Showing 24001 words to 27000 words out of 220972 words

Chapter 9 - DAN MACE COMPLETE Hausa Novel

23 Aug 2025

1200

min,na ji sunan yamin dad'i sosai",bata d'ago ba tace "Treasure of noor",tace "gaskiya na gode,but nace ba.. Za ki iya min kyautar baby'n ina sonsa sosai",murmushin k'arfin hali tayi ta d'ago kanta dake k'asa tace
"Wannan shi ne farin cikina,amma tunda kina sonsa na baki"
Murmushi nurse d'in tayi cikin jin dad'i tace "Kai amma gaskiya na gode sosai,kyautar baby sukutum,Allah dai ya k'ara muku lafiya Maman baby"
Hauwa tace "amin'',tana zaune nurse d'in tana mata hira tunda ta kula tana cikin damuwa,har ta rubuta sunan tace mata "kinga sunan yayi.!?"
Da kyar Hauwa ta sake d'aga kai ta kalli takardar,ganin *NURAZ RAFEEK* a jiki bar'o² wasu hawayen suka sake taho mata,da sauri ta girgiza kai tace "A'a" kasa fahimtar abunda take nufi nurse d'in tayi har ta matso kusa da ita tace "bai yiba kenan sunan.!?" Ta gyad'a mata kai "me za'a rubuta to.!?" Sai data share hawayenta tana sake kallon yaronta dake kwance cikin incubator jikinsa duk anyi connecting na'urori yana bacci tace
*"NURAZ BIN HAUWA."*


*#Posting abun so ga reader's,#Comments abincin writer's,mu daku kamar k'waryar sama dana k'asa ne,idan akwai d'aya babu d'aya al'amarin baya tafiya dai²,it's better ace mun faranta ran wad'anda suke k'aunar mu fisabilillah.!*


