansa Dan dukkanin idanuwansa mamakinsa a bayyane,
Dad Lameenu Daya rasa abin fada cikin yar rikicewa yace
"Da Jamaal Yana kasar Nan da babu abinda zai hanani tinanin shine a gabanmu,
Haroon hankalinka kuwa kake mayarwa akan aikin gabanka kokuwa gyaran fata ka mayarda hankali Akai sbd mace??
Dad da har lokacin idanuwansa na kan Jamaal din Yana Jin zuciyarsa na kokarin dawo masa da kewan Jamaal da tsananin buqatansa dayakeyi Kuma sai zuciyar ke Jin kaman ta samu Jamaal a gabansa Amma Kuma yasan abune da bazai taba yiyuwaba Dan Koda Jamaal Yana Nigeria ya shigo bazai taba Sako kafarsa SEELAHs ba Dan haka duk yanda idanuwansa ke nuna masa kaman Jamaal ne gabansa bazai yiyuba Dan haka ya dauke idanuwansa daga Jamaal din Yana sauke numfashi ahankali Shima Jamaal din sai alokacin ya ya dago ya zuba musu idanuwansa da suka sauya sosai sedai Bai furta komai ba Dan maganarsa a lokacin zata bayyanarda radadin ganinsu kawai Dake cin zuciyarsa Dan haka ya zabi yin shiru kaman yanda Haroon keyi a gabansu.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
43
A cikin murya me nutsuwa Kai tsaye ya gaidasu Dad din acikin jam'i batareda ya Bada amsar maganarda Dad Lameenu ya jefesa da ita ba ta farko.
Dayake dukkaninsu kowa da abinda yake bakinsa na maganar Dake cinsu Basu tantance sauyin muryanba Wanda Daman Shima Haroon idan jikinsa na Sanyaye muryansa a natse da sanyi take fita Dan haka Babu Wanda ya tsaya amsa gaisuwan bare tambayar ya jikinsa Kai tsaye Dad dayaji Baya iya kallansa Dan yau din cika masa ido Haroon keyi sbd kamanninsa da Jamaal sun tsananta ayau dayake ganinsa kaman Jamaal Dan haka batareda y kallesa ba murya a daure da bacin ran abinda yayi yace
"Ko zaka bani dalilanka Daya Saka bawa project dinmu da ma'aikatan aikinsa Hutu harna kwana uku batareda sanar damu meyake faruwa ba??
Numfashi me sanyi ya sauke Yana dauke idanuwansa daga kallansu kafin ya Tako ahankali dukkaninsu sukai saurin kallansa ganin ya tinkarosu Yana kallansu Dad Lameenu ne yayi saurin cewa
"Amsar abinda yake faruwa muke buqatan Dani sbd Haroon Banga alamar zaka cika alkawarin daka dauka ba na sakamu alfahari dakai,
Aikin Nan fa duka duka sauran sati uku ne a time dinsa ya cika,.
Dad kallansa ya sake yi Yana Jin zuciyarsa na son shiga tinani daban daban Amma ya watsar Yana cewa
"Karka manta nutsuwanka akan aikin Nan shine tabbatan aurenka Dan Neman aure ba shine aurenba Karka manta da Hakan Dan nakai maquran rashin nutsuwan Nan taka,
A Hakan kake Neman mutuwa sbd mace kanason kayi aure batareda kasan ciwon kanka ba bare tinanin tsayuwa ka zama abin alfahari ga iyayenka ba tayaya zaka tsayu ka zama abinda matarka ko yayanka zasuyi alfahi dashi....
Dakatawa Jamaal yayi daga inda yake tsaye tareda dago idanuwansa da sukai ja ya Kalli Dad din dashi ma shi ya Dan kalla Yana cewa
"Yes, Haroon haryanxu ka kasa sakani farin cikin Da kowannen Uba yake shiga akan yayansa da alfahari dasu,
Alkawari nayi Maka akan idan kasakani farin ciki akan wannan aikin zan nema Maka auren da kakeso Amma......
Katsesa Jamaal yayi Dan bazai iya tsayawa sauraron wainnan maganganun akan Dan uwansa ba komai zai iya faruwa Dan zai iya bayyanarda kansa Dan haka wayarsa ya daga ya kira siddeeq take siddeeq ya shigo da takardun komai dasuka gama a yau din ya karba daga hannun siddeeq ya ajiye gaban Dad din Yana kallansa yace
"Gashinan Alkawarin zan cika Maka acikin kwanakin da bazasu kai na cikan kwanakin ba Amma Kuma a ranar da komai ya tabbata a yanda kakesonsa a ranar nakeson a daura mun auren da yarinyar....."
