Showing 66001 words to 69000 words out of 130249 words

Chapter 23 - ME KAMAR SARKI

  

04 Oct 2024

17611

na kara ki gidan kitson nan Allah yasa Suwaiban bata aiki yanzun nan tayo miki na dawo gida na d'ora abinci kar dare yayi maza tashi ki dauko min" mi'kewa Indo tai tana daukowa rufe d'akunan Dalah tai tana sa hijab din suka fita.

Asabe na fita daga gidan Balarabe tayi anguwar babbar 'kawarta Markah hankalin ta a tashe tana zuwa ta yada gyale da jaka ta soma zaga tsakar gida tana jan tsaki da maganganu ita kad'ai Markah na gefe tana yanka loma ganin yadda Asaben ke zarya tace "a'a 'kawar arziki na ta'ba ki da alkairi wannan abinda kike nasan bakya cikin nutsuwar ki akwai wani wanda ya 'bata miki rai wa kike zagi"?.

Zama Asabe tai tana sake jan dogon tsaki cikin takaici kamar zata fashe da kukan ba'kin ciki idonta fal da ruwa tace "wannan mara mutuncin ne ya tozarta ni dan kawai naje gidansa harda cewa uban me ya kawo ni".

Cikin alamar tambaya tace "wa kenan akan me kike magana ne"?.

Cizon yatsa Asabe tai tana zama tace "waye kuwa Markah bayan masifaffan nan Balarabe kalar jaraba wai kawai dan naje gidan sa bakiji wulakanci ba kamar wacce naje maula".

Dariya Markah tai tana cewa "kema dai Asabe kina da shishshigi kinsan waye Balarabe meyasa zakije masa gida"? "Humm Markah kenan sonshi fa nake da gaske so nake na aureshi banajin dad'i idan ban ganshi ba" baki Markah ta ta'be "tab aiko kin hada kanki da wahala Asabe maganar gaskiya Balarabe bazai ta'ba sonki ba balle ya aureki gara ki ha'kura" zaro ido Asabe tai "kinsan me kike cewa kuwa na ha'kura fa kikace Markah"? Kai Markah ta d'aga "eh shine mafita kema kya hutar da zuciyarki daga 'kuncin da kika jefata" mi'kewa Asabe tai tana daukar gyale tace "inaa bazai yuwu ba Markah ya yau d'in nan zanje gurin boka na" zaro ido Markah tai "haba Asabe a yau kuma"? Kaita d'aga "eh yanzu ma kuwa kinga tashi ki raka ni" kallonta Markah tai kafin ta she'ke da dariya harda tafa hannu da sakin gud'a cikin zolaya da sha'kiyanci tace "sai kinyi hajiya Asabansi amarya a gidan malam Balarabensi mai kayan gwanjo in Allah ya yarda" hade rai Asabe tai tana cewa "kinga idan zaki rakani kawai ki taso muje wallahi indai kika taimake ni na cika burina zan baki kud'i naira dubu hamsin kyauta kiyi jari ki bud'e kasuwanci a gidanki" dafa 'kirji Markah tai "da gaske kike 'kawar arziki? Aiko yanzun nan makuwa zamuje tab irin wannan samun gara'basa da ganima haka ahh muje akwai gurin wani ri'kekken boka a cikin wani ba'kin daji sunansa 'kadaga aikinsa me kyau ne yanka daya ne saidai akwai kashe kud'i da tsada" jin haka yasa cikin azama Asabe tace "indai aikina akan Balarabe zaici ko maye zan bayar ko meye zan 'batar dashi naga na samu kansa ya soni ya aureni" "shikenan 'kawar muje" Markah ta fad'a tana dauko gyale suka fita tana sake fad'awa Asabe shaharar bokan da irin aikin da yake farin ciki kuwa tuni ya cika Asabe hango Balarabe kawai take a tafin hannunta tana jujjuya shi kamar yadda ranta yake so.


๐Ÿค—AYI HAKURI YAU TYPING ๐Ÿ“ฒ DIN BABU YAWA KUMA BANI DA CHAJI๐Ÿ“ฑ GASHI SABODA INA MATUKAR 'KAUNARKU A GIDAN BIKI NAYI MUKU TYPING๐Ÿ‡๐Ÿ˜˜๐Ÿคฃ.


MRS AL'AMEEN AHMAD CE ๐Ÿ˜˜
Yusrah Musa Abubakar maman little Zaran aunty ๐Ÿ˜‚๐Ÿคฃ๐Ÿค—๐ŸŒนโœŒ๏ธ.


๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน
๐ŸŒDuniyar da za'a barta
Me ya kawo had'ama?๐Ÿคจ
๐Ÿ™๏ธRayuwar da zata 'kare
Ina wani farin ciki?๐Ÿ˜ง
Ana sauraron mutuwa๐Ÿ˜ข
Ina wata walwala?
Jikin da zai zama gawa ๐Ÿ˜”
Me zaisa alfahari?
'Karshen da makomar sa kabari ๐Ÿ˜ญ
Me zai jawo girman kai?
Duk wanda ya manta da wannan ๐Ÿ˜Ÿ
To ina yabar hankalin sa?๐Ÿค”.


