Showing 69001 words to 72000 words out of 130249 words
wani irin sanyi da naji yana ratsani kai gaskiya na gode Markah aikin bokan nan me kyau ne"
Dariya Markah "aha kin gani ko? Ai dama na fad'a miki karki gaggawa kice aiki baiyi kyau nasan waye bokana shiyasa na kaiki gurin sa dan nasan bazai saki 'kasa a gwiwa ba wannan somin ta'bi ne kika gani Asabe wallahi nan gaba idan kika aje kara Balarabe bai isa ya tsallaka ba muna nan dake zakice na fad'a miki" sauke ajiyar zuciya Asabe tai farin ciki ya gama cikata jiki na 'bari ta shiga d'aki sai gata da dubu hamsin kamar yadda taiwa Markah alkawari ta bata tana cewa "to ko yanzu nasan burina zai cika naga alama ga alkawarin danai miki nan" bakin Markah 'kin rufuwa yai godiya kuwa kamar wanda tayi mata kyautar miliyon ranar wuni tai a gidan sai bayan sallar magriba Asabe tayi mata Rakiya ta tafi gida.
Dalah na zaune Balarabe ya shigo yana zama d'an kallonsa tai tana cewa "daga ina haka na ganka afujajan tun d'azu da kace bari ka dawo sai naji shiru ko nisa kayi ne"? Shiru Balarabe yai yana sake kishingid'a kamar bazai magana sai kuma yace "daga anguwa nake" da sabon mamaki Dalah tace "anguwar gabas ko yamma wacce kaje" da yanayin fad'a yace "anguwar kudu da ta arewa naje ina ruwan ki da samun ido ko da haka kike idan na fita na dawo idan kuma yau zaki fara ki sanar dani" kasa rufe baki Dalah tai sai ido da take binsa dashi jin abinda bata saba jiba to kodai wani ne ya 'bata masa rai a waje sake kallonsa tai tana cewa "kayi hakuri bari a kawo maka abinci" zata mike yace "na 'koshi karki zuba" komawa tai ta zauna bata sake magana ba shima haka kamar kuma an taikare shi zunbur ya tashi zaune yana cewa "Dalah nifa aure zan 'kara" jiki a sanyaye Dalah tace "Allah ya sanya alkairi wacece"? "Kinsan Asabe"? Kaita girgiza "a'a ban santa ba" "to amma ai kinsan wacce ta baiwa Indo kosai kwanakin baya to itace" a d'an zabure Dalah tace "wai matar da tazo gidan nan kwanan baya" "eh ita" da mamaki Dalah ta kalleshi "amma kasan bazawararka ce harda kama ta da balbalin fad'a a gabana"? "Eh ai sannan banji ina son ta ba" sauke ajiyar zuciya Dalah tai "ai shikenan Allah yasa haka ne yafi alkairi idan kuma ba alkairi bace a tare dakai Allah ya baka wacce ta fita" caraf Balarabe yace "ai itace ma ki daina yimin fatan tsiya kodan kina ba'kin ciki zan karo miki kishiya ne" kai Dalah ta girgiza bata sake magana ba sai tsananin mamaki daya gama cika ranta mutumin daya hau fad'a ranar da tazo kamar zai daketa shine kuma yau me cewa yana sonta anya kalau ta barshi abun nan da dubawa.
Lokacin rabon da habu yake yi yayi ya sayo atamfofi da yadika kamar yadda ya saba gida gida da majalinsa haka yake rabon kaya da kud'i sosai yake shan addu'a shiyasa koda yaushe samunsa yake bun'kasa ga bikin suna ya gabato Habu yayi shirin sunan yarosa ya sayo komai da manyan raguna guda biyu ba'kin 'yan uwa kuwa har sunzo ana gobe suna jaririn ya rasu😣 innalillahi kamar babban mutum ne ya rasu haka gidan ya cika da jama'a kofar gidan ma haka sosai Habu mutuwar ta ratsa masa jiki ba shiba hatta sauran jama'a sun jajanta masa washe gari kowa cewa yake saidai a hakura da daurin auren Habu yace a'a kawai a d'aura haka akai daurin auren babu wani armashi ranar da yaron ya cika kwana bakwai da rasuwa ranar aka rako A'i.
