Showing 48001 words to 51000 words out of 130249 words
lafiya bane ya miki wannan aika la'ilaha illallahu kaito na dama banga wannan rana ba wannan wanne irin masifa ne da bala'i" hakuri su Salamatu ke bata duk da kowa jikin sa rawa yake aka nufo gida wasu na cewa a kaita asibiti wasu na cewa bata da rai.
Kwantar da ita akai Baffah dake durkushe gabanta yana kallon fuskarta abubuwa da na masa yawo cikin kwakwalwa musamman maganar da sukai na zai kaita makaranta gobe ashe yarinyar nan burin ta nason ganin tayi karatu ta samu ilimi bazai cika ba hawaye ne masu zafi ke zuma daga idon Baffah wanda suke sauka saman goshinta gida kam ya cika da jama'a ya kaure da koke koke mi'kewa Baffah yai da'kyar yabar gurin yayin da masu wankan gawa suka dauketa domin mata sutura bayan su kammala akace ba damar kaita dare yayi saida safe haka tai kwanan keso.
Washe gari da wuri bayan anyi sallar asuba aka mi'kata makwancinta kafin suka dawo zaman makoki da sauran mutane da ba'ki lokacin da aka dawowa da Ramatu zanin da aka lullu'bi Lami dashi nan sabon kuka ya tashi da bori har rirri'keta ake ana dankwafarta da lallahi da bata hakurin cewa addu'a zatai mata ba kuka ba.
Tashin hankali wanda ba'a sa masa rana lokacin da su Musbahu suka labarin karyatawa sukai saida suka zo suka gani da idanuwan su Musbahu yayi kuka ya kara kamar mace balle mama da Naja'atu alpha kuwa tunda ya suma bai farfad'o ba sai a gadon asibiti ya ganshi kwance daure da ledar ruwa hannu yasa ya fisge yana tashi zaune tare da saukowa daga gadon yayo waje likita daya taho d'akin zai sake duba shi ganinsa ya fita sai layi yake yace "a'a ina zaka je baka samu lafiya ba please yalla'bai mu koma ka kwanta" ko sauraron sa alpha baiyi ba yai gaba da sauri likitan yabi bayan shi yana masa magiya.
"Dan Allah ka saurare ni ka dawo ciki na duba ka".
Tamkar da gunki likita ke magana haka Alpha yai banza dashi yaci gaba da tafiya batare da ya kalli kowa ba kasa nutsuwa doctor yai domin yasan waye alpha d'an babban mutum ne duk abinda ya same shi yanzu shi za'a tuhuma bai daina binsa ba har suka fito harabar hospital din anan ya hango mom din Alpha da sauri yaje yana cewa "hajiya dan Allah ki taimaka kiyi masa magana ko zai tsaya", kallon Alpha daya nufi hanyar fita a gate din hospital tayi tare da girgiza kai tace "karka damu doctor zan dawo dashi" tana fadin haka tabi bayansa itama da sauri taga inda ya nufa domin basu taho tare da abbansa ba.
Tsaye ta same shi jikin wani karfe ya kifa kanshi yayi shiru tsayawa tai a bayansa tare da sauke ajiyar zuciya tace "Alpha" bai juyo ba kuma bai amsa ba 'kara matsawa tayi kusa dashi tana dafa shi tace "Alpha me ya faru"? Har lokacin shiru baiyi magana ba juyo dashi tayi tana rike hannunsa cikin lallashi ta soma tafiya dashi tana cewa "haba alpha kaifa musulunci ne ka dau kaddara komai yai zafi maganinsa Allah na sani Lami rayuwar kace kuma kana kaunarta amma wanda ya halicce ta ya fika sonta shiyasa ya kar'bi kayarsa kayi adduar ta samu rahma da haske a kabarinta shine yanzu abinda take bukata kuma kaunar daya rage ka nuna mata kenan kaji", Alpha tari dabai kama shiba baiyi ba ganin haka yasa dole ta 'kyale shi tasan baya cikin hankalin sa doctor na tsaye yaga sun shigo d'an sauke numfashi yayi yana cewa "kiyi hakuri hajiya nayi kokarin dakatar dashi bai saurare ni ba" kai ta girgiza "a'a babu komai doctor nasani muje ka mayar dashi ya kamata ya samu hutu na d'an lokaci" "to shikenan hajiya" doctor ya fad'a yana bud'e kofa ya shiga suka bi bayanshi.