Daga dad har Dad Lameenu sakin Baki suke kokarin yi gurin kallansa da mamaki hankalinsu na rabuwa biyu daga abinda ya fada da Kuma karanta takardun Daya zuba a gabansu suna karantawa cikin tsananin mamakin sabuwar project din data dawo musu Da cikakkiyar damansu a hannunsu.
Dad Lameenu Daya kasa Kai karshen takardan cikin farin cikinsa Daya mantar dashi mamakin dasuka shiga yace
"Nayi Maka alkawarin daura Maka auren Ameenatou a washe garin ranar da Akai bikin Budewa duniya wannan aikin project dinnan Haroon idan abinda nake Gani da suna SEELAHs a jikin takardan Nan ya bayyana.
Dad ma mamakin ne yayi mugun kashesa kafin idanuwansa su sauka kan signature din jamaal Dake karshe wayarsa tayi ringing daga turawansu na Abujan ne Yana dauke idonsa Akai siddeeq ya matso Yana rufe file din tareda amsar masa cikin girmamawa Dan basa Daman amsa wayan wadda ta Saka Dad Lameenu washe dukkanin bakinsa cikin tsananin farin ciki Yana sake tabbatarwa da Haroon zuwa wani sati zai tabbatarda Abdul yayo parking da familynsa sun iso Lagos din gaba Daya.
Wayar da Dad keyi ta sakashi Shima dukkanin farin cikinsa bayyana Yana washe Baki Yana wayar cikin turanci Dan nutsuwa Yana Kuma Basu tabbacin wannan Karan Inshallah komai zai tafi daidai Nan da 3 zuwa 4 weeks komai ya zama cikin Shirin bikin qaddamarwa.
Dad na gama wayar Haroon din ya kalla cikeda farin ciki yace
"For the first time da yau nake alfahari dakai Son"
Kalman zafafa zuciyar JAMAAL tayi Dan haka baice komaiba sai sake fuska da yayi ya amshi zancen Dan kawai da zargi.
Buga kofar Akai kafin aka Bude tareda shigowa
BB ne Wanda duk kwakwalwansa take Neman Juyewa sbd ba dare ba Rana a bincike da yawon garuruwa suke da kauyuka gurin Neman da haryanxu Babu me baccin arziki akansa tsakanin shi dasu Mam din.
Tinda yake a rayuwansa wannan shine aiki mafi wahalan dayakesha mara sauko ko kadan a duk shekarun Nan,
Shi kansa sbd baqar wahalan dasuke Sha a wannan aikin yakejin bazai taba samun nutsuwa ko Kwanciyar hankali ba matiqar ba Gano abinda suke Neman sukaiba kaman yanda yasan har abada uwayen gidan nasa bazasu taba samun baccin nutsuwa da Kwanciyar hankali ba idan ba burinsu na shekarun cika yayi ba.
Cikin girmamawa yace
"Sir Haroon barka da dawowa"
Batareda Jamaal ya amsa ba Dad Lameenu ya Kalli siddeeq Wanda Shima Kai tsaye ya juya daga office din ya fice tareda Turo musu kofar.
iPad din hannunsa ya ajiye gabansu tareda bayanan daya samo akan bincikensu ya fara da cewa
"Ranka ya Dade na samu tabbacin 'yayan matar sir Omar Daya gudu da abinda ta haifa a daren yanada nasa 'yayan guda biyu Kuma dukkaninsu Maza ne sedai Kuma matarsa an bani tabbacin kafin barinsu gombe a wancan lokacin ta haihu Wanda nakeda tabbacin ba haihuwa tayi ba babyn sir Omar dinne"
Cikin zaquwa Dad Lameenu yace
"Bayanin inda suke shine babban abinda muke buqatan Jin idan an samo"
Hakama Menene asalin abinda aka haifa din?
Mace ne ko namiji??
Hakurina da bugawan zuciya akan wannan lamarin ya kusa kamani BB a gaggauta samo mana inda suke sbd tashin aikinmu yau da aka samu shi kadai bazai riqe mana matsayinmu da tsagwaran dukiyar da muka rasa ba muna tsananin buqatan dukiyarmu Dake hannun Omar.
Dad da Shima abinda yake ransa kenan ya Kalli Haroon dayake tsaye har lokacin gabansu Yana kallan fuskokinsu da bakinsu yace
"Haroon ya qara muku kudin Daya kamata banason aurensa yazo duk tsanani duk wuya batareda an samo mana inda suke ba,
Idan Kuma bamu samo Hakan ba to tabbas lokacin zuwansa garemu yayi Dan bazai taba yiyuwaba ayi auren 'dana dayake matsayin dansa batareda yazo ba,
Zuwansa Nigeria kuwa ba abune da zai taba yiyuwaba yazo ya tafi batareda ya kaiwa abinda ya Haifa da cikinsa ziyara ba Wanda shi da kansa zai kaimu ga Magajinsa batareda ya saniba.