#Share.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*


*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥



*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2


Pᴀɢᴇ 8.
#Hᴜᴍɪʟɪᴀᴛɪɴɢ

Kallonta nurse d'in ta dunga yi kamar taga bak'uwar halitta,can da taga ba zata iya shiru ba ta janyo kujera ta zauna tana kallon Hauwa tace
"Dan Allah kiyi hak'uri y'ar uwa idan har maganata zata sa kiji babu dad'i" da kai Hauwa ta amsa mata saboda kukan da take har a lokacin yak'i bari tayi magana,nurse d'in tace "Idan babu damuwa can we be a sister's so that sai muyi maganar a matsayin y'an uwa ba mai kula da yaro ba.!?"
Hauwa ta sake kad'a mata kai,godiya tayi mata sannan tace "dan Allah mene ne dalilin da yasa kika ce asa masa sunanki al'halin na san yana da mahaifi.!?"
Sai da tayi k'ok'arin tsayar da sababbin hawayen dake sake taho mata sannan tayiwa nurse d'in tak'aitaccen bayani akan matsalolin da suka samu wanda sune silar da suka janyo musu fad'awa mawuyacin halin da suka tsinci kansu a ciki,da ta samu ta d'an fad'awa nurse d'in,wacce lokaci d'aya taji har zuciyarta ta aminta da ita,wani irin kuka take tunda ta samu ta fitar da maganar daga ranta,burinta kenan a lokacin yadda take ciki damuwa ta samu wanda zata fitarwa da maganar ko zata huta da rad'ad'in dake addabarta,tausayin Hauwa da baby yasa nurse bata gama jin labarinsu ba sai da tayi musu hawaye,tana kallon Hauwa bayan sun gama maganar tace "kada ki damu yar uwata,in sha Allah komai mai wucewa ne,,da yardar Allah lokaci zai zo da Rafeek zai neme ku duka,a lokacin zaiji kunyar wulak'anta kyautar da Allah yayi masa,in Allah ya yarda sai Yaron da nuna baya k'auna ya zame masa jigon da bazai tab'a samun kamarsa ba a rayuwa,,fatan da zan masa shi ne Allah ya nuna masa hanyar gaskiya komai tsayin lokaci..",sun jima sosai nurse d'in tana mata hira saboda tana son rage mata damuwa,da Hauwa zata tafi nurse d'in ta fad'a mata sunanta *AAEDAA* Hauwa ta mata sallama ta koma room d'in da take,da yake duka a ward d'aya suke,tana shiga d'akin su Hajiya suna zaune tun fitarta suna hira da Maimunatu,tayi sallama suka amsa ta wuce saman gado ta kwanta tayi shiru bata sake magana da kowa ba,,bayan wani lokaci Hajiya taje ganin Yaro ta tarar da abunda Hauwa tayi,tazo tana mata fad'an me yasa zata yi haka,al'halin kowa yasan Yaro nasu ne ita da Rafeek.? Babu kunya Hauwa ta fashe da kuka but ta kasa magana,Hajiya jikinta yayi sanyi ta matso ta rarrasheta,Hauwa tayi shiru cikin sanyi da lallami Hajiya ta tambayeta ko me yasa tayi hakan.? Bata b'oye ba ta sanar da Hajiya kaf abunda ya faru a ranar da incidence d'in ya faru,Hajiya taji bak'in cikin abunda ya faru musamman sakin da Rafeek yayi,amma da yake babu yadda za tayi tunda ya riga ya yanke hukunci tace "ai shi kenan,kansa ya cuta ba ni ba,Allah ya baki lafiya daughter,kiyi hak'uri da duk abunda zai faru,in sha Allah tunda yace baya son yaron nan sai ya zama mafi k'ololuwar alkhairi a rayuwarsa,da yardar Allah zai yi nadamar abunda ya aikata a nan gaba" a zuci hauwa tace "Allah yasa"
Hajiya dake rike da ita tace "maza kwanta ki huta kinji,Allah ya k'ara muku lafiya",da Alhaji yazo duba su shima lokacin da Hajiya ta fad'a masa ya ji bak'in ciki sosai,har yaji ina ma ace yana da wani d'an namiji,da a yau ya d'aura musu aure da Hauwa ko dan ya huce takaici da kunyar da Rafeek yasa shi ji,sai dai da yake y'ay'an duka guda biyu ne Allah ya azurta su da su bayan wanda suka binne guda uku,biyu b'ari d'ayan kuma an haifeshi rayuwar ce da Allah bai nufa zaiyi mai tsayi ba shi yasa tun yana jariri ya karb'i kayansa,Alhaji ya yiwa baby khud'ba da suna *NURAZ* kamar yadda Hauwa ta zab'a,,a kullum duk wanda zai d'auke ka tunda aka yi haihuwar duk da babu wanda ya san abunda yake faruwa har lokacin,addu'ah yake Allah yasa ka kasance haske ga mahaifiyarka kamar yadda ta ambaceka,,bayan shafe kwanaki da aka rik'e ku a hospital aka sallamo ku muka dawo gida,Hajiya taci gaba da kula da ku,kullum rana tunda kuka fito daga hospital na kasance ina tafe akan hanyar gidana da gidan kakanninka ba dan komai ba sai dan na duba yaya kuke,har Allah yasa duka kuka samu lafiya,kamar yadda kullum ake sake samun ci gaba,kana girmanka da wayo,Hauwa kuma ta koma shiru ta daina hira da kowa kullum cikin keb'e kanta take daga idanun mutane.