Anyi sadakar uku ba'ki wasu suka fara tafiya saura kadan suma bayan bakwai suka dauri niyya suka koma garuruwan su domin Baffah mai jama'a ne sosai.
Zaune Sabi'u da Habu suke a gaban Baffah suna masa 'korafin abinda akaiwa Lami wanda basu san waye ba Habu ne ya fara magana.
"Yanzu Baffah shikenan haka zamu zuba ido baza ayi binciken wanda ya aikatawa Lami wannan rashin imanin ba gaskiya baza mu yarda ba sai mun kai rahoto gurin 'yan sanda a zo garin nan a tsananta bincike duk wanda yake da hannu sai an hukunta shi".
Tarar numfashinsa Sabi'u yayi "eh 'kwarai Habu wallahi baza mu yarda sai an bi mana kadin wanda yai sanadin yarinyar nan taya za'ai mata haka mu 'kyale kamar wacce bata da gata dole mu tashi musan abin yi amma me kace Baffah"?.
Shiru yai duk damuwa ta addabe shi ya rasa inda zaisa kansa yaji dad'i yana matukar takaicin rashin yarinyar nan yayi kuka ya 'kara harya gode Allah mutuwa lokaci in yazo ba jira amma Ramatu ta cuceshi bazai ta'ba yafe mata ba a rayuwa................................
Tunanin sane ya katse jin Sabi'u na cewa "Baffah baka ce komai ba"?.
'Dagowa Baffah yayi yana kallon dukkan su biyun cikin nazari ya sauke ajiyar zuciya yana cewa "Sabi'u Habubakar Allah yai muku albarka ya albarkaci rayuwar ku da zuriyar ku na amince da abinda kuka ce kuma na yarda ku dauki mataki akan koma waye ya cutar da Lami kuyi bincike ni na amsa muku da yardata Allah ya taimake ku ya tona asirin wanda yai mata haka yasa bazai gama da duniya lafiya ba".
Da sauri Habu yace "Amin Baffah daga yau yanzu idan muka fita zamu fara aikin mu Baffah ka taya mu da addu'a mu samu nasara matukar aka samu wanda yai mata wannan rashin imanin shima a take zamu kashe shi dan wallahi bai isa mu rabu dashi yaci bulus ba".
"Kwarai Habu kayi gaskiya tashi muje yanzu ma kuwa" Sabi'u ya fad'a yana mi'kewa tarar zancen nasu Baffah yai "a'a Habubakar karku kuje kuyi abinda za'ai dana sani dan Allah ku bi a sannu kunji"? "To shikenan Baffah zamu kula Yaya Sabi'u zo muje" fita sukai Baffah daya bisu da kallo hawaye na zuba a idonsa yana farin ciki da samun su matsayin 'ya'yansa.
Gidan da suka d'aukata sukaje dube dube suka fara amma dai basu ga wata alama ba jingina jikin bango Habu yai yana cewa "tsaya yaya Sabi'u nifa na kasa fahimta musamman yanzu da muka zo nan".
D'agowa Sabi'u yai "kamar ya ban gane ba"?.
Kallon daidai inda suka ganta kwance Habu yai yana cewa "ka duba man lokacin akwai alamomi sakamakon muna rud'e ya hana na tsaya amma wanda yai hakan yabar alamar wani abu kai baka gani ba"?.
Shiru Sabi'u yai yana tunani zuwa wani lokaci yace "amma kai a ganinka waye zai iya yi mata haka a garin nan da kewayen mu waye shi".
Rufe ido Habu yai ya kasa cewa komai abubuwa yake tunawa suna masa yawo a kunne ya riski zancen da Lami tayi da su Tanko lokacin zai fito harya tsaya ya saurari wani abu kamar inda Tanko ke cewa saiya sa tayi kuka da idonta tayi nadama.
Da sauri ya bud'e idon yana kallon Sabi'u yace "yaya Sabi'u tabbas akwai wani abu ina zargin mutum daya wallahi shine kuma ko kaffara bazan ba shi ya aikata mata haka" "waye habu wa kake tunani a ina yake yanzu muje"?.
