Showing 111001 words to 114000 words out of 130249 words
komai a gaban kowa".
"Amma Ameer..................................
"A'a Ajeeb basai kace komai ba na fahimta yanzu muje gurin Mami daga baya ma karasa maganar".
"Ok shikenan amma wallahi yadda ya 'kona min rai shima saina hukuntashi ta inda baya zato".
Dariya Ameer yai yana cewa "tofa me zakai masa karfa ka jawo mana tashin hankali a gida idan kace dole yazo nasan zai iya yazo d'in kuma ya aikata abinda yace ya kasheta kasan Asad daya hauro zaku ri'ka uban dambe kamar wasu 'yan wrestling dan ma yanzu hankali yazo an girma an rage wasu abubuwan"?.
"Ba wani tashin hankali kawai kayi shiru kai kam Allah ya kaimu lokaci ya dawo wallahi saina bashi mamaki zan firgitashi idan yana jin kansa shi Aliyu Asad ne to zaisan nima Aliyu Ajeeb ba kanwar lasa bane😡 zan nuna masa isa da mallaka zai gane Allah da girma yake".
Murmushi Ameer yai yana girgiza kai yace "Uhm Ajeeb bansan meyasa ka zafafa al'amarin Khimiyyah ba bayan bakasan komai ba to kodai sonta kake"? Ameer ya karasa maganar yana kau dakai ya soma dariya.
'Dan bugarsa a baya Ajeeb yai yana cewa "so dai wanda na sani da zakacewa budurwa ina son ki shi kake nufi"?.
Kallonsa Ameer yai "eh shi nake nufi man".
Kai Ajeeb ya girgiza yana cewa "inaaa ko d'aya babu so tsakani na da ita saina 'yan uwankmtaka amma badai maganar aure ba kawai ina fad'a ne dason 'kwata mata hakkinta dan kaf cikinsu babu wacce tai min indai a matar aure ne bazanyi auren had'i ba".
"Humm mukwa kaga shi zamuyi".
Da mamaki Ajeeb ya kalleshi "da gaske kake amma wace a ciki"?.
"Kai wace kaga ta dace dani"?.
Shiru Ajeeb yai cikin tunani yace "a'a ai bansan abinda ke ranka ba kasan ra'ayi riga".
"Eh haka ne amma na baka za'bi banda Khimiyyah ka fitar min d'aya a cikinsu uku sai ayi tuwona maina ga abu a gida ai bazamu fita waje mu auro ba ko ya kace"?.
Kai Ajeeb ya jinjina "eh kun kyauta saidai gaskiya a cikin su kamar ina ganin Shaukiyyah tafi dacewa dakai".
Dakatawa Ameer yai yana cewa "da gaske tafi dacewa dani"?.
Kai Ajeeb ya d'aga "eh a nawa ganin ba".
"Ok Ajeeb dakata ka bud'e idonka ka kalleni dakyau ka za'ba min"?.
"Allah da gaske nake Shaukiyyah tafi saidai kai bansan wacce kake hari ba Makiyyah ce ko Khaldiyyah"?.
"A'a nima ta takan gaskiya dama tun tuni a raina Shaukiyyah na za'ba saidai na sake baka za'bi ne saboda ko zakaga wacce tafi dacewa dani sannan nifa ba sosai nake bambancewa tsakanin ta da Makiyyah ba tunda kaga kamar su d'aya".
"No akwai hanyar ganesu mana ai Makiyyah tafi Shaukiyyah fad'in fuska sannan ita kuma Shaukiyyah tafi Makiyyah haske da dogon hanci kai baka ta'ba lura ba"?.
Kai Ameer ya d'aga "eh gaskiya ban ta'ba ba saidai yanzu na tsaya na ganeta kar wata rana naji kunya garin kiran Shaukiyyah na kira Makiyyah".
Murmushi Ajeeb yai "idan ka kirata ba matsala ranar sai ayi hirar da ita a maimakon Shaukiyyan".
Kai Ameer ya jinjina yana cewa "to amma kai babu wacce tai maka a cikinsu ka za'bi Makiyyan shikenan tunda kaga ita Khaldiyyah Annur takewa naci dan ya'ki ne".
"Hum ai kasan Annur d'in sai a hankali muskili ne halinsu daya da Asad ko yana sonta bazai nuna ba saiya wahalar da ita Makiyyah kuma saidai ta auri wani a waje ita da Khimiyyah dan nikam wallahi bazan auri 'yar gida ba ba wacce taimin a cikin su".
Dariya Ameer yai "tofa wacece a wajen kake so"?.