๐ŸŒน๐Ÿ’žMU'KAMIN KA DA GIRMA YAKE ME KA'ABU DA ZAHIDU KA TAKA DAI DAI UBAN GIDANA YA RASULULLAH๐Ÿ’–๐Ÿ’.
A baitin farko sunanka ne ya Al Aliyu ina tawassuli ga annabin nan almakiyu sirrin wadatuwa wanda ya zamma madaniyu albarkacinsa nazo kai mini ya 'kawiyyu ka 'kara bani dama in wa'ke nuru zatullah.๐Ÿ’ž๐Ÿ’˜
Summas salatullahi alam daharujjanani mai kausara da zam zam ya sahibul bayani mai kyau da kyan gani ya sirrin samun sukuni wadatuwar wadata kaine ayyunul ya'kini lale wa marhaba bika ya kairu kal'ki indallah.โค๏ธ๐Ÿ’
Ranar kowa yana kasa kai kuwa kana buraka mala'ku rundunar Allah na bayanka suna ta gaisuwa da sallamar su a gareka ranar dukkan annabawa ne fadawan ka ashe kwa zamu sha kallo matsayin rasulullah,๐Ÿฅ€๐ŸŒน๐Ÿฅ€
Niko nace ka taka daidai abban kasim ina isar waninka a yau ya jikan hahim aljannah taka ce makiya ba uhm ba um um ashe kwa zasu sha narko tunda sun 'ki sallallah๐Ÿ’•๐Ÿ’š.

TYPING ๐Ÿ“ฒ {Sat 20Apr 24 02:18PM}%๐ŸŒน๐Ÿ‘‰ YUSRAH MUSA ABUBAKAR.


๐Ÿ‘‘ME KAMAR SARKI ๐Ÿ‘‘

WHATSAPP NO:234 905 527 3614.

Story and written
โœ๏ธMrs Al'ameen Ahmad ce maman little Zaran aunty ๐Ÿ’….

Wannan page din naka ne d'an uwa rabin jiki ha'ki'ka kai jarumi ne a cikin jarumai jarumtacce a cikin jarumtattu u're the champion ๐Ÿ‹๏ธ๐Ÿ’ช best hero in the world ๐ŸŒน d'an uwa na Allah ya tsare mana kai ya tsare ka daga sharrin miyagun makiya annabi na wannan daji Sambisa๐Ÿ˜ฃ๐Ÿ˜ฅ Allah ya dawo mana dakai gida lafiya cikin aminci alfarmar Manzon Allah saw Amin ๐Ÿคฒ๐Ÿ‘.
CPT. SALISU ABDULLAHI (*()*) KOLI๐ŸŸ ME TAMBARIN NO GOING BACK๐Ÿ‘ฎ๐Ÿ’ช๐Ÿ”ซ๐Ÿ”ซ๐Ÿค›๐Ÿ‘Š๐Ÿ’ฃ.


YUSRAH MUSA ABUBAKAR MRS AL'AMEEN AHMAD CE MAMAN LITTLE ZARAN AUNTY ๐Ÿ’ƒ.

YUSRAHMUSA65@GMAIL.COM INA MASOYA 'YAN UWANA MA MAKARANTA (READER'S)๐Ÿ“š INA MATUKAR FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA GA WATA BABBAR DAMA TA SAMU YAR UWA KO DAN UWA MAKARANCI KANA NEMAN LITTAFI SABABBI KO TSOFAFFI NA TARIHI KO NA YA'KE YA'KE WANNE A CIKI KAKE DA BUKATA? HUMM MAZA KA MATSO KUSA GA BABBAR DAMA TA SAMU TASKAR HAUSA EBOOKS TA SAMAR MUKU SABUWAR DUNIYA WATO SHAFIN SU NA MR HAUSA EBOOKS KUMA KODA LITTAFI KA RUBUTA KANA SON YA'DAWA ZASU DORA MAKA SHI SHAFIN SU NA GOOGLE TWITTER FACEBOOK DA TELEGRAM KAI HARDA INSTAGRAM KAWAI YAN UWA KU DANNA WANNAN LINK 'DIN.
Taskar Mr Hausa Ebooks
http://tnovels.com.ng/novels/ sai kuyi serch kuna kasa sunan littafin da kake so kai tsaye zaka shiga shafin sai kayi downloading duk littafin da kake so๐Ÿค—.


#VOTE
#SHARE
#COMMENTS
#FALLOW

31~AL-KHABIR
The all Aware
33~AL-HALIM
The Forbearing.

16~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Nadiminah.

Bintu Musa jikar Abubakar Muhammad.