*Ina labarin RAFEEK..!??*

B'angaren Rafeek (mahaifinka) kam tun daga wannan tafiyar da ya bar gida cikin fushi,sai ya kasance bai sake waiwayen gida ba,a waya idan an kira babu wanda yake samunsa,shima kuma baya kiran kowa,,tun ranar da Hauwa ta haihu da Hajiya ta buga waya ta fad'a masa,ya daure yace "Allah ya raya" daga haka har ta gama maganar da zata yi bai sake cewa komai ba,lokacin da suka samu labarin abunda ya faru tsakaninsu a bakin Hauwa Alhaji zakar ya kirashi yayi masa tas,shi ne ya sake jin haushin Hauwa akan ta had'a shi fad'a da mahaifansa suna ganin laifinsa,suna gama waya a lokacin gaba d'aya ya cire sim cards d'in ya canja wasu,a cewarsa tunda sun zab'i zama da ita suje suyi ta sonta,shi ya hak'ura zai zauna a nan har zuwa sanda zasu gane gaskiyar abunda yake son su fahimta.
Zamansa a k'asar bayan y'an wattani ya kama aiki da yake lokacin ya kammala karatunsa,cikin hukuncin ubangiji tunda ya fara aiki da skul d'in da yaje karatun a matsayin lecturer a b'angaren Economics,ko shekara bai kai da farawa ba world bank suka yi sanarwar neman kwararru a b'angaren Economics,da yake harka ce ta kwakwalwa kuma Alhamdulillah Rafeek yana da k'ok'ari sosai tun kafin yaji labarin wasu abokansa da suke tare a k'asar suka shawarce ko zai gwada sa'ar sa,ya tura details d'insa through mail da suka bada,bayan turawa Rafeek ya duk'ufa addu'ah ba da wasa ba,tunda ya tura yake jiran amsar su still yana ci gaba da aikinsa,a weeks later da tura details suka masa replying idan ya shiryawa special exam d'insu ya tuntub'e su duk lokacin daya samu damar shigowa k'asar,cike da farin ciki lokacin da yaga sak'on ya tattara komansa a satin ya bar k'asar bcos dama zaman k'asar ya isheshi taurin kai ne yasa shi zama,ya tura takardar ban hak'uri ga hukumar collage d'in da yake aiki ya ajiye musu aikinsu,lokacin da jirginsu yayi arriving a babban birnin *WASHINGTON* charter taxi ya samu da zai kaishi masauki,ya samu hotel mafi kusa da 1818 street ya sauka,,kwana biyu da zuwansa k'asar bayan ya huta sannan yayi shirin tunkarar world bank headquarter,daga hotel d'in daya sauka zuwa headquarter babu wani nisa sosai,duka baifi mutum ya taka da k'afa ba,,a cikin sama da mutum d'ari daga k'asashen duniya mabambanta Rafeek becomes *CONQUEROR* bayan special exam da suka yi,ya samu damar zamowa d'aya daga cikin ma'aikatan su,,yanayin gogewarsa a b'angarensa cikin tak'aitaccen lokaci da kama aiki ya zamo wani jigo a gurinsu,tunda ya fara aiki ya rik'e aikinsa da gaskiya babu wasa,ci gaban rayuwa ya kasance yana zuwa masa a kowane yini like brightening burning light,a gefe guda tunanin gida da mahaifansa kullum yana mak'ale da zuciyarsa,but a ganinsa har lokacin tunaninsa shi ne ya basu lokaci da yake ganin idan har basu nemesa ba shi zai koma musu a lokacin da zai gama duk wasu shirye² na korar Hauwa daga gidan.