Kafad'a Ajeeb ya d'aga "oho nima ban santa ba sai ranar da Allah ya had'amu".
"Ok baka da garanti tsayayya"?.
"Eh banda ita".
"Amma Asad fa"?.
Zaro ido Ajeeb yai "tab wannan mara hankali ubanwa zai d"au 'ya ya bashi😂 indai uban ba tsanar ta yaiba saidai ya had'ota da likafani dan maybe dukan dazai mata sai yafi na Khimiyyah itakam washe gari zai waye matane a 'kabari".
Da mamaki Ameer yace "meyasa kace haka"?.
"Ameer dubawa nai Asad d'an damuwa ne fiye da tunanin mai tunani shiyasa nace haka dan wallahi na tabbata duk yarinyar da tsautsayi ya afka kanta ta aureshi tofa ta kad'e har ganyenta dan abinda na lura Asad ko yana son mace ya aureta uhmm balle ace ta cushe ce me kake tunani zai faru shifa Asad babu aure a tsarinsa ya dad'e da fad'a min wannan"?.
Dariya Ameer yai yana kallon Ajeeb dayai masa magana da serious face yace "babu abinda zai faru sai alkhairi kasan da muna tunanin tsaurin sa zai iya bamu mamaki yayi sanyi".
"Me? Yayi sanyi fa kace Asad d'in tab gaskiya abunfa da kamar wuya a yadda Asad yake ace babu neman shawararshi babu sanar masa kawai yaji an d'aura masa aure subahanallahi ranar kuwa da anga tashin hankali wanda ba'ai zato ba iri-iri Asad Asad uhmm Allah ya kiyaye" Ajeeb na rufe baki Ameer ya kama dariya wato yana jin dad'in gidan su drama bata karewa.
"Kai Ajeeb da alama dai Asad yayi zafi da yawa yanzu dai mubar wannan maganar ya kake gani Shaukiyyah ce taimin meye shawararka"?
"Ok indai haka ne kad'au Shaukiyyan kunfi dacewa".
"Shikenan Ajeeb na gode amma dan Allah karka fad'a mata so nake sai an gama case din Asad da Khimiyyah hankali ya kwanta kafin zan bayyana kowa ya sani".
"Ok babu damuwa Ameer muje dare ya fara nisa kuma Mami da Annur nasan suna can suna jiranmu tunda ga abinda likitan yace idan Allah ya kaimu gobe darai sai mu Kira abba ansan abin yi".
Wucewa sukai babu wanda ya kara cewa wani abu har suka koma a zaune suka samu Mami tare da Annur suna hira zama sukai Ajeeb daya kasa durtsuwa abin nacin ransa yace.
"Wai Mami yanzu tsakani da Allah bazakiwa Asad magana yazo ya duba yarinyar nan ba idan fa ana ta 'barawo ayita mabi sau koda ace laifin Khimiyyah ne tunda Asad yake nuna halin ko in kula akanta dole mahaifiyarta taga kamar shine mara gaskiya kuma ko mahaifin ta kara yake da yake cewa koda ace kasheta yai haka za'ai shiru laifin d'an uwa daud'ar gora ne duk da haka ba dad'i yadda ya d'aukaki Asad a cikinmu tun muna yara komai yace d'an gidana komai d'an gidana bai kamata ya saka masa ta wannan hanyarba haba koni da muke uwa d'aya uba d'aya Asad yaiwa haka zanji haushi".
Kallonsa Mami tai tana cewa "zauna ka nutsu Ajeeb yanzun wani abune ya faru"?.
Zama Ajeeb yana sake kallon numbar Asad d'in kamar zai Kira sai kuma ya fasa yana mayar da hanakalinsa kan Mami yace "na kirashi yanzu bayan mun fito daga gurin doctor nace masa yazo ya duba Khimiyyah amma yana fad'a min wani bazai zoba idan kuma na matsa yazo saiya kasheta dama ba ha'kura yaiba tilas ya barta saboda ke kiji shi Mami".
Tashi sukai zasu tafi masaukinsu Mami tace "Ajeeb kaima kasan waye Asad basai na tuna maka ba dama da mai nasara yace a 'kyale shi daka barshi domin idan kace dole ta 'karfi zakabi shi Asad bazai bi umarninka ba".
"Amma Mami saina zuba masa ido har yana maganar ko yanzu suka had'u saiya kashe ta".
"Eh ya fad'a ne kawai babu abinda zai sake had'asu insha Allahu Ina fata yarinyar nan ta tashi kuma ta dawo cikin hayyacinta ayi komai a gama wannan tashin hankalin ya isheni Sultana Hadizah ba mace ce mai kara ba kuma ko ba haka ba ta ta'ba cewa mighty Alhussain yafi sonku saboda ku maza ne akan su Khimiyyah".