Kallon Sabi'u Habu yai yana d'an d'aga kansa sama alamar tunani a hankali yace "Tanko ne yaya Sabi'u tabbas shine ba kowa ba" zaro ido Sabi'u yayi yana 'kure Habu da kallo yace "Tanko kuma? Habu Tanko dai da na sani d'an gidan malam Balah saurayin ta? Meyasa kake zargin sa"?.
Ri'ke hannunsa Habu yai yana cewa "kwarai shi nake zargi kasan wani abu na ta'ba jin suna hira da ita shida abokinsa Mudi akan saita rabu da yaron nan Alpha ta aureshi saboda ta'ki amincewa ta shiga gida basu san ina la'be ba suke cewa zatai nadama da dana sani a rayuwar ta dan haka dole nace sune".
"Habu ka tabbata kaji haka"?.
"Eh yaya Sabi'u wallahi da kunne na naji lokacin da suke wannan maganar da ace bishiyar kofar gidan mu tana magana zata bada sheda".
Kai Sabi'u ya jinjina "shikenan Baffah yace kada muyi abinda za'ai dana sani amma ba baza mu 'kyale ba yanzu muje mu same su" fita sukai kai tsaye dandali suka nufa sukai sa'a suna majalisar su harda Ilyah tsayawa daga gefe Sabi'u yai yana cewa "je kayo mana magana dasu" kai Habu ya d'aga yana karasawa yai musu sallama tare da baiwa kowa hannu suka gaisa yana kallon Tanko yace "kadan zo zamuyi magana yanzu" dafa 'kirji Tanko yai idonsa kamar zai fito waje yace "ni"? Wata uwar harara Habu ya sakar masa yana cewa "a'a ba kaiba ni" saroro Tanko yai jikin sa na 'bari yana kallon habu wanda takaici ya gama cika shi cikin tsawa yace "dallacan kana bata min lokaci zaka taso ko saina figoka"?.
A zabure Tanko ya mi'ke tun kafin ya d'ebi takalmi Habu ya jashi kiiiiii suka je gurin Sabi'u sannan ya dawo yana cewa Mudi "malam saura kai kake 'kwalalo min ido" shima jiki a sanyaye ya mi'ke suka fita ganin sun fara tafiya yasa Mudi cewa "ina zamu je"?.
"Ka biyo mu man zaka gani ai" ya fad'a yana sake tisa 'keyar sa gaba har suke cikin kangon gidan nan juyowa Sabi'u yayi yana nuna musu gurin yace "Tanko wanne irin rashin imanin ne haka me Lami tayi maka zakai mata fayd'e gashi ka zama silar mutuwarta"?.
A wannan lokacin tsabar firgici Tanko har saida ya 'kwaru muryarsa a sha'ke da'kyar yace "ni kuma amma Allah ya isa na sharri zaku min ina ruwa na da ita me tamin zanyi mata haka aiko bazan yarda ba saina kai ku gurin me gari".
A fusace Habu ya sha'ki wuyan rigar Tanko yana naushin sa yace "sharri ma kace zamuyi maka tsinanne asararre wallahi yau saika amsa laifinka ko kaima ka ba'kunci lahira ka gano abinda ake gani" ya karasa maganar yana sake dam'ke wuyan Tanko wanda idonsa suka fito waje.
Ganin Habu na neman yi masa illa yasa Sabi'u cewa "ka sake shi Habu kada kaji masa ciwon da zamu zo shari'a ta kada mu" saida habu ya gwara kan Tanko da bango yaga ya fad'i baya motsi sannan ya rabu dashi yana huci ya maida kallon sa kan Mudi da yake rarraba ido alamun rashin gaskiya ya bayyana a fuskarsa 'kiri 'kiri.
Kamar wanda zai fad'a masa ya kashe shi haka habu yai kansa gadan gadan yana cewa "kai kuma munafiki zaka fad'i gaskiya ko kaima saina tura ka suman kamar abokin naka? FA'DI MANA" yai maganar a tsawace.
Jikin Mudi na rawa yace "dan Allah Habu ka tsaya ni bansan komai ba".
Wani kallo yai masa na baka da hankali amma zan koya maka kafin yace "kace bakasan komai ba ko? Haka kace ko? Lallai yau saina bambance maka abinda ake kira da jaki sha duka" warto shi yai tare da d'uma shi da 'kasa yabi ya take ya hau jibgarsa da dukkan karfi sa ihu Mudi keyi yana neman agaji Sabi'u na tsaye da yake baida zafin rai kamar Habu amma bazai hana shi dukan nasu harsai sun amsa cewa eh.