Tashin hankali da bala'i iri iri Ramatu ta ri'ka saukewa Ilyah ta hana shi zaman lafiya har saida taga ya auri Maimuna sannan bakinta yai shiru ta 'kyale shi ya huta bayan sallar isha kad'an sai ganin tawaga Ramatu tai tana shigowa duk zaton ta masu rako Maimuna ne amma sai taga sunyi hanyar d'akin Bara'atu da gudu taje ta sha gaban su tare da cewa.
"Kai kai kai ya haka ku tsaya meye wannan daga ina zuwa ina?".
Da mamaki wata 'kanwar kandiya tace ", a'a kamar ya daga ina zuwa ina wanne wacce irin tambaya ce Bara'atu mana muku rako ta dawo d'akin mijinta" wani kallo Ramatu ta watsa mata tana cewa "ke kuma me kamar 'kanzo ki rufa min baki ban sauko dake ba da wannan asararriyar nake wato tsabar rashin zuciya ba'a je bikonki ba shine kika d'ebo wadannan murd'a murd'ar 'kafafun naki masu zubin doyar kudu kika dawo ko to wallahi bazaki shiga d'akin nan ba sai an kawo Maimuna kinji na fad'a miki dai ko"?.
Ri'ke baki Kulu tai tana kallon Ramatu tace "to ikon Allah wannan wulakancin har ina wai madai tsaya ma dai tukuna wace wannan me maganar uwarsa ce ko 'yar gayyar sod'i ce? Dan duk wacce tasan me take bazata tozarta mu haka ba"
Wata uwar harara Ramatu ta sakar mata tana sake tare kofar d'akin tace "au sannu isashshiya to uwar sace idan bakisan Ramatu ba ko kinajin labari na yau kin ganni" kai Kulu ta jinjina "tabd'ijan Allah ya sauwake wannan rashin arzikin naki har yai yawa ai da Kandiya zataji shawara ta Bara'atu bata samu gurin zama ba hartai shanya ba" kanta Ramatu tai "au jimin makirar mace dama ina ta isa samun gurin zama a gidan nan can da tsiyarta Ilyah yafi karfin aurenta dan haka zaku iya tattarawa ku juya inda kuke fito harda yin 'karyar tana da ciki wata shida ai zamu gani idan wata taran tayi kuma wallahi ba kinji nace haka ba nan gaba kikace ya 'bare sai kin ci gwafar ubanki" duk zaro ido sukai Dijalle zatai magana sukaji ana sakin gud'a alamar an kawo Maimuna matsawa Ramatu tai tana musu kallo she'ke'ke tace "to yanzu kam zaku iya shiga mayu kawai" tana fad'in haka tai gaba.
Da kallo suka bita cikin takaici Kulu tace "ke Barah baki zauna a gidan nan ba komawa zamuyi ke dama ba sonki take ba amma saboda tsabar rashin sanin ciwon kai kika yarda ki sake zama dashi" tsaki Dijalle tai tana cewa "to gashi kinga alama kuwa a gaban mu ma tana wulakanta ta balle kuma taci gaba da zama da d'anta yadda bata da mutuncin nan har dukan suruka zata iya" 'kanwar kandiya dake kallon yadda jikin Bara'atu yai sanyi tace "to yanzu me kuke so ayi zamu juya da itane"? Caraf Dijalle tace "me zai hana Ilyan wa? zata samu wanda ya fishi amma wallahi yadda uwarsa nan bata da mutunci tasa ya kara aure idan Barah tace zata zauna ma ba'kin ciki ne zai karta kuzo kawai mu tafi" juyawa sukai zasu fita Ramatu dake kallon su tace "as as as a gaida na gaba mayu kawai masu ba'kin ido" babu wanda ya kula ta a cikin su suna fita kofar gidan suka hadu da Ilyah yana shirin shiga da mamaki yace "ya na ganku haka akwai abinda ya faru"? Yai tambayar dan shi ko kad'an bai kula da Bara'atu ba ya dauka tana ciki ko Ramatu tai musu wani abu dan yasan sai ita gani ba 'kyalewa.
Kulu ce tace "to me zamuce Ilyah mahaifiyar kace ta wulakanta mu shiyasa mu kuma zamu juya da Bara'atu dan bazata zauna hawan jini ya kama ta ba tunda har mahaifiyar ka tana maganar cikin 'karya gareta".