Har aka shekara guda da watanni da haihuwarka babu wanda yasan duniyar da Rafeek ya shiga,wayoyinsa idan an kira ba'a samu,anbi sahunsa k'asar ana tunanin ko wani abu ya same shi ba'a same shi ba sai labarin tafiyarsa birnin Washington aka tsinto,ran Alhaji zakar ya sake b'aci,a lokacin daya fahimci nufin Rafeek ya yanke hukuncin babu ruwansa da shi daga nan har zuwa ranar da zai dawo,,a wannan d'an tsakani da aka samu na haihuwarka al'amura suka yi ta faruwa,nima nawa gefen Allah ya karb'i rayuwar mai gidana,hatsari ya runtsa da su a hanyarsu ta zuwa lagos,,Hauwa da kai har lokacin kuna gidan kakanninka,duk da a farkon dawowa ta gida naso ku dawo gurina mu zauna tare a gidanmu tun bayan dana gama iddah,but yadda Alhaji zakar da iyalinsa suka tsaya kan al'amuran ku da kunya irin ta bafulatani yasa sai na kasa fitowa na fad'i abunda ke raina,haka nayi ta zuba ido kullum a gurina kake wuni,har Hauwa suka fara k'ok'arin yin exam zuwanta bai dai²ta ba sai Maimunatu kad'ai take zuwa wasu lokutan saboda damuwar da take ciki ya fara affecting tunaninta,,a wata ranar Talata da rana bayan sun dawo daga hospital suna zaune a parlor Maimunatu na bawa Hajiya labarin matsalar da doctor yace zata iya samunta nan gaba kad'an idan bata ragewa kanta damuwa ba,Hajiya tana mata nasihar ta maida komai ba komai ba,suka tsinkayi sallama daga bakin entrance,shiru duka suka d'auka Maimunatu na kallon Hajiya cikin tsananin mamaki tace
"Hajiya kamar muryar Yah Rafeek ko.?"
Kallonta Hajiya tayi tana had'e rai tace "ban sani ba,sai dai ki duba ki gani"
Hauwa ta shiga rud'ani da tunanin anya shi d'in ne da gaske tunda gaba d'aya lokaci ya tafi da tunanin baza ta sake ganinsa ba,Maimunatu ta daure ta amsa sallamar,tun kafin taje ta duba a bashi izinin shigowa ya bayyana,yana sanye cikin shiga ta alfarma d'an gayu da shi ya had'e cikin wani d'anyen suit mai matuk'ar tsada daya fito daga company'n armani,duk wanda ya kalleshi dole ya sake dan yadda ya dawo tun daga kan tsarin outfit da gyaran kansa sak bature,gaba d'ayansu kallonsa suke yi da wani irin mamakin dama yana raye a cikin duniyar,fuskarsa babu wanda ya kasa shaida ta tunda shi d'in ba bak'o bane bare ace sun kasa tantance shi,ya tsaya gaban Hajiya yana niyyar durk'usawa ya sake tabbatar msusu lallai Rafeek d'in ne da gaske,to amma yanayin sauyawar da yayi da irin tufafin da ke jikinsa yasa suke ta binsa da kallo,shi kam tunda ya shigo babu wanda ya kalla a cikinsu Maimunatu fuskarsa nan a d'aure kamar wanda yayi gamo da mutuwa,kansa a k'asa ya tunda ya durk'usa ya magana,yanayin yadda yayi shi zai tabbatarwa da duk wani mai ido lallai ya aikata gagarumin laifin da yake son neman yafiya,but kamar wanda ya rasa baki haka yayi ta zama da sunkuyayyen kai ya kasa d'agowa bare ya fuskance ta,Hajiya da duk wanda yake cikin parlor'n gaba d'aya sai kallonsa suke babu wanda ya iya magana har bayan wani lokaci sannan Hajiya tana jinjina kai tace
"Rafeek.! Idonka kenan ko.? Anya kana son gamawa da duniyar nan lafiya,kana buk'atar albarka kuwa.!?"
Ya sake sunkuyar da kai kamar zai tsaga k'asa ya shige cikin dauriya muryarsa na wani irin karkarwa yace
"Ki garfaceni Hajiya ta,wollahi ba'a son raina na aikata haka ba,,kiyi hak'uri ki yafe.."

Bai k'arasa ba ta dakatar da shi cikin fad'a² "Rafeek baka da bakin da zaka nemi yafiyata,tun da wuri kuma muna shaidar juna maza ka tashi ka fice min a gida kafin na sab'a maka."
Saurin rik'o k'afafunta yayi,Hajiya ta lumshe idanu ta bud'e tana d'an janye k'afafunta,ya sake rik'owa sosai muryarsa na ci gaba da rawa yace
"Dan Allah Hajiya ta ki gafarce ni,wollahi na tuba."

"Baka ga komai ba Rafeek,me zai kaika saurin neman yafiya.? Mu laifin me ma kayi mana da zaka nemi gafarar mu,mu da muka yi laifi mu yafi kamata mu nemi yafiyarka saboda mun yanke hukunci ba tare da tunanin abunda gaba zata haifar ba,da ace tun farko mun tsaya munyi tunani da haka duk bata faru ba,amma tunda kai muka yiwa ba dai² ba kayi hak'uri ka gafarce mu,in sha Allah hakan ba zai sake faruwa ba."
Tana kaiwa nan ta sauko daga saman kujera tayi tsugune akan k'afafunta tana kallonsa tace "Muna fata zaka yafe mana laifukan da muka yi maka,muna sane da wanda ma bama sane."
Wani irin kunya ce ta dabaibayeshi ya kasa kwakwkwaran motsi a gurin bare yayi magana,Hajiya cikin fusata ta banka masa harara tace
"Da kai nake isashshe uban mutane,,idan ma banda rashin kunya irin taka Rafeek har kana da idon da zaka kallemu.? Bayan tarin kunyar daka samu ji yanzun ka d'auko jiki mu yafe maka.. Idan munce mun yafe sai kuma ayi yaya.?"
Shiru yayi bai yi magana ba,Hajiya taci gaba da fad'a son ranta ta inda ta shiga ba tanan take fita ba,Hauwa tunda ya shigo take jin gabanta na fad'uwa ta kalle su duka a hankali ta sunkuya ta d'auke y'an kayanta ta bar parlor'n,Hajiya ta bita da kallon tausayi bayan ta dawo da kanta kan Rafeek da yayi wani irin kicin² tace
"Sai ka wuce ai kaga yaron,ka kuma tabbatar ka bata hakur'in abubuwan da suka faru a bayan,yanzun kam kayi kad'an kace yaron nan ba jikinka bane.."
A karon farko ya d'ago yana kallon Hajiya data had'e girar sama dana k'asa yace
"Hajiya ni kuma me zai had'a ni da yaro.!?"

