Showing 36001 words to 39000 words out of 220972 words

Chapter 13 - DAN MACE COMPLETE Hausa Novel

23 Aug 2025

1190

na d'auki takardata na fita daga gida,na samu mai napep na fad'a masa inda zai kaini,yace na shiga ya san gurin,na shiga muka d'auki hanya,mintuna kusan talatin suka d'auke mu saboda baya wani sauri sosai muka k'araso,ya tsaya a dai² block d'in dana fad'a masa,ina ta tunanin halin da zan tarar da ita yace min "Hajiya mun k'araso."
Na kalli gurin da muke nace "Ka tabbata nan ne kuwa.!?"
   Yace "Hajiya ai number za ki duba,ke kika fad'a min fa,ga gidan nan ki sake dubawa mana"
    Na kalli house number sosai na duba ta jikin takarda,na ga iri d'aya ce babu bambanci,na sake kallon tsarin gidan na tabbatar nan ne inda ta rubuta,na sauka na biya mai napep kud'insa sannan na juya na kalli gidan,zuciyata har lokacin cike taf da tunanin anya nan d'in ne.!? Ina wannan tunanin na tunkari get d'in gidan,na yi shahada nayi knocking ina tunanin ganin ta inda Hauwa zata b'illo amma sai naji shiru,har kusan mintuna goma ban ji motsin kowa ba bare na ga mutum,nayi tunanin sake kwankwasawa amma wannan karon sai na tab'a entrance d'in,abun mamaki ashe k'ofar a bud'e take duk tsaiwar da nake yi,da mamaki sosai akan fuskata na kalli unguwar da nake jinta shiru sannan na wuce ciki na fara tafiya ina yi ina kallon ikon Allah da mamakin yadda aka yi Rafeek yayi mata kyautar gida kamar wannan,har na k'araso varenda da zata sada ni da parlor,na tsaya ina jin fargaba,a zuciyata ina addu'ar Allah yasa lafiya,na daure nayi knocking door d'in kusan mintuna uku shiru babu wani amsan da na samu,na sake yin knocking abun mamakin babu alamun mutum yana rayuwa a cikin gidan,gabana ya fad'i dana tuno kalamanta na ji hawaye suna k'ok'arin wanke min fuska,na nemi guri na zauna na ci gaba da addu'ar Allah yasa ba mutuwa Hauwa tayi ta barni ba,after 2 hours na goge hawaye idanuna duk sun kumbura,na mik'e da niyyar tafiya jikina duk yayi sanyi,na sakko daga saman varenda na kama hanyar get zan bar gidan,ina tafiya ina waiwaye,na yi nisa cikin hukuncin ubangiji na jiyo kamar sautin tari,da sauri na tsaya ina kalle² da tunanin ta ina sautin yake fitowa,amma kuma sai na rasa ina ne,na dawo da sauri na fara bin windows d'in da suke zagaye da gidan,duk window da na nufa sai na tarar da ita a rufe,idan na lek'a bana iya ganin komai saboda curtains dake zagaye da su duka masu duhu ne,nayi ta zagayawa kasancewar ginin gidan detached house ne da baiyi joining ko wane wall ba,irin ginin nan dai kawai da ake yinsa a tsakiya,na kusa gama zagaye gidan ina neman hanyar da zan shiga,dai² lokacin dana gama fitar da tsammani da samun mafita ubangiji ya taimake ni ya ji k'aina.
   Window ne guda d'aya daga can edge na k'arshe na gidan a bud'e,har ina had'awa da gudu na k'arasa jikinsa na tsaya ina addu'ar Allah yasa abunda zuciyata take sanar da ni ya kasance gaskiya,sai dana gama addu'o'i na sannan nayi k'arfin hali na kai hannuna jikin windowpanes d'in ina k'ok'arin bud'ewa,kasancewar da yawa windows dana bari a baya na yi gwada bud'ewa ban samu dama ba,sai wannan da alamu suka nuna a bud'e take,ina janyowa ta bud'e na runtse idanuna cikin fargaba,curtains d'in da suka rufe ba'a ganin komai nasa hannu ina k'ok'arin bud'ewa duka,a nan idanuna suka yi bak'in gani.....
   
