Showing 126001 words to 129000 words out of 130249 words

Chapter 43 - ME KAMAR SARKI

  

04 Oct 2024

17589

dan wallahi banga shegen🙊 daya isa hana ni auren wannan yarinyar ba ko d'an uban waye shi a garin nan kin gane😣😳 ai garama kafin kowa yaji kibi ta ruwan sanyi ki bani ita idan kuwa ba haka ba zaki bani aurenta da qarfin hatsi dan wallahi Allah ko zaki mutu saina aureta".

SUBAHANALLAHI ASABE TAKI TA SAMEKI KIN GAMU DA GAMONKI🤔🤨.

Yana rufe baki Asabe ta kaiwa Bahijjah dake tsaye kusa dashi wata irin sha'ka tana cewa "zaki wuce ki shiga gida ko saina kasheki a gurin nan"?.

Da sauri Bahijjah taja baya tana cewa "na shiga wanne gidan ni wallahi shi zanbi nabar zaman gidan nan daga rana irin ta yau idan make bazaki aura min Shiba zamuje gurin liman yakai sadaki a daura mana aurenmu".

Dafe 'kirji Asabe tai cike da rud'ewa idonta kamar zai fito waje batasan lokacin da hawaye masu zafi suka fara yi mata zarya a kuncinta ba nuna Bahijjah take da yatsa amma ta kasa magana a fusace ta fisgeta tana hakad'ata cikin gida tasa murfin kofa ta rufe tare da juyowa tana kallon Iluh wanda ya tsaya 'kerere yana kallon ta tace.

"Allah ya tsinewa uwa da uban da suka haifeka shege tsinanne talakan banza wallahi karya kake Bahijjah tafi qarfin auren d'an garuwa irinka tun wuri kaje ka nemi daidai dakai" tana fad'in haka ta bud'e kofa ta fad'a gida kai Iluh ya jinjina yana cewa "lallai matar nan baki sanni ba amma babu damuwa zan nuna miki iyakarki indai ni d'an halak ne na cika sunana Ibrahim wallahi tallahi wallahi tallahi saina auri yarinyar nan kuma zaki gani" yana fad'in haka shima ya juya yabar gurin haka Asabe taiwa Bahijjah tsinannan duka a cikin gida bayan shigarsu harda fasa mata baki tayi mata jina jina saboda irin ciwon da takejin zuciyarta nayi.

🌴 CAMEROON 🌴
Sakamakon ganin irin ri'kon amanar da su malam Habu suke dashi yasa Alhaji Idrisu ya saki jiki dasu yake musu duk abinda suke so ya d'auke nauyinmu komai shi yake musu suma haka suka zage karfin su suna kyautata masa da d'an abubuwan da baza'a rasa ba kuma hakan saiya zame musu gamda katar domin sun ninka da samun kud'i albashi kusan ninki biyu yake biyansu akan nada ga ihsani da sutura akai akai tuni sukai 'kiba dakyau suka mayar da jikinsu babu rama saidai malam Habu kullum yadda yaga rana haka zaiga dare baya samun barci tunanin iyalansa yake ya a wanne hall suke ya taho bai bar musu sisi ba.

Suna zaune a wajen gate d'in kofar Alhajin Sadi na masa hira amma ba sosai yake amsawa ba saidai yace masa umm umm saboda tunani dayai masa yawa kallonsa Sadi yai yana cewa "lafiya kuwa nifa naga kamar kana cikin damuw ko baka da lafiya ne"?

Kai malam Habu ya girgiza "a'a ina lafiya Sadi hankali nane ya juya izuwa gida idan ba zuwa nai na ganosu ba bazan mayar da hankalina akan aiki ba".

"To babbar magana yanzu ya kake so ayi"?.

"Alhaji nake jira ya dawo nayi masa magana idan ya amince saimu tattara muje gida ko sati biyu muyi mu dawo idan ma kai kana ganin baza kaje ba saika bani sakon da zankaiwa matarka ko"?.

Kai Sadi ya girgiza yana cewa "a'a nima zanje basai mu dawo tare ba ai inaga tunda Alhaji yana gari ma dayya dawo mu sanar masa gobe kawai sai tafiya ko ya kace"?.