"Amma Mami wannan sa'banin fahimta ne ba haka abin yake ba".
Itakam haka ta dauka haka ne, Asad yasan abinda yake baya aiki babu lissafi saidai nayi mamakin miye ya had'asu nima bazance ba Asad ne yake da gaskiya ba dan yana d'ana fatana ta farfad'o kawai".
"Humm Mami Asad ai yasan baiyi daidai ba amma kana masa magana zai hayayya'ko kanka da fad'a kamar zai rufe ka da duka wallahi kwanan baya Mami da ina masa magana cewa yai zai saitani da bindiga daga inda yake ya harbeni".
Murmushi Mami tai "shi Asad d'in ne yace haka? Harbi fa"?.
"Kwarai Mami haka yace saboda yana gadarar shi soja ne yana da makami harda min barazana".
"Amma Ajeeb naga harbi a hannunsa ranar da abinda ya faru waye ya harbeshi ko Khimiyyan ce"?.
"No Mami ba Khimiyyah bace nine".
"Kaine ka harbeshi amma meyasa kasan abinda ya had'asu ne ko kana part d'in"?.
"A'a ban sani ba kawai Ameer ya tambaye inda yake nace rabona dashi tun a wajen sallar asuba amma bari naje part dinsa na gano zuwan danai na tarar yana dukanta kamar yana dukan 'karfe ko itace ya zage da dukkan 'karfinsa ya sha'ke mata wuya shine fa naje kiranku bansan meya had'o suba yanzu iya lallahi da magana mai dad'i nayi akan ya fad'a min laifin da tai masa ya'ki ki gwada kiransa ko zamuyi sa'a ya fad'a miki Mami nikam in son sanin gaskiyar abinda ya had'asu".
"Ai Asad bazai ta'ba fad'a maka ba komai zakai kuma dama u're highness yace min na 'kyale shi harsai Khimiyyah ta farfad'o shi kuma ya dawo dan haka abinda nake so dakai idan ka kirashi a waya ka daina masa wannan maganar tunda mai nasara yace a bari ta samu lafiya".
"To shikenan Mami Allah ya bata lafiya".
"Amin Ajeeb" sauran ta kalla tana cewa "Ameer Annur kuxo mu tafi Allah ya rufa asiri" mi'kewa sukai suna fita a hospital din zuwa hotel din da suka kama.
CAMEROON
Alhamdulillah yanzu kam alhaji Idris ya baiwa su malam Habu aikin majinsa a wani karamin ofishin dattawa kuma babu laifi ana biyansu albashi mai d'an tsoka har sun fara tara kud'i a gurin hajiya mammah mai abinci.
Akwai wani mutum munafiki sunansa Haliru a cikin ma'aikatan gurin yana da zagon kasa sosai yake jin haushin su malam Habu duba da cewa sunzo sama takai Allah ya bashi farin jini sun d'aukaka agun mafi yawan ma'aikata sun sansu kuma suna yi dasu hakan yana 'kona ran Haliru a 'bangare guda ga yaron alhaji Idris (komai da ruwanka) zama masinjoji dasu malam Habu ba karamin firgitashi yaiba saboda yanzu duk wani kud'i da Alhaji Idrisu zai bayar a rabawa mutane harda su a ciki suna tsaye zai rabawa mutane sisi bai isa ya tafi dashi ba sun kafa sun tsare ba'kin ciki ya gama isarsa ya tsanesu ji take kamar ya kashesu da ransu shiyasa Sam basa shiri ko hannu suka bashi da sunan gaisuwa baya kar'ba sai harara sai zagi haka kud'i yana gama rabawa zai wulla musu jakar yana hucin takaici yabar gurin har dariya yake basu saidai sunyi alkawarin har subar Cameroon kamar yadda suka cewa alhaji Idrisun bazasu ci amanarsa ba zasu ri'ke komai tsakani da Allah Malam komai da ruwanka yaso su had'a baki su ri'ka cutar alhaji Idrisu zasu koma Nigeria da ma'kudan kud'i su kuma suka a'a shikenan ya d'aura gaba dasu kome ya had'o su sai zage da hantara.
😘MRS AL-AMEEN AHMAD CE😘
KAI WASH ALLAH NA TYPING 📲 AKWAI WUYA😣 KUYI HAKURI FANS YAU BA YAWA NA GAJI NE ANAN ZAMU TSAYA MU KWANA SAI MAI DUKKA YA BAMU ARON RAI ZUWA GOBE INSHA ALLAHU ZAMU D'ORA LITTAFIN ME KAMAR SARKI 👑 INDA MUKA TSAYA👌.