   
   
    
#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*      

                   *'DAN MACE..*
              (Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥

  
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*    
https://my.w.tt/29u2S26SG2

   *Wah! 😍 U people are killing me with ur warmth comments,thank u so very much,thank u all my friends..Bahot² shukhurya..*♥

Pᴀɢᴇ 12.
#Iɴꜱᴀɴɪᴛʏ
   
    Akan Hauwa idanuna suka fara sauka,kwance take amma cikin wani irin yanayi mai ban tsoro da firgitarwa,na koma baya da sauri cikin tsananin tashin hankali har ban san lokacin da na fasa k'ara ba,ta juyo ta kalli inda taji ihun bata ga kowa ba,ta juyar da kanta babu damuwar komai a ranta,nayi kuka sosai har sai da naji na sire bana iya sake yin hawaye,guiwoyina sun yi sanyi bayan na bawa zuciyata hak'uri na sake matsawa jikin window ina ta kallonta a hankali cikin muryar mai kashe jiki na kira sunan ta "Hauwa'u.!"
     Ta juyo da sauri ta kallo inda nake,a hankali ta k'uramin ido kamar mai son tuna wace ce ni,na daure duk da hawayen da suke bin fuskata nace "Me ya same ki kika dawo haka.!?"

    Ta yi shiru ta ci gaba da kallo na ba tare da ta ce komai ba,ina kuka nace "zo maza ki bud'e min k'ofa,ni ce y'ar uwar ki,ban san haka rayuwarki zata dawo ba,ki gafarce ni y'ar uwata,da na san haka al'amarin nan zai kasance tabbas ba zan tab'a bari kiyi nisa da ni ba,sai dai duk abunda zai faru ya faru,ki yimin afuwa k'anwata,ba a son raina haka ta faru ba.."
       Still bata motsa daga inda take ba,ta yi shiru dai ta zuba min idanunta,duk abunda nake fad'a tana saurare na,sai dai alamu sun gwada gaba d'aya bata fahimtar abunda nake cewa,nayi magana nayi begging d'inta amma kusan duka a banza babu wanda ta ji,bare ta aikata.
   Yinin ranar ya kasance a nan na yi shi ina yawo tsakanin harabar gidan da window d'in d'akin da take,har dare ya fara gabatowa ban samu damar shiga cikin gidan ba,wajen misalin k'arfe goma saura mintuna na sake komawa inda take,har lokacin tana nan kamar yadda na barta,na tsaya ina kallonta da tausayawa nace "Hauwa.!"
    Jin magana yasa tayi sauri ta waiwayo tana kallona,na daure nace "Zanje gida na tattaro kayana,in sha Allah ina nan dawowa ba da jimawa ba kin ji.!?"
     Kamar ta fahimci abunda nake nufi ta juyar da kanta ta k'urawa guri d'aya ido,cikin yanayin sanyin jiki na janyo k'afafuna na fito,ta waje na samu cable na d'aure get d'in sannan na kama hanya ina tafe ina gabana sai fad'uwa yake,a haka na fara neman abun hawa,da kyar lokacin 11pm saura mintuna 15 na samu napep,na fad'a masa inda zai kai ni,yace na hau mu tafi,na shiga muka fara tafiya,Allah ya taimake ni na samu irin masu napep d'in zamani,gudun da muka yi a lokacin ni na san ba kadan bane,11:00pm muka tsaya a k'ofar gidanmu,na sauka na sallami mai napep,na wuce cikin gida gabana yana ci gaba da fad'uwa,saboda ban san me zan tarar ba.

***
     Abunda ya faru gidan mu kuwa a yinin ranar,bayan fita ta daga gida,ban san wane ne ya fad'awa Baba na fita ba,ya saba baya dawowa da wuri amma ranar after Maghreb Baba ya dawo ya fara jkran yaga ta inda zan b'illo,har 11:00pm saura mintuna bai ganni ba bai kuma samu labarin inda na mak'ale ba,dai² lokacin da agogo ya nuna 11pm Baba ya kira babban yayanmu Abdullahi yace yaje ya rufe masa k'ofar gidansa,yayanmu ya taho da niyyar rufe k'ofa kamar yadda Baba yayi masa umarni muka gamu a zaure,ya kalleni ya wuce ba tare da yace min komai ba,na wuce cikin mutuwar jiki saboda irin kallon da naga yayanmu yayi min na k'araso tsakar gida,nayi sallama babu wanda ya amsa,na kallesu d'aya bayan d'aya naga ni suke kallo,nayi ajiyar zuciya ina k'ok'arin wucewa suka fara gulma a tsakaninsu suna tambayar juna "Ko daga ina take da wannan talatainin daren.." rashin samun amsa yasa kowacce taja bakinta ta tsuke.