Yatsunta ta ware tana zaginsa tace "Zaka tashi kaje ko sai na sab'ar maka,kuji min futsararren yaro,to dan ubanka idan baka sani ba abunda kowa yake hangowa a fuskar yaron nake son ka gani da idanunka,,kuma bari ma kaji na sake fad'a maka kamar yadda kowa ya gani ya tabbatar yaron nan jininka ne yake gudu a jikinsa,kaf fad'in duniyar nan banga wanda za'a kira da ubansa bayan kai ba,tashi ka wuce ka bani guri,idan kak'i kuma salin alin maza wuce ka bar min gida.."
Ta karasa maganar tana nuna masa hanya,girgiza kai yayi cikin bayyanannen b'acin rai zai yi magana ta sake tarar numfashinsa
"Ka wuce nace ka gansu,ni ban b'ukaci jin komai daga bakinka ba.!"
Bisa dole ya tashi yabi bayan Hauwa cikin bin umarnin mahaifiyarsa,shi kam ba don plans d'insa na son raba Hauwa da gidan daya k'ullo da baya so yayi ruining d'insa da baiga abunda zaisa yaje ba,wannan shi ne dalilin da yayi masa jagoranci zuwa d'akin Hajiya inda yake tsammanin nan ta shiga,a saman bed d'in mahaifiyar tasa ya hango ta zaune ta zubawa guri d'aya ido ko k'iftawa bata yi,kana gefenta a kwance kana bacci cikin kwanciyar hankali,da ganinta kasan tana cikin tsananin damuwa but bata san wane ne ya kamata ta fito ta fad'awa ba,har ya k'araci kallonta bata sani ba,sai daya shigo cikin room d'in kafin ta farga ta san wane ne a kusa da ita,saurin mik'ewa tayi tsaye tana ja da baya like taga abun cutarwa kusa da ita,kad'an ya kalleta ya d'auke kansa a kanta,yaci gaba da takawa har ya k'arasa inda take tsaye kamar wacce ke jiran ace kyat ta zura a guje,ta ci gaba da matsawa tana saita entrance da zai kaita waje,still ya sake tab'e baki ba tare daya sake kallonta ba ya fara magana
"Me yasa kike da tsananin taurin kai ne.!? Bayan duk maganganun da muka yi dake a bayan,nayi tsammanin zuwa yanzun da kika tabbatarwa kanki nan d'in ba gidan mahaifinki bane zanzo na iske kin koma naku gidan... But sai naga ashe baki yi zuciya ba kina nan still.!"
A karon farko ta d'ago ta kalleshi bata ce masa komai ba ta d'auke kanta daga gare shi,harararta yayi yana tab'e baki
"Hakan yayi miki kyau,but kamar yadda kika ga na dawo a yanzun ina so ki sawa ranki lokacin barinki gidan nan ne yayi,cos ni banga amfanin zaman ki a k'ark'ashin inuwar mahaifana ba,ko muna da wata alak'a ne kuma bayan waccan ta baya.!?"
Sake d'aga kai tayi ta kalleshi suka had'a ido yana jifanta da mugun kallo,juyawa tayi tana kallon baby'nta da yake motsawa alamun yana son tashi,dakatawa shima Rafeek yayi da zancen da yake har sai da yaga yaron bai tashi ba sannan ya juya zai fice daga d'akin muryar Hauwa ta dakatar da shi
"Duk abunda kace naji but har yanzun maganar kawai kake yi babu evidence,,idan dan kana ganin bazan iya barin muku gida bane kake tunani ina so ka cire wannan a ranka,in sha Allah zan tafi cos ba'a binne kurwata a nan ba bare kace na zaune muku a gida.."
Wani irin juyowa yayi yana murmushi da gefen bakinsa ya tako ya dawo gabanta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login