See you next time we will meet again tanks for ur support Allah ya d'aukaka ku fans d'ina ina yinku babu adadi😘🌹.
💋YUSRAH MUSA ABUBAKAR💋
BARKAN MU DA KWANA MASOYA YAN GROUP DIN ANNURI WRITER'S ASS💫 DA SAFREEYYAH FANS GROUP🍇👌 DA MR HAUSA EBOOKS AND VIP WOMEN 24TV NOVELS INA MIKO GAISUWA MAI TARIN YAWA GAREKU FATAN RAHMAR ALLAH TA TABBATA A GAREKU.
TYPING 📲 Fri, Jul, 19/24 03:43PM (+_+)(+_+) Little Zaran Aunty💃.
💞ME KAMAR SARKI💞
____________________
____________________________
___________________________________
ANNURI WRITER'S ASSOCIATION💫
🏠Home of 🤗hospitality and 🌲harmony🤙gidan kar'ba hannu biyu da zaman lafiya🙅.
STORY AND WRITTEN
✍️Yusrah Musa Abubakar
MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CÊ😘
Wannan page naku ne 'yarana ta kaina Allah ya rayaku kan tafarki madaukaki akan hanya ta shiriya da turba ta musulunci Amin.
💞FATIMA ZARAH (ILHAM)
💞HABEEBAT (IKRAM).
51-~AL-HAQQU
The Truth
52~AL-WAKILU
The trustee
25~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil 'Dayyibina.
🌄INSIST ND JEER🌄
Episode 51&52
Kamar yadda Asabe ta umarci Balarabe cewa yayiwa liman magana idan akwai wanda zai auri Indo sadaka haka yayi da asuba bayan anyi sallah a masallaci liman yace kada kowa ya fita akwai sanarwa saida yayi addu'a aka shafa sannan ya juyo yana fuskantar mutane da Sallama a bakinsa bayansun amsa ya fara bayani kamar haka.
"Assamu alaikum jama'a kunji nace ku dakata ko? To ba wani abu bane dama sa'ko ne zan fad'a na sauke nauyi daga Malam Balarabe yace a sanar muku cewa 'yarsa Indo ta kawo mizanin aure hartana neman wuce iyaka amma babu wanda ya ta'ba zuwa kofar gidansa da sunan yana sonta shiyasa ya gaji ya kawo tallar sadakarta masallaci idan Allah yasa akwai wanda baida karfin yin aure ga mace sadaka bayan mun fita zaka iya zuwa gidan malam Ka sameshi saiku tattauna Allah yasa mu dace assalamu alaikum" ya karasa maganar yana mi'kewa ya fita sannan sauran mutane suma suka tashi suna rufa masa baya kowa mamaki ya rufeshi na wannan irin tagayyara da Balarabe yazo yaiwa 'yarsa yana yayata asirin gidansa ai saiya jawowa 'yar gori daga baya ko yasa ta zama 'karamar bazawara.
Malam Balarabe yana shiga gida Indo tana shara buguzun buguzun kamar zaibi ta kanta haka ya wuce fuuuu yana shiga d'akinsa da kallo Indo ta bishi hawaye shakaf a fuskarta ta gaza gane mene ainishin abinda dake damun Balarabe yau kusan wata uku da sakin Dalah ya hana taje ko sau d'aya ta ganota ga takura da tsinuwa iri iri da take kar'ba a gurin su shida Asabe ga bahijjah da take jin kanta tafi kowa gwalli da takura mata saita 'karawa Balarabe zagi 'kuyal yana ji tari bazai iya ba huuuuuhsh kawai ta sauke numfashi tana aje tsintsiyar zata shiga d'aki taji tsawar Asabe.
"Kee kee da'ki'kiya gidan uban wa zakije baki gama min aiki ba matsiyaciya mai ba'kin hali wato dama tun d'azu ashe shara kike da nace kiyi sauri ki hura min wuta shine kikai kunnen uwar shegu dani aiko yau sai naci uwar data haifi uwarki bankad'add'iya kawai".
Had'e rai Indo tai cikin takaici ta kalli Asabe duk da zuciyarta na bugawa ta dake domin abubuwan da take mata ya gama isarta gara ta fara mayar mata kota 'kwaci 'yancinta a gidan ubanta tasan itama 'yace ba tsintota akai ba tasan ko 'yar tsintuwa baza'ai mata irin wannan wulakancin da cin fuskar da ake mata ba......................