    Kai tsaye hanyar d'akin kwananmu na nufa,ina tafiya ina sake tunanin halin da na bar y'ar uwata,na kusa da k'ofar d'aki na jiyo muryar Baba yana daka min tsawa
       "Kece.! Maryam ina za ki shiga.!?" Na juya a tsorace na kalleshi jikina sai b'ari yake nace "Baba d'aki zan shiga."
Ya kalle ni sosai yace "Wane d'akin.!?" Nayi shiru na sunkuyar da kaina a k'asa,ya girgiza kai "Ko da wasa kada ki kuskura ki shiga ciki,idan baki jiba kina iya gwadawa,zan nuna miki ni ne na haifeki.."
   Nayi shiru ban d'ago ba,zuciyata ta cika da tsoron shi kenan mai afkuwa ta faru,ina nan tsaye Baba ya kalli babban yayanmu "Abdullahi.!" Ya amsa,yace "Maza shiga d'akin can duk abunda kasan na ta ne ka watso min su nan" yayi masa nuni da tsakar gida,ya sake amsawa ya wuce,ina tsaye ina kallon y'an gidanmu gaba d'aya duk wad'anda suke gida suna nan idan aka cire mata na sama da ni da suke gidan aurensu,mutum goma sha uku suna tsaye suna kallon abunda yake faruwa,haka matar Baban namu itama tana tsaye,har Yayanmu ya gama watsar min da kayana ban iya nayi kwakwaran motsi ba,na sunkuya na tattara kayana ina jin zuciyata kamar za ta fashe da tsananin bak'in ciki,ina gamawa Baba ya fito daga d'akinsa ya kallesu duka ya girgiza kai,muryarsa cike da tsoratarwa "Wannan ita ce makomar duk wanda ya ji ba zai iya yi min biyayya ba,a matsayina na mahaifinku ni kad'ai ne gatan ku,shin ina iyayenki suke.!? Duk da suka watsar da ku akwai wanda uwarsa ta tab'a zuwa da sunan ta zo duba shi.!? Ni nake wahala da ku,bai zama dole ku bini ba.!?"
   Babu wanda ya iya amsawa,yace "Idan kunji ba zaku iya ba,kuna da zab'in ku tafi kuyi rayuwarku yadda kuka so,,sai dai ku sani daga ranar da muka rabu mun rabu kenan,har abada zan kasance a matsayin ba mahaifinku ba.. Sauran shawara ta rage ga mai hankali."
   Jikin kowa yayi sanyi,Baba ya juyo gare ni ya kalle ni "Maryam! Tun da har kin kasance bakya jin magana,ga hanya nan na baki kina da damar kiyi duk abunda kika ga yayi miki kyau,kamar yadda na jima ina tunatar da ke,duk ranar da Allah yasa na ji labarin kin je gurin y'ar uwarki za mu rabu,amma sai baki ji magana ta ba,,shi kenan tunda kin zab'e ta,ki je Allah ya bamu alkhairi.. Dan na cire ku a cikin zuri'ata ba wani abu ne da zai d'aga min hankali ba,Allah ya so ina da wasu y'ay'an.. Ba zan yi bak'in ciki ba,kuma dai Allah ya gani na tsaya akan tarbiyyar ku har na aurar da ku,tsakanin ni da ku idan akwai wanda ya zalunci wani ubangiji ya saka masa.."
    Yana fad'a ya wuce d'akinsa yana barwa Yayanmu sak'on "idan ta fita ka rufe min k'ofar gidana.." Duk y'an gidanmu sun yi cirko² kamar zakarun k'auye kowa si bina yake da kallo,nayi godiya ga Allah da irin k'addarar daya zab'a mana,sannan na d'auki jakar kayana nayi sallama da y'an gidanmu,dan na san ba lallai ne ko a hanya mu sake gamuwa ba..