"Subahanallahi yaushe wai duk yanzun hakan ta faru? Ai ban sani ba dan Allah kuyi hakuri abinda tai muku muje ciki" Karima 'kanwar kandiya tace "a'a Ilyasu babu cikin da zamu koma gaskiya gida zamu mayarta ba abinda Bara'atu zata d'auka a gidan ka sai wahala da damuwa dan haka kayi hakuri kuzo mu tafi" ganin da gaske tafiya zasuyi yasa a rikice Ilyah yace "dan girman Allah kuyi hakuri kuzo muje ku mayar da ita nayi muku alkawari babu abinda zai sameta bazan bari ba" shiru kowa yai Kulu tace "shikenan amma gaskiya ka kula sosai da gidan ka domin akwai matsala" zan kula karku damu ina son Bara'atu bazan bari a wulakanta taba" sun d'an ji dad'i ganin ya damu da ita ko tanan zataji sauki dan haka suka amince ya musu jagora suka mayar da ita har d'akinta tare da mata fad'a cewa duk wani abu zaisa ta tashin hankali da uwar mijin ta koda kishiyar ta ta kiyaye ta ri'ka kawar dakai akan abinda bai shafe taba tunda tasan Ramatu ba mutunci gareta ba karta shiga harkarta karta bari wani abu ya shiga tsakanin su.
Amma asubar fari gari da duhu ko assalatu ba'ai ba Ramatu ta fito daga d'akin ta tana zuwa kofar d'akin Bara'atu ta soma bukawa da karfi tana cewa "ke tsinanniya bunjinjimar asara fito ai ba barci kika dawo yiba zaki bud'e ko saina karya murfin kofar na shigo da kaina na fito dake na miki dukan tsiya yar fatararru" cikin takaici Bara'atu ta bud'e kofa tana kallon Ramatu dake tsaye zatai magana Ilyah ya fito daga d'akin maimuna cikin rashin jin dad'i yace.
"Wai dan Allah babah me yasa kike haka ne da asubar farin nan me zatai miki kika zo kina buga mata kofa duk makota na jinki".
Kansa ta koma "dambun ubanka zatai min asararre waini Ilyah kodai bankad'add'iyar matar nan asiri tai maka ban sani ba babu dama nayi magana saika mayar min bakaso a fad'i laifinta nuna Bara'atu tai da yatsa amma Allah ya tsinewa uwarki kandiya dan komai silarta ne itace ma'kasudin komai bari gari ya gama wayewa wallahi ko bari su karya cikin dad'in rai bazan ba sainaje na 'kaddamar musu bala'i iri iri dama ai tasan hadina da ita ta iya d'ebo ba'kin ido tazo a gantsara mata abinci taci zakuci gwafar ubanku ne daga ke har tsigalgalar uwar taki".
"Dan Allah babah kiyi shiru wannan fa zubar da girma ne" Ilyah yai maganar ransa a 'bace.
"Kai zanci malafar ubanka idan bakai min shiru ba so'ko'kon banza sakalin asara wanda kare ya lashewa zuciya kayi asara tunda harka za'bi matarka akan ni da nake uwarka".
Had'e rai Ilyah yai "ni bance miki na zabeta akanki ba fad'ar kice kawai daga naga kinyi ba daidai ba nayi magana gaskiya abinda kike bakya kyautawa wannan fa ba neman girma bane".
Caraf Ramatu tace "dama nace maka ina neman girma ne? Karta girmama nin mana taga yadda zanci 'kashin ubanta tasan karon mu da ita ai abin baya mata dad'i" Ilyah bai sake magana ba ya kalli Bara'atu yana cewa "koma d'aki ki kwanta" da sauri Bara'atu ta shige cike da tsoro ta rufo kofa hararar sa Ramatu tai "humm Ilyasu kayi asara wallahi kaji jiki da ina da wani d'an bazan zauna a gidanka ba saidai ka nemi wata uwar badai niba" shikam tari da bai kama shiba bai sake ce mata uffan ba ya juya shima yana komawa d'akin amaryarsa yayin da Ramatu taci gaba da balbali a tsakar gida ita kadai taja kujera ta zauna sai zazzaga fad'a take bakinta har kumba yake ta'ki yin shiru duk ta dami jama'ar anguwa sai Allah wadai suke har akai assalatu aka shiga masallaci bata tashi ba balle tai alwala da sallah saida gari yai haske sannan tayi niyyar yi.