Kallan Haroon ya sake yi Yana sake cewa
"Ka Basu duk adadin kudaden da suke buqata kaje ka fara Shirin aurenka Dan daga lokacinda Omar ya sauka a Nigeria dukkanin motsinsa a tafin hannunmu zai zama."
Gyara Kai Jamaal yayi Yana kallan BB dayakejin bazai iya barinsa ya sake ahakan iskan yanci ko Daya ba Amma Kuma Yana buqatan sanin abinda yake faruwa kafin komai Dan kuwa zantukansu sun Saka kansa daukan zafi.
Gyada Kai BB yayi Yana Jin nutsuwa da farin cikin Suma wahalallen burinsu ze Kai karshe sbd a saukake ma auren Haroon din zai kawo Omar har gida Kuma zuwansa kaman bayyanar abinda yake boye ne.
Maganganun sauran ayyukansu dasu BB din keyi ne suka fara Kai tsaye tareda tambayan huldan datake hannun BB din da yaransa ya tabbatar musu da komai Yana tafiya lafiya kalau duk da an kama wasu yaransa Amma ya tura yaronsa Daya Daya bari aka kamasa aka Saka cikinsu Sbd ya hanasu fadan komai sedai aka wayi gari sun rasu dukansu su biyu sai shi Dayan yaron nasa sun fito dashi Dan haka Babu matsala Tako ina.
Juyawa Jamaal yayi ya fito idanuwansa basa ganin gabansa sosai sbd Ja da tashin hankalin Daya tsinci kunnuwansa daji batareda ya tsaya jin sauran abubuwan da hankalinsa yake Neman kasa dauka duk da ya Dade da sanin ba imani a lamarinsu Dad bare tausayi sbd abinda sukaiwa fadila da har yanzu baida sheda ko tabbacin sune sukai Amma ayau da kunnuwansa Yana Jin abubuwan da baisan tayaya ma zaace sune suke aikatawanba,
Haroon ya San dukkanin wannan abin dayake faruwa kenan ya boye masa tinda gashi suna maganar a gabansa batareda sanin ba Haroon dinne ba.
Yana fitowa Kai tsaye mota ya nufa Yana miqawa siddeeq hannu ya basa key batareda ya Juyaba,
Kirjinsa yake Jin ya toshe masa Babu iska ko kadan Babu abinda yake buqatan so kaman ya fita daga Mansion din.
Siddeeq na ganin Hakan ya miqa masa key din motar Haroon Daya fito dashi Dan fitarsu idan sun gama.
Saida siddeeq ya nuna masa motar ya nufi inda take tin kafin ya Isa ya Budeta Yana Isa shiga kawai yayi ya tayar da reverse ya fice daga Mansion din Yana saukar da duka glasses din motar sbd iska ta shigesa.
Yana ficewa siddeeq ya Ciro wayarsa Yana shakkar abinda ya faru daga cikin office din Amma dai koma Menene Haroon Yana buqatan sani Dan dawowa sbd ansamu matsala ga dukkanin alama.
Su Dad kuwa farin ciki da zaquwan auren ne gaban Daya ya mamayesu sbd ga dukkanin alama sanadiyar auren zasu samu abubuwa da dama dasuke so suke fata,
Haroon ya fara zama abin Alfaharin da zai sake fitar da sunan seelahs da tsayuwarsu hakama dawowan Omar dasuke fata ta sanadin auren da dole zaizo ko Dan Yan jarida dazasu yada maganar auren koina da rashin zuwansa auren 'dan farko da zaayi a Seelahs din tinda na Jamaal kaman auren boye ne da ba kowa ya saniba Amma wannan da kansu zasu Kai masa gayyata ta musamman da matsayin zamansa wakilin ango da zai karba auren da hannunsa.
******Haroon dayake tareda mahaifiyarsa tana jinyarsa cikin tsananin so da kauna da kulawa tareda tattali Jin yayi zuciyarsa ta karaya Da yanda tin farko ya zabi mahaifinsa akan mahaifiyarsa,
Bata taba nuna masa banbanci tsakaninsa da Jamaal ba sedai shine Karan kansa ya zabi mahaifinsa akanta sbd sonsa dayakeji cikin ransa fiyeda komai.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
44
Mum Aleena datake Jin batason sake rabuwa da 'danta sbd halinda yake ciki na tsananin buqatan kulawansu dan sai sunyi da gaske zasu iya rabasa da depression din Daya kamasa,
Drug kuwa da suka samu a jininsa Basu sanar masa ba itada Jamaal sbd sunason tantance shine yake Sha da kansa kokuwa sbd sun kasa yadda ko sanin tayaya zai zama Yana Shan kwayoyi irin wainnan.