     Ba tare da na samu tausaya daga mahaifina ba,duk da kasancewarsa shi ne wanda yayi silar zuwa na duniya,y'an gidanmu ma kuma tun da Baba yace na bar masa gidansa babu wanda yayi ko da tari bare su iya bashi hak'uri ya barni na kwana zuwa da safe,,a cikin wannan daren na sake barin unguwar duk da kasancewata y'a mace na kama hanyar Sardauna crescent,na sauka a k'ofar gidan around 12am har da mintuna na bawa mai napep kud'insa na bud'e get na shiga na kulle,na k'araso bakin entrance nayi knocking,still tak'i zuwa ta bud'e,,na yi magana nayi bagging d'inta amma bata yi niyyar zuwa ta bud'e ba,na yi shimfid'a na zauna ina tunanin rayuwa a haka muka ga wayewar gari,da safe ma still na koma nayi magana amma bata kula ba bare ta bud'e,na tafi orphanage da ta fad'a min zata kaika da niyyar na karb'o ka,zuciyata da tunanin hakan zai sa idan Allah ya taimake ni ta ganka ta yarda abunda na fad'a mata gaskiya ne,,na sha wahala sosai a wannan yinin ranar kafin hukumar gidan marayun su yarda su bani kai,muka dawo gida na koma ta can baya wajen window da nufin yi mata magana ina rik'e da kai kana bacci,har lokacin tana zaune inda na barta,nayi ta rok'onta har dare shiru,na hak'ura nace "shi kenan za mu jira duk tsayin lokaci,muna nan tare dake ba zamu barki ba,kinga yaronki ma na karb'o miki shi.."
   Daga haka ban sake magana ba na koma inda nayi shimfid'a na zauna ina ci gaba da tunani,ban san me ya faruba dana barta a d'aki ba,bayan wani lokaci tazo ta bud'e k'ofar tana lek'owa,na d'aga kaina muka kalli juna da ita,jikina a sanyaye nayi murmushi nace "kin gani ko,bamu tafi ba muna nan muna ta jira mu zo gurinki."
   Bata yi murmushi ba sai gesturing fuskarta da take yawan yi kamar wacce ke jin wani abu na mata yawo a jiki,kusan mintuna uku muna kallon-kallo ta koma ta bar k'ofar a bud'e,na tattara y'an kayana na bita a baya ina rik'e da kai a hannu d'aya d'ayan muka kayanmu,,,zuwa na gidan na iske abubuwa da dama,wasu masu dad'i wasu kishiyarsa sai dai mafi yawa daga ciki sune marasa dad'in,rashin lafiyar Hauwa ba k'aramin gigita min tunani yaso yi ba,a wannan hali rashin fahimta daya shafi tunaninta,muka yi ta yawon zuwa hospital,daga karshe muka samu wani likita ya bani shawaran mu gwada zuwa psychiatry,saboda duk binciken da likitoci suka yi sun tabbatar kwakwalwarta ce ta fara tab'uwa,tun daga ranar da likitan nan ya fad'a min hakan bamu sake komawa ko wane irin hospital ba sai psychiatry,munyi yawo akan neman lafiyarta har ban san adadi ba,a nan Kano munje² har ban san adadin yawon mu ba,muka shafe tsayin shekaru biyar muna yawo tsakanin *DAWANAU* da gida,sai dai kullum muna nan tsaye guri guda tana dai under medication ne,naga lamari babu ci gaba na tattaro ta muka dawo gida,sati uku da fitowarta daga dawanau muka nufi birnin ikko (lagos),can d'inma dai yawon muka yi ta fama da shi,ita sun rik'eta a asylum mu kuma muka kama haya,a can ne saboda kasancewar baka gama primary ba na samu damar mayar da kai shool,har ka gama makarantar primary ka tafi secondary muna zaune a can,bamu da kowa a garin ni nake kaika makaranta ni nake d'auko ka,idan na dawo na ji da aikin gida da zuwa duba ta,har zuwa lokacin da kayi wayo kana iya zuwa da kanka ka dawo,,a takaice dai muka sake shafe tsayin shekaru sha biyu a Lagos gurin neman magani ba tare da samun nasara ba,,nasarar da zan iya cewa mun samu a wannan fannin duk abunda yake faruwa da ita bata duka,but idan abun ya haura mata za kaga tana yi kamar zata fita aguje tana surutai,bayan wannan babu wani abu makamancinsa sai dai ko shirun data koma yi daga baya,idan ka yi o magana baza ta amsa ba,haka ma surutai ta daina yi,,daga lagos al'amari yak'i a lokacin ka kammala secondary school muka sake dawowa Kano,dawowarmu babu jimawa idan baka manta ba shi ne farkon lokacin dana nema maka admission a U.K a jami'ar Oxford,after then na sake neman kasuwancin da zai rik'e mu na fara saboda dukiya idan ba'a juya ta tabbas wata rana dole ta k'are,bare mu da muka d'auki shekaru muna yawo,,mun shekara uku ina yawon kasuwanci komai dana san ana amfanin yau da kullum ina siyarwa,Alhamdulillah ubangiji shi ne komai,ya sawa mutane son kayan da muke kasuwancin su,Allah cikin ikonsa ya sake dafa mana kasuwanci ya karb'u,a da mu muke siyarwa cikin k'ank'anin lokaci ya juya al'amarin ya zama mun koma wholesaling sai dai mu shigo da kaya mu raba su ga retail's,Alhamdullah ba zan gaji da fad'a ba a tsakanin shekaru bakwai da dawowarmu kasuwancin mu ya tsaya da k'afafunsa mun samu wadata fiye da baya,Alhamdulillah alaa kulli halin,ba mu da wani damuwa daya wuce lafiyar mahaifiyarka,kullum rayuwarmu cikin haske take but a kullum na kasance mai addu'ar hasken da zai tunkaromu nan gaba ya kasance mafi girma daga cikin hasken da muka samu a baya... Wannan shi ne tak'aicce cikin labarin rayuwar mu..!"