Jin da Mudi yai idan ya sake za'ai bashi yasa cikin wahala da numfashi da'kyar yace "dan Allah Habu ka tsaya zan fad'a maka gaskiya wallahi zan fad'i gaskiya karka kashe ni zaka 'balla min 'kafa" jin haka yasa da gudu Sabi'u yaje yana 'bam'bare Habu daga ruwan cikin Mudi yai dauke shi yai gefe dashi.
Yana cewa "tsaya haka Habu yanzu zaiyi bayani" huci Habu keyi yana kallon Tanko dake kwance sharkaf kamar matacce a hasale yaje ya wanka masa wani irin gigitaccen mari me karfi sai ga Tanko ya mi'ke tsaye a firgice yana neman hanyar guduwa dam'ko shi Habu yai yana maka shi da 'kasa yace.
"Gidan uban wa zakaje"? Idan kaga na barka ka fita anan to saidai ka fad'a min amsar tambayar danai maka meyasa kaiwa Lami fayd'e"? Zaka fad'a ko saina fasa ma kai"?.
Ganin ya cakumo shi yana dunkule hannunsa zai kai masa naushi yasa jikin Tanko na rawa bakinsa na jini yace "zan fad'a dan Allah kamin hakuri wallahi zan fad'a maka gaskiya".
Sakin sa Habu yai yana kallon Sabi'u yace "kasan Allah yaya Sabi'u bazan 'kyale su fita nan cikin hayyacin su ba indai basu fad'i gaskiya ba saina dau fansar abinda sukai mata kamar yadda kai ka fad'a a kofar gidan mu dan na jika" ya karasa maganar yana kallon Tanko dake ta goge jinin da ya 'bata masa fuska.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana sha'kar wuyan rigarsa 'kara Tanko yana cewa "Habu zaka yanka min wuya dan Allah ka sake ni zan fad'a maka".
Habu bai sake shiba saidai ya sassauta ri'kon da yai masa fuskarsa a d'aure tamau yace "ina jinka".
Jikin Tanko na 'barin tsoro bakinsa na rawa ya fara magana "dan Allah Habu kuyi hakuri ku yafe min na aikata muku kuskure tabbas nine naiwa Lami fayd'e ranar amma dan girman Allah ku dube ni da idanun rahma ku yafe min"..........................
Takaici ne ya rufe Sabi'u yana kallon Tanko yace "kenan zargin mu ya tabbata kaine silar mutuwarta me tai maka zaka dau alhakin ta"?.
Muryar Tanko na rawa yace "babu abinda tai min kawai naji haushi ne saboda tace min bazata aure ni ba na makara shine abun ya 'kona min na tare ta a ranar na mata fayd'e ba da niyyar kasheta na mata haka ba wallahi da nasan zaka mutu bazan yi mata ba kawai ganin ta gane ni yasa na kasa barinta dan karta tona min asiri har saida naji bata motsi ku gafarce n.....................
Bai karasa ba Habu ya d'auke shi da mari yana hankad'a shi ya mi'ke ransa a 'bace ya goge hawayen fuskarsa yana kallon Sabi'u yace "wallahi tallahi bazamu yarda ba yaya sai munkai 'kararsu gaban hukuma dole ne a yanke musu hukuncin daya dace dasu".
Kai Sabi'u ya jinjina yana cewa "muje" fita sukai daga gidan yayin da Mudi ya tashi a guje yana zuwa gurin Tanko dake kwance yana numfashi ya d'ago shi yana mikar dashi tsaye yace "sannu abokina gaskiya habu ya cika 'kasurgumin mugu kaga yadda duk ya sauya ma kamanni Allah ne yai da sauran kwanan ka a gaba da yanzu ya kashe ka" shidai Tanko shiru yai ya kasa magana cikin azaba da'kyar yake jan kafa suka fita daga gidan.
Bayan fitar su Habu kai tsaye gida suka nufa a kofar gidan suka samu Baffah zaune yayi ba'ki dan haka basuyi masa magana bayan sun gaisa suka wuce zuwa ciki suna jiransa ba'a dad'e ba shima ya shigo tare da zama kan wani 'karamin dutsi dake kafe a wajen kofar d'akinsa yana kallon yadda yanayin ya sauya yasan ba kalau ba akwai matsala.