Kai Malam Habu ya d'aga "eh haka ne gaskiya na damu naje gida dan haka insha Allahu gobe iyanzu mun sauka bari ya dawo daga ofishinsu zan sameshi naji me zaice Allah yasa kar yace mu d'an kara zama wallahi haka kawai naji lokaci guda garin nan ya isheni gida nake so".

"Humm malam Habu kenan dama ai haka ne suma kuma na gidan suna can suna kewarka saboda wasa-wasa fa mun dad'e anan amma zamuje mu yiwa hajiya mammah mai abinci sallama ko"?.

"Eh zamuje bari ya dawo tukuna mu fara sanar masa kar muyi gaggawa duk da nasan bazai hana ba domin munyi muguwar dad'ewa a garin nan shekara da kusan watanni hud'u kamar wanda aka rufe mana bakin mu koma gida".

Da dare bayan Alhaji ya dawo suka sameshi da bukatarsu ta zuwa gida akan nan da sati kamar biyu zuwa uku idan sukaga ahlinsu zasu dawo ya amince harma ya musu alheri irin wanda basa zato dasu da matansu yadika da atamfofi ga kud'i kamar dama ajiya suke bashi sunyi murna qwarai da gaske sukai masa godiya da addu'a mai kyau washe gari tun asubar fari sukai shiri ana fitowa daga masallaci d'auko hanyar gida.

Amma me tafiya batai kyau ba domin a hanya sun had'u da 'yan fashi🙊 haka suka taresu a daji sukaiwa wasu duka bayan sun yashe musu komai na motar karshen wulakanci hatta kayan jikinsu basu bar musu ba saida sukai musu tikk sannan suka korasu cikin mota suka gudu wadanda basusan qaddara ba harda kuka haka malam Habu ya tsinci kanshi cikin wani irin yanayi na takaici bayan lokaci mai tsawo daya d'auka baya gida yau ya dawo da qwarin gwiwa zai kawowa iyalansa abunda da dad'e yana mafarkin samu yaga ya wadatasu amma tsinannun sunyi musu bankad'a sai bayan sallar isha sosai suka sauka a 'kauyen kusa dasu daga nan ko kud'in mashi basu dashi sai a qasa suka d'auko hanyar gida sanda suka iso sai mutane d'ai d'ai dare ya fara kowa ya shiga gida da'kyar Malam Habu yacewa Sadi saida safe wanda Sadin shima da'kyar yace masa Allah ya tashemu lafiya jiki babu armashi a sa'bule kowa ya nufi gida da yake Malam Habu yafi kusa Sadi yana anguwar gabas a gurin suka rabu shiya wuce gida shi kuma ya qara gaba.

Malam Habu da'kyar yake d'aga kafarsa da babu takalmi yake takawa zuwa cikin gidansa jiki a mugun sanyaye cike da tunanin me zaice musu da wacce fuska zai kallesu tsawon wannan lokacin me suke ci daya suke rayuwa waye yake kula dasu sauke ajiyar zuciya yai yana shiga gidan da sakaliyar sallama😥 a bakinsa duk suna zaune a tsakar gida cikin hasken farin wata tarr daya haske ko'ina.

Cike da mamaki suka zuba masa ido suna kallonsa domin a yadda yai sallama da muryar daba tashi ba basu saba jinsa da ita ba duk tunanin su ko wannan mahaucin ne 'kwalisa tunda yake shigowa qauyen kuma basu rufe gida ba a razane kowa ya tashi Aisha da tafi kowa tsoro da gudu tai hanyar d'akinsu tana cewa.

"Wallahi 'kwalisa ne ku tashi yanzu ya fara duka jiya ma ya mari Habiba a dandali".

Jin haka yasa kowa ya mi'ke a firgice zasu gudu muryar malam Habu da tsantsan damuwa yace "ku dawo kufa nine ba wani bs yanzu na dawo".

Duk tsayawa sukai sak A'i dake ri'ke da fitila ta haskesa ganin da gaske Malam Habun ne yasa tace "innalillahi wa inna ilaihi raji'un mun shiga uku malam me zan gani haka"? Ta karasa maganar tana sake haska fitilar da sauri suka matso gurin sa Aisha ma dake d'aki jin abinda A'in tace yasa da gudu ta fito kaii da gaske shine duk salati suka saki Asma'u kam da yake tafi kowa saurin kuka haka ta fashe dashi tana dur'kusawa a gun domin kowa yaga a yadda malam Habu yake yasan tafiya batai kyau ba.