*BACK TO STORY...*

     Dogon ajiyar numfashi suka yi a tare Nuraz ya kalli Annie a hankali idanunsa sunyi ja hawaye suna zuba yasa handkey yayi whipping d'insu yace "Annie me yasa bayan rasuwar mijinki baki yi wani auren ba!?"
   Murmushi tayi wanda iya kacinsa saman lips tace "Habibiiy.! Shin ta yaya ne ni da nake da patient zanyi wani aure,sannan kai kuma na kai ka ina.!? Kada ka manta ba ko wane namiji ne yake son rik'on d'an da ba nasa ba.. Besides ma ko da ace zanyi aure a wannan lokacin ko wane ne yazo da niyyar aurena ba zai tab'a yarda da aure ni ba."

    Yace "Me yasa to Annie.!?" Tace "Ka manta a baya na fad'a maka korata babanmu yayi kamar yadda ya yiwa Hauwa.!? Saboda haka ka ga babu namijin da zai yarda ya auri wacce take *KORARRIYA*,bcos zai ta zargin me tayi haka mai muni iyayenta suka rabu da ita.!? Ka ga kenan rayuwar aurenta kawai dai zai kasance ne ta yi auren amma baza su tab'a samun nutsuwar zuciya ba,,sannan a duk ranar da aka samu sab'ani zai iya goranta mata,hakan kuma zai iya kaisu ga rabuwa.."
      Gyad'a kai yayi yace "Na fahimci uzurinki Annie.."
     D'an murmushin yak'e tayi ta goge fuskarta,a hankali tana kallonsa cikin salon son ta canja hiran ganin ya yi shiru yana tunani tace "Yaushe zaka koma ne.!?"

    Ya d'ago kansa da sauri dake k'asa yana tunanin irin hukuncin da zai yiwa mutane biyu da suka canja tarihin mahaifiyarsa yace "Ina kenan Annie.!?"

     Tace "School nake tambayar ka.!"

   Ajiyar zuciya yayi yace "Maybe sai wani satin."
     Tayi saurin kallonsa tana had'e rai tace "Kai bana son shashanci,da karatun yazo k'arshe saura baifi one month ba shi ne zaka fara delaying wajen komawa,,thought cewa kayi k'arshen satin nan zaka tafi.!?"

      Ya gyad'a kai yana marairaicewa "please Annie ki bari na zauna sai wani satin.?"

    Kafin ya kai aya tace "Bafa zan bari ka zauna ba,,gara ka wuce,da can me yasa baka tab'a zaman ba tsayin shekaru bakwai sai yau ne zaka fara min shirme.!?"
      B'ata fuskarsa yayi yayi kicin² a tunaninsa zata ce ya zauna sai yaga ta tab'e baki ta mik'e tsaye,d'auke kansa yayi gefe,Annie ta kalleshi tace "Za kayi kuma zaka gama,,in dai nice ka san maganata d'aya nake bana biyu..

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login