"Ke Indo dan uwar uwarki ba dake nake magana ba shine kika tsaya kallona saboda ga sa'ar gyatumarki ko nayi miki kama da mummunar tsohuwarki Dalah kome kike kallo idan kuma ke mayya ce nafi 'karfin ki".
Ba zato Asabe taji saukar muryar Indo tace "kada ki sake zagar min uwa".
Da sauri Asabe ta dubeta da tsananin mamaki ta zaro ido waje tana cewa "maimaita abinda kikace Indo ta yuwu ko kunne na ya fara samun matsala mema kika ce"?.
A fusace Indo tace "cewa nai kada ki sake zagar min uwa".
Baki Asabe ta bud'e tana kallon ta sama da 'kasa tace "karna sake zagar miki uwa?.
"Eh haka nace".
"Ohhh lallai yau kuwa saina nuna miki cewa kinyi kuskure kuma har kibar gidan nan wallahi bazan sake sassauta miki ba wahala da damuwa yanzu kika fara sha".
Kai Indo ta girgiza tana cewa "kece a wahale bani ba domin ni bana dauke da alhakin kowa a kaina amma kefa kin cuci mahaifana kin lalata musu zama kin zama ba'kar ashana ba'kar mace mai ba'kin hali Allah wadaren mata irinki Asabe kuma insha Allahu zakiga 'karshen ki ina mai tabbatar miki bazai kyau ba dole ki girbi abinda kika shuka zaki dana sani a lokacin da baida amfani"...............
"YA ISHEKI INDO" Asabe ta fad'a cikin tsawa tana kai mata sha'ka taci gaba "bari kiji ko uwarki Dalah bata isa fad'i in fad'a dani ba balle ke 'karamar alhaki yaushe har kikai bakin da zaki iya kallona kina magana? Heyyyyy yau ake yinta kan bala'i tabd'ijan BALARABE kai BALARABE kana ina? fito yau saina ci burar uban wannan tsinanniyar 'yar taka daga kai har ita sai kun yabawa aya za'kin ta" jin shiru yasa tace "kana ina ne munafiki gidan ubanwa ka shige ina magana kai burus wato ga wacce aka kunto daga turu ko"?.
Fitowa Balarabe yai da sauri yana cewa "lafiya meya faru"?.
Wata uwar harara Asabe ta sakar mata "oh abinda ya faru kake tambaya sabida ka zama tsohon kwantukwan ko? Nuna Indo tai da yatsa tana cewa "to wallahi wannan yarinyar yau saina kusan kasheta a gidan nan da hankali na ya kwanta".
A rikice Balarabe yace "metai miki"?.
"Au bakasan metai min ba kana cikin d'aki kanajin yadda take aiko min zagi tana tsiyatani sannan kace bakaji komai ba" ?.
Zaro ido Balarabe yai jiki na rawa yace "Indo d'ince ta zage ki"?.
A fusace Asabe tace "a'a ba ita bace ai kasan na saba 'karya shiyasa har zaka tsaya ja'inja dani wannan 'yar ba lallai jininka bace da jininka ce bazan ta'ba fad'a mata magana ta mayar min ba ka dau mataki yanzu ko nasa bahijjah ta kira 'kawayen ta su nad'a mata na jaki su mata kisan kawo wu'ka".
Tsaye Balarabe yai kamar bishiya yana kallon ta a tsawace Asabe tace "wai ubanme kake kallo ko yau ka ta'ba ganina d'an gidadawa nace ka mata shegen duka sannan hankalina ya kwanta kuma bada bulala ba kaga wancan iccen? Ta fad'a tana nuna masa wani sanda "to dashi zakai mata d'an ala tsinan duka wanda zaisa ta kama zazza'bin wuya.............,................
Katse mata magana wani yaro yai da cewa "salama alekum wai malam Balarabe yazo a kofar gida".
Kafin Balarabe yai magana da sauri Asabe cikin zumud'i tace "kai inji waye"?.
Juyawa yaron yai yana cewa "inji Iluh d'an garuwa wanda yake kwana a shagon gidan mu".
Wata irin gud'a Asabe ta saki tana cewa "ahayye nanaye ayuririiiiii nesa tazo kusa kwanan nan zan rabu da 'kaya na yada mangoro na huta da 'kuda masifa ta kusa barmin gida malam kayi sauri kaje man karya fusata ya tafi nasan kila sadakar dakai magana zaka bada wannan asararriyar ne yasashi zuwa idan ba haka ba muda ba ruwa muke saya ba mezai kawoshi"?.
Shiru Malam Balarabe yai kawai ya tsaya tsam yana tunani ba zato yaji Asabe ta hankad'a shi kamar baro ta tura shi hanyar kofar gida tana cewa "uban me