"Malam meya faru dakai haka daga ina lokaci mai tsawo shiru muna sa rai zaka dawo mana gida fal da Abubuwan arziki sai muga haka" A'i ta fad'a tana sake kare masa kallo.

Saude dai ta kasa magana Binta ce ta danyi qoqarin cewa "sannu da dawowa Malam bari na kawo maka tabarma" ta karasa maganar tana juyawa zuwa d'aki tare da share 'kwalar data zubo mata ta dauko tana shimfid'a masa kasa zama yai yana tsaye kamar an dasa shi.

"Malam dan Allah ka zauna nasan a gajiye kake"?.

Kai Malam Habu ya girgiza yana cewa "ban dace da Wanda zakuyiwa shimfid'a ba ban kasance mutum wanda zai zauna akan shimfid'a ba mena kawo muku dame na tafi na barku a wanne hali kuka tsinci kanku bayan tafiya ta daya kuke ciyar da kanku daya kuke tufatar da kanku tsawon wannan lokacin hakika yau ina matukar jin kunyar hada ido daku saboda abinda na aikata muku dan Allah ku yafe min😒🤲🙏.

Kai kowa yake girgizawa murya a sanyaye Binta tace "malam bakai mana komai ba dan Allah ka zauna".

Shima kan ya girgiza yana cewa "Binta bazan ta'ba zama ba wallahi har sai kunce kun yafeni sannan ne zuciyata zata d'an samu nutsuwa kad'an na samu qwarin gwiwar iya zama daku a yanzu saboda na gaza na kasa".

"Ayya malam baka kasa ba mun fahimce ka kuma nidai na yafeka duniya da lahira".

Kai Saude ta d'aga "Nima malam na yafeka babu abinda kai mana"..

Nanfa kowa ya dauka sun yafeshi jikin A'i ma dai yayi sanyi qalau sai ido kawai take binsa dashi sai lokacin Malam Habu ya iya zama ruwa Binta ta kawo masa sannan ta nufi murhu tana d'ora masa tukunyar ruwan zafi dan a yanzun kam sun fahimta cewa da 'yan fashi suka had'u tunda ga alama nan ya nuna jikinsa da akwai tabambuna Saude ma da sauri ta tashi tana dauko masa tuwo ta sako miya ta kawo masa kai ya girgiza mata domin a yadda yake jin jikinsa ko ruwa had'iya d'aya bazai iya shaba kawai ruwan zafi yake bu'kata su Jamila na gefe sunata aikin share hawaye sun san yau da ace Amatu tana nan hummm ba'a san ya zatai ba gara da bata nan kuma sun dau alkawarin insha Allahu bazasu fad'a Mata ba bazata ta'ba sanin anyi wannan abun ba.

Saida malam Habu yai wanka da ruwa mai zafi sosai ya d'umama jikinsa ya gasa shi sannan ya fito yana zama cikin nutsuwa yace su saurareshi a hankali ya basu labarin duk abinda ya faru tun daga ranar da sukaje Cameroon har yau da 'yan fashi suka taresu a daji suka kar'be musu komai yana rufe baki A'i dake faman ciwon yatsa tace.

"Kai amma Allah dai ya tsine musu albarka Allah ya tarwatsa su mitsiyata tsinanu in Allah ya yarda suma kud'in bazai amfanesu ba shine ajalinsu".

Shidai malam Habu baice komai ba haka sauran babu wanda yace qala sai jimami da takaicin irin dukiyar da Malam Habun ya Tara kuma wadannan 'yan fashin suka kar'be haka kowa jiki a sanyaye sukaita zaune a gurin ba um ba um um kowa babu barci a idanunsa sai damuwa haka Binta tayi hamdala da babu a Amatu a gidan da yau batasan wanne irin hali zata shiga ba ganin a yadda babanta ya shigo gida tun daga wata 'kasa ga tabon ciwon dukan 'yan fashi a jikinsa kila saita kwanta jinya".


🌃️MARSHALL ISLANDS🌃
Clarah tana zaune duk abun duniya ya isheta so take su had'u da Asad akwai abinda zata tambaye shi amma kwanan nan baya samun hutu kullum suna fita operation ne sauke numfashi tai tana d'aukar phone d'inta ta kira numbar sa amma line busy bari tai kamar mintuna biyar ta sake kira still number busy tsaki taja cikin takaici tana mi'kewa ta soma zaga gurin tare da tunani a zuciyarta shin meye ya rageta meye ya tauyeta me zatai wanda zaija hankalin Asad dame Yusairat ta fita har tayi nasara akansa meyasa ita ta har yanxu ta kasa koda samun nasarar lokacin sa? wannan tunanin ne fal ranta kullum bata aiki sai son gano me yake so ta ri'kayi wanda zata jawo ra'ayinsa da gaggawa.....,.............