Habu ne zaune yayi tagumi gaban Salamatu dake kwance sharkaf kamar gawa Sabi'u na gefensa sunyi shiru babu mai cewa uffan shigowa d'akin Rakiya tai da sallama cikin sanyin jiki tace "ya jikin nata"? Kai Sabi'u ya d'aga "da sauki Rakiya" zama tai ta wajen 'kafafun Salamatun tana cewa "amma me gida tunda likitoci sunce ba ciwon asibiti bane mezai hana muyi na gargajiya kaga ciwon gaba yake 'kara yi kuma kalli wani abun tsoro yadda jikinta yake 'kai'kashewa kalli yadda fuskarta ta koma kallonta kamar bana mutane ba" ta karasa maganar tana fashewa da kuka.
Kallon Sabi'u Habu yai cike da damuwa yace "yaya Sabi'u gaskiya wannan ciwon na babah ba 'kalau ba abun da tsoro tunda kaji likita yace a dawo gida ayi na gargajiya lallai akwai abun dubawa ga kuma kullum sai anyi mata 'karin ruwa amma yan awanni ace sun tsotse wanne irin abu ne wannan kodai mayu ne"? Numfashi Sabi'u ya sauke tare da girgiza kai ganin yadda bakinta ke kakkarwa ya kalli Habu yana cewa "nima tunanin dake raina kenan saidai bamu tabbatar ba na samu malam Zayyanu jiya akan batun yace yasan wani mutum mai maganin hausa duk abinda ya shige duhu indai anje wurinsa insha Allahu ana samun waraka dama jira nake alhaji Hamidu ya dawo daga saudiyya kud'ina da yake gurinsa ya bani sai mu tafi" gyara zama Habu yai yana cewa "ba matsala yaya Sabi'u indai maganar kud'i ba damuwa mudai lafiyar ta muke bukata bari naje gida na dawo saimu tafi tunda kaga yanzu na iya motar dana sayo ba haya nake bada itaba sai muje" mikewa Sabi'u yai shima yana cewa "to bari naje gurin malam Zayyanun yamin kwatancen garin kafin ka dawo" Rakiya ya kalla "ki jirani a gurinta ina zuwa" to tace yayin da suka fito tare Sabi'u yai gurin da zai sami malam Zayyanu Habu kuma yai gida.
Zaune ya sami Saude da amayarsa A'i dan Binta kam tana gida wanka ganinsa da damuwa yasa Saude cewa "lafiya meya faru naganka haka"? 'Dan tsayawa yai yana kallon Asma'u dake zaune gaban A'i tana mata kitso yace "eh lafiya babah zamu kai gurin magani wani gari yanzu" "subahanallahi sake tashi jikin yai"? Wucewa habu yai zuwa d'akinsa yana cewa "ai dama baya sauka kullum a tashe yake" shiru sukai cike da jimami harya fito Saude tace "bari muje mu gano ta A'i bar kitson nan sai mun dawo" mikewa suka kowa na dauko hijab suka fita motar na waje yace su shiga tunda shine zai jasu shiga sukai duk inda ya gifta da ido ake bin motar masu hassada nayi masu tayashi murna nayi saidai yan ba'kin ciki sunfi yawa a sanda sukaje al'ajabine ya kamasu ganin yadda kumfa ke fita a bakinta sai mummurd'ewa take tana surutai duk zaro ido sukai jiki na rawa musamman A'i da sauri tai baya Dan akwaita da tsoro cicci'bota habu da Sabi'u sukai suna fita da ita wajen motar da'kyar suka tan'kwasata suka sata a cikin kafin suka shiga habu na baarwa Saude sakon yadda zasuyi amfani da kayan abinci kafin suka dau hanya.