"Sabi'u Habubakar me ya faru nagan ku haka ko kun samu wani bayani ne".
Kai Sabi'u ya d'aga "eh Baffah samu ma na ha'ki'ka Habu ya baka labari".
Maida kallon kan Habu Baffah yai yana cewa "Habubakar meya faru ne na ganku cikin fushi musamman ma kai"?.
Zazzafan numfashi Habu ya sauke yana cewa "wallahi Baffah baza mu yarda ba sai munje kotu wai tsabar zalunci ashe wannan tsinannan ne Tanko ya mata fayd'en bamu sani ba gashi yanzu da yaji wahala ya fad'a da bakinsa harda dan kada takai labari yasa bai 'kyale taba saida ta daina motsi".
Runtse ido Baffah yai jin abinda Habu ke cewa basu ankara ba sai ganin hawaye sukai sharr yana zuba a idanun Baffah tabdijan tashin hankali wanda ba'a sa masa rana hawaye fa suke ganin a idanun Baffah a zabure cikin tsananin fushi habu ya mi'ke yana cewa "wallahi bazan kyale Tanko ba Baffah saina kashe shi tunda yai silar zubar hawaye a idonka abunda ban ta'ba gani tare dakai ba a rayuwa ta sai yau" juyawa yai zai fita muryar Baffah da alamun kuka yace.
"Habubakar dawo kada ka koma gurin su na barwa Allah shine ya halicce mu sannan shike da iko damu zai sakawa Lami bazai kyale shiba Tanko ya cuce bazan ta'ba yafe masa ba har ranar komawa ta ga ubangiji" ya karasa maganar kukan nasa na sake fitowa.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana kifa kanshi a jikin Baffah kawai shima ya fara kuka wanda Sabi'u da sauri ya rungume su shima yana zubda hawaye suna wannan hali sukaji sallama yaro.
"Wai Baffah yana nan yazo inji Isubu me gari yana nemansa".
'Dagowa Baffah yayi yana kallon yaron cikin ajiyar zuciya yace "kace masa gani nan ina zuwa" yaro na fita Baffah ya mi'ke yana daukar buta ya wanke fuskarsa.
Ran Habu a 'bace yace "wato 'kara suka kai gurin me gari? Aiko yau saina tabbatar basuyi kwanan gida ba wallahi saina d'ebo musu hukuma muje Baffah.
Baffah bai iya magana ba kawai yayi gaba ne suka bishi a baya har gaban me gari suka samu guri dam ya cika da jama'a ma'kil ana ta hayaniya sallama Baffah yai yana zama cikin mutunci suka gaisa da kowa.
Kallon sa me gari yai "Baffah kasan dalilin kiranka?.
Kai Baffah ya girgiza "a'a ina fata lafiya"?.
Cigaba me gari yai "eh lafiya ba lafiya malam Balah ne ya kawo 'kararka cewa Habu da Sabi'u sun daki d'ansa Tanko harda rauni sukayi masa ga sun zubar masa da ha'kora guda biyu haka ne"?.
Kallon su Sabi'u Baffah yai ganin basu musa ba yace "gasu nan me gari ka tambaye su ni ban sani ba".
Kafin me gari yai magana Balah yace "a 'kwarai ka turo suwa adamu dukan mutuwa sannan kace wai baka san komai ba wallahi bazan yarda ba sai munyi shari'a dakai" gun me gari ya juya yana cigaba "me gari nifa ba cewa nai a tambaye shiba kuma ba sasanto naso ba idan bazaka iya ba zan kai gaba a bimin kadin dukan da sukai masa".
Shiru Baffah yai yana kallon Balah cikin mamaki wato d'ansa ya aikata wannan mummunan zunubin amma tsabar tsaurin ido har ya samu bakin magana.
Hayaniyar da suka kaure tsakanin Habu da Balah ne ya dawo da Baffah daga tunanin da yake yana cewa "Habubakar kayi shiru wannan ba zancen ka bane"
Shiru yai Balah dake binsa da kallo yace "kai mara kunya ba dakai nake yi ba da ubanka nake magana ba hurumin ka bane" a harzu'ke Habu zai magana Baffah ya dakatar dashi, mi'kewa