Tunanin tane ya katse jin wayanta na 'kara ga sunan Asad da manya ba'ki da sauri ta d'auka jikinta har rawa yake cikeda shau'kin so tace.

"Hello Asad kana jina"?.

Daga can 'bangaren Asad dake zaune gaban laptop hankalinsa nakan wani abun da yake so ya kashesa da mamaki yace.

"Eh Ina aiki ne meya faru kike kirana"?.

Sake kashe murya Clarah tai tana cewa "am Asad inason zamuyi magana ne" tambaya ya jefo mata.

"Yanzu"?.

Da sauri tace "eh a Ina zan sameka"?.

"A'm at home".

Zaro ido Clarah tai jin abinda take fata ya samu tana so ya bata damar da zata shiga gidansa har 'kwaruwa take wajen cewa.

"Ok nazo na sameka"?.

"No karki zo min gida".

Sak tai jiki a sanyaye tace "meyasa ne Asad baka so na ra'be ka"?.

"Saboda ni sam ban cika son mace tana zuwa gidana inda nake ba".

"Saboda kar mutane su zargeka"?.

"A'a ina ruwana da mutane saboda kare mutunci na kin gane"?.

"Ok ok na gane to dan Allah ka fito muyi magana".

"Bazaki iya fad'a min a waya ba dole saimun had'u"?.

'Dan shiru tai sai kuma tace "a'a zan iya amma nafi so saigani gaka kamar zaka fi fahimta ta yadda ya kamata"?.

"Ok ki bari zuwa nan da dare idan na samu lokaci zamuyi magana kuma saina nemeki" yana fad'in haka taji d'itttt ya kashe wayarsa hawaye ne masu zafi suka zubo mata 'kafafunta na rawa da'kyar ta samu ta zauna tare da kifa kanta akan cinya ta soma kuka zuciyarta na rad'ad'i tabbas idan Asad bai tsaya ya saurareta ba ya juyo da hankalin sa kanta ba tofa rayuwar ta tana cikin had'ari dan matukar sukaci gaba da tafiya a haka gara ta rataye kanta ta huta da wannan 'kunci da damuwar da take fuskanta kullum.

A 'bangaren Asad kuwa bayan ya kashe waya da sauri ya tattara dukkan nutsuwa da kulawarsa akan laptop d'in gabansa ganin cewa an samu wanda ya gano 'kungiyar kuma alama ta nuna mace ce saidai babu ta yadda za'ai ka gane wacece ba suna ba photo ba location ba information empty file d'inta yake a list d'in unknown shiru yai yana kallon rubutun dazai kaishi shafinta na website kafin ya danna link d'in amma yana shiga babu komai a shafin zero d'an rufe ido yai yana sake kallon laptop d'in zuciyarsa na tambayar sa wace ita a ina take taya zan sameta awane yankin 'kasa ko gari take a duniya ta Ina zan fara shin sojace ita ko 'kanwar soja ko 'yar gidan soja shin a familyn su akwai soja tasan ana neman 'kungiyar ko a'a akwai wanda takewa aiki ko kawai a bincikenta ta gano? Mi'kewa yai batare daya rufe laptop d'in ba ya soma zaga gurin cikin nazari da yadda zai 'bullowa al'amarin kafin kamar wanda aka tsikare shi ya sake zama yana jawo laptop d'in yaci gaba da aiki ko zai dace ya samu wata 'yar alama.


🏙️DUTSE MOPAL-BASE🏙️
Amatu tana zaune ita kad'ai a bedroom da laptop a gabanta sai bincike take ta shiga nan ta fita nan wani assignment zatai mai matukar wuya da had'ari tafi awa biyu tana bincike ta shiga nan ta fita duk ta hargitse tad'au zafi ga abinda take nema bata samu ba gashi Maryam ta mata maganar ta shirya zasuje gano amaryar yayansu Ahmad kwasam taci karo da tashin hankali abun d'imuwa dasa a gigice a firgice a fita hayyacin wato dai taga wani abu da wani 'bangare da 'yan 'kananan bayanai game da wannan ba'kar mummunar azababbiyar 'kungiyar wacce gwaraza da hazi'kan sadaukan maya'kan sojoji suke son sani da mafarkin samu ta kowanne hali.