Dalah na zaune Balarabe ya shigo da kaya cikin leda a hannunsa ya aje mata ba magana d'agowa tayi a damuwance tana kallon sa kamar hawaye zai zubo mata dan tasan ba kalau ba yanzu gabadaya ya canza ya zama wani iri tace "wannan meye a ciki"? Bai kalleta ba yace ki bud'e ki gani mana ba kina da ido ba"? Bud'ewa Dalah tai ganin kayane yasa tace "na maye"? Kai tsaye Balarabe yace "na fad'ar kishiya ne kin gane aure zanyi Asabe zan aura dan haka duk wani shirginki da kika san yana wancan d'akin ki tattare zan gyara" sauke zazzafan numfashi Dalah tai tana cewa "shikenan Allah yasa haka ne mafificin alkairi" Amin inda gaske kike" ya fad'a yana Mi'kewa zai fita sai kuma ya tsaya tare da cewa "nayi gidan Asabe kada ki dafa abinci dani" kafin Dalah tai magana Indo tace "baba ka taho min da biskin" "da uban biskin zan taho miki dashi tsohuwarki ta baki kud'i kije shagon Habu ki sayo ni bani da kud'i" yana fad'in haka yai waje yabar Dalah tana sharar 'kwalla Innalillahi wa inna ilaihi raji'un tun ba'aje ko'ina ba Balarabe ya fara canzawa ina ga yayi auren kenan.
Tafiyar su habu da kwana biyu Rakiya ta haihu gashi ba waya a tsakani balle ta fad'a sai wata tsohuwa ce daga ma'koftansu take kula da ita da jaririn mutane nata zuwa barka ranar suna itace ta za'ba masa tunda Sabi'un bayanan cikin dabbobin da yake kiwo aka yanka mata raguna biyu Binta ma tazo bikin sunan saboda tayi wata biyu jira take Habu ya dawo daga tafiya ta dawo d'akin ta gashi dama Bashir ya bar gida ya tafi dutse karatu sai lokaci lokaci yake d'an zuwa gida su gaisa yana can yayi gidansa da matarsa harda d'an sa Ahmad.
Suna zaune anata hira irin wacce akeyi idan an had"u a gidan biki Dalah da shigo da atamfar biki a hannunta suna gaisawa ta shiga d'akin Rakiya domin 'kawarta ce sosai tun suna yara sakamakon zafi yasa Dalah ta fito waje tana zama cikin mutane a 'kar'kashin bishiyar badalar dake tsakiyar gidan yafendo ce ta kalleta tana cewa "sannu 'yarnan kinji Allah ya miki tsari da sharrin wannan muguwar mace Asabe da mijinki yake kokarin aura" zaro ido waje Hajjah tai "ke wacce Asaben amma dai ba Asabe ta bayan layin muba matar da tai zaman logus ko lagwas (Lagos) yake na manta sunan garin ai itace zai aura"? Kai yafendo ta d'aga "eh itafa" har 'kwaruwa Hajjah take waje tafa hannu da cewa "Innalillahi amma gaskiya Balarabe baiyi zabin mace ta gari ba na taya ki ba'kin ciki Dalah Allah ya tsare ki daga sharrin ta dan wannan matar kwalba ma haka ta ganta" "aike dai kawai bari dan ko wancan mijin nata ma ba mutuwar Allah yai ba kashe shi tai haka mutane suke cewa dama saboda dukiyar sa ta aure shi* "oh ni kinji irin abun ko? Kuna zamanku lafiya zai yayo muku bala'i ke dashi" ita dai shiru tai kawai tana sauraron su yayin da suke tsinka mata zuciya da maganganunsu amma ya zatai bayan ha'kuri da addu'ar Allah ya tsare ta da tarkon Asaben.
Batun su habu kam sunje gurin me magani mutumin ya matukar 'kwarewa a iya cire aljanu komai taurinsu amma me abun ya bashi mamaki babu aljanu jikin Salamatu kuma ba mayu bane yayi iya bakin kokarin sa amma baiga komai ba dan haka shawara ya basu cewa kawai saidai ai mata sauka ko Allah zaisa a dace damuwa da tashin hankali baisa sun iya ce masa 'kala ba sai shine ya fahimci suna wani hali na d'imuwa ya taimaka musu amma dai labarin yana nan yadda yake babu sauki ko sasssuci a jikin Salamatu sunfi wata yana abu d'aya karshe yace sunyi hakuri su koma gida su sake jarrabawa zuwa gurin wani