Siddeeq Kuma ya tabbatar musu da Babu kwayoyi mayen ko makamancin Hakan da Haroon yake Sha Amma Kuma duba da depression dayake ciki da tsananin matsi a Hannunsu Dad zai iya samun kansa da Shan kwayoyin Dan samun fita hayyaci ya Dena Jin komai.
Tin daga ranar da Haroon din ya taho aranar ya ringa yiwa mum din kuka kaman karamin yaro cikin ciwo da tsananin buqatan again Dan uwansa akan bayason rasa Ameenatou kaman yanda ya rasa fadila,
Shi a yanzu ba yabon mahaifinsa yake nema ba Ameenatou kawai yakeso a rayuwarsa.
A gaban Mahaifiyarsu Jamaal ya Sakasa sukaiwa juna alkawari.
Idan Haroon yayi masa alkawarin dawowa ga mahaifiyarsa Dan samun lafiyansa da rayuwar nutsuwa da Kwanciyar tare Kuma da cika burin Mum dinsu na ganin yayanta duka biyu a tareda ita to shi Kuma yayi alkawarin zuwa ya gyaro dukkanin abinda Haroon yakeso Dan samun yabo daga Dad dinsa da Kuma zama abin alfaharinsa tareda tabbatar da aurensa da yarinyar Amma ana daura auren zasu taho tare.
A daidai wanna gaban Babu abinda Haroon bazai iya yiba akan samun Ameenatou da samun nutsuwan zuciyansa data Dan uwansa da mum Dan haka ya amince da dawowa cikinsu gaba Daya bayan auren take mum ta rungumesa cikin farin ciki da Jin dadi sosai tana Jin kaman tinda ta haifesa sai yanzu ne zata samu zaman datakeson yi da 'danta hakama zata kaman yanda ta kaunaci fadila take taji tana kaunan Ameenatou har cikin ranta duk da Bata taba ganinta ba Amma tayi masa alkawarin inshallah da ita zaayi aurensa.
Daman ba wani zama zasuyi a Poland dinba Nigeria zasu taho sbd bikin auren Da Haroon din kwata kwata yaji Baya son a dauko lokaci ayi kawai ya tahowansa kusada mahaifiyansa Dan haka sauki kawai sukeson ya Dan samu su taho saiga Kiran siddeeq Wanda ya sakashi shiga fargaba da tsoron abinda Jamaal yaji Dan haka shine ya dagawa mum hankalin komawansa baima jirata ba washe garin ranar ya Siya ticket dinsa ya tahowansa Dan bayason abinda zai janyo fushin Jamaal ya lalata masa komai adaidai lokacinda ake gap da samun abinda yakeso.
Jamaal kuwa a ranar Bai kwana a Lagos ba ya wuce Abuja tareda siddeeq ko su Dad din Basu saniba Dan idan Yana ganinsu zuciyarsa kasa riqe koshi waye din takeyi gwara ya tafi ya Jira zuwan Haroon Daya San duk inda yake idan har baida gaskia Yana hanyar dawowa.
Kwana Daya saiga Haroon din ya diro Amma Bai yadda ya Hadu da Jamaal din ba Kai tsaye Nasarawa ya wuce sbd bayason suyi hayaniya Kuma baisan Menene yaji bama tukuna bare yasan ta inda zai fara.
Da yamma sosai ya iso Dan haka wanka da sallah kawai yayi Bai tsaye komaiba ya wuce gidan Babbah.
Zaune suke a tsakar gidan sai lallabata dadah keyi sbd taqi Shan magani daga ciwon Kai zazzabi ya maqale kwana biyu anata fama da ita.
Zuwansa ya Saka Abdul sakin ajiyan zuciya hakama Hafiz Babbah Baya Nan
cikin sakewan fuska da nutsuwa ya qaraso Hafiz na janyo masa kujeran zama Yana masa barka da zuwa.
Yaya Abdul ya fara bawa hannu suka gaisa cikin tsananin kulawa Yana tambayarsa kwana biyu ko numbernta Baya shiga.
Murmushi ya sake Yana cewa aikin dayake gabansa ne ya sakashi kashe dukkanin wayoyinsa sbd aikin ya koma babba fiyeda yanda suke tsammani.
Gurin dadah ya Maida kallansa Yana gaidata cikeda girmamawa da kulawa kafin idanuwansa suka koma kan Ameenatoun Dake zaune sanye da Riga da wando na bacci ko hula Babu a kanta ko inda yake Bata juyo ta kalla ba maganinta take kokarin Sha tana kasawa sbd batason magani ko kadan.
Hafiz Dayafi kowa shiga damuwan bayan Ameenatou tambayarsa siddeeq yayi suna sake shiga wata firar Amma gaba Daya hankalinsa