Abun ya firgita mata tunani daga farko har batasan lokacin data rufe laptop d'in ba jikinta na rawa kamar maijin sanyi lokaci guda taji wani irin 'karfin zuciya da tsikewa ya dirar mata kamar wacce aka 'kara mata kuzari haka ta mi'ke daga kwancen da take tana yaye bargon data lullu'ba ta sake bud'e laptop d'in tana kunnata taci gaba da bincike saidai sa'banin na d'azu dan yanxu zallar rubutu ne take karantashi wanda dama already an turo ne dan ita ana mai mata gargad'in ta kame bakinta idan kuma ba haka ba zata hallaka ta'be baki Amatu tai bayan ta gama karantawa tace.

"Ji wani jahilci su waye kuma wadannan mutanen a wanne gari suke 'kungiyar meye wannan d'in" mutttttsss ni harsun bani haushi ma aikin banza uban me zanyi da 'kungiyar su harda gargad'ina wani karna fad'awa kowa wanda ya damu da kasuwa shiyake bada sautu" Amatu na rufe baki Maryam ta shigo tana cewa.

"Surutun me kike ke kuma koda Nabilah ne"?.

Kai Amatu ta girgiza tana rufe laptop d'in tace "a'a kawai Ina duba abu ne".

"Ok kiyi wankan mana ko kin fasa zuwa gidan ya Ahmad d'in ne"?.

Mi'kewa Amatu tai tana cewa "oh sorry wallahi sha'afa nai amma yanzu zan shirya ku jirani" ok Dan Allah da sauri kinga yazo tare zamu tafi dashi tunda nikam bansan gidan ba garama keda Nabilah kunje sau d'aya".

Dariya Amatu tai tana cewa "humm ai kema rashin kirki ya hana ki zuwa Allah yasa idan mukaje yau ya Ahmad d'in ya hanaki tahowa saikin musu weekend naga tasan zillewa".

Ta'be baki Maryam tai tana cewa "tab wallahi bazan zauna ba haka kawai na zama yar shara da wanke wanke suna d'aki sun 'kule ni ina waje Ina shan aiki umm daina fad'a ma karkisa na fasa".

"A'a indai danna fad'i haka ne zaki fasa dama dai baki da niyyar zuwa fad'ar hakan ne zaisa ki fasa"?.

"Eh man sauri ki shirya muna falor" ok ganinan yanzu" bathroom ta wuce Maryam kuma ta fita duk suna falor harda Alhaji Bashir da yake yau ba ranar aiki bace ganinta ita kad'ai yasa Ahmad cewa "ke maye haka ina soldier🤗 d'in take"?.

'Yar dariya Maryam tai tana d'aukar handbag d'inta tace "yanxu zata fito wanka take".

"Oh sai yanxu ma ta shiga wanka dama an fad'a mata sojoji haka suke da sanya komai a zafafe sukeyi anya kuwa zata iya aikin nan kawai bari ta fito na bata shawara ta koma 'bangaren doctor ta barwa maza soldier d'in nan"?.

"Maza irin ka"? Aunty Safiyah ta tambaye shi cikin tsokana d'an zaro ido yai yana cewa "niiii a'a tabdijan mazai kaini daji mahallaka ina daga bangaren allura💉 da magunguna💊".

"Ok kasan a barka 'bangaren allura da magani saika barta itama bangaren bindiga🔫 da bullet kowa da kiwon daya kar'beshi ma'kofcin mai akuyi🐐 yasai kura🐆.

Kallonsa Alhaji Bashir yai yana cewa "to kai meye naka na tambaya tunda kasan burinta ne kuma yawe ya fad'a maka Amatullahi me sanyi ce ko kai bazaka fad'a Mata zafi ba saidai ka fad'a mata tsoro".

Dariya Ahmad yai yana kallon Amatu data fito tana sanya hijab yace "ai Daddy ba tsoro ne ya hana nayi soja ba".

"To meye idan ba tsoro ba"?.

"Allah Daddy ka yarda ra'ayi nane".

"Shikenan na yarda kodan abar

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login