๐ŸŒ„ INFANT ND PRETENDING ๐ŸŒ„
Episode 31&32
Har dare ya fara nisa wajen karfe sha daya babu likitan daya fito balle su samu wani d'an labari dazai sanyaya musu rai a gajiye Sabi'u ya kalli Habu dayai tagumi yana cewa "Habubakar ya Kamata kaje gida dare kada yai nisa ga Rakiya ku tafi tare" kallonsa Habu yai tare da girgiza kai yace "yaya Sabi'u bazan iya tafiya na barka ba cikin kad'aitaka ga damuwa bayan babu likitan daya fito balle muji abinda ya sameta bazan iya zuwa ko'ina ba anan zan kwana" dafa shi Sabi'u yai yana cewa "a'a Habubakar na sani kayi matukar damuwa da hakan amma zan baka hakurin dan Allah ka tafi gida ka dawo da safe kaji"? Shiru Habu yai tare da sunkuyar da kansa kamar me tunani zuwa wani ya d'ago zaiyi magana Sabi'u ya dakatar dashi "a'a dan Allah kar kace komai ka tashi ku tafi" mikewa habu yai batare daya sake cewa 'kala daidai Rakiya ma ta tashi tana d'iban kwanuka Sabi'u ya d'ora da cewa "yauwa habu gobe da safe kaje gidan malam Zayyanu kace wannan kud'in dana bashi ya baka na fasa sayan gonar baba ce bata da lafiya zan biya kud'ad'en asibiti" kai Habu ya d'aga "to zan fad'a masa saida safe" Allah ya tashe mu lafiya" har wajen asibitin ya rakosu yana sake jaddadawa Rakiya tazo da wuri.

Ramatu na zaune da safe a kofar d'aki Ilyah ya shigo da sauri sai ganinsa tai a kanta kamar an jefoshi har haki yake binsa tai da kallon mamaki tana cewa "kai makau lafiya meye hakan zaka shigo min a wani hargitse kamar sabon kamu meya faru"? Kasa zama Ilyah yai sai kaiwa da komowa yake harda gumi yace "yanzu naji labari wai babah Salamatu bata da lafiya an kai ta asibiti" tsaki Ramatu tai tana zafga masa harara tace "au Salamatu bata da lafiya shine na wannan shigowar a gigice kana dawurwuri kamar me neman wani abu saime dan tana jinya asirin tane ya fara tonuwa irin 'kulle 'kulle da makirce makircen da take ne ya fara dawowa kanta kaga yanzu kowa zaisan ita ba mutuniyar arziki bace sungungumar asarace" "kai dan Allah wai me kikeyi haka"? Gyara zama Ramatu tai "ubanka nakeyi haka asararran banza asararran wofi wanda ya rako maza meye hadinka da Salamatu ne dan malafar ubanka fad'a min naji idan ta fini martaba sai nasan matsayin daka ajiye ni tunda dama ka fara nuna matarka ta fini mu'kami inaga nan gaba zakace banice na haifeka ba" jin abinda Ramatu tace Ilyah yasan fitina kawai take nema saboda kwana biyu babu Bara'atu da take saukewa damin bala'i shiyasa zata koma kansa amma bari ya bita a sannu zama yai kusa da ita yana cewa "kiyi hakuri nifa ba haka nake nufi ba gani nai ya cancanta a dubata tund.. .......,........

Katse shi Ramatu tai da cewa "a gurin kaba sakarai ni a gurina bai cancanta ba bani da had'i da ita" mikewa Ilyah yai takaici ya gama cika shi domin ta gama 'kureshi amma bai nuna mata ba yace "Ki tashi muje dan Allah ki dubota" wani kallo Ramatu tayi masa tana cewa "uban waye zaije dubo Salamatun amma dai bani Ramatun ba wai Ilyah meke damunka ne ka fara haukacewa kome ka manta ita muguntar da tai maka kazo saika wuni a rana tun daga safe zuwa dare biyar bata bata shigo maka ba wallahi Babu inda zanje na dubata Allah yasa ma ta mutu"๐Ÿ˜ฒ shiru Ilyah yai yana kallon ta ya kasa magana tsaki tayi "meye ne ka wani tsaye tserere a akai na kamar bishiya ko bakiji yaren da nai maka magana dashi bane? nace bazanje asibitin ba kuma kaima in kaje ban yafe maka ba" zaro ido yai cikin mamaki yana kallon ta zaiyi magana sukaji sallama duk kallon gurin sukai Habu ne ya shigo yana durkusawa a gaban Ramatu yace "babah ina kwana"? Baki da ido Ramatu ta bud'e tana kallon sa tace "tofa jama'a yau za'ai ruwa da 'kan'kara a garin nan Habubakar yaushe rabon duniya da ayyaraye kaine a gaba na kake gaida ni ko kuma mafarki nake"?.

'Dagowa Habu yai cike da mamaki yana kallon ta abinda kullum sai yazo ya gaida ita wata rana harda aje mata kud'in goro yake amma zata ce yaushe rabon duniya da ayyaraye tab lallai Ramatu ta fara gigin tsufa kawai yabar abun a matsayin haka katse masa tunani tai "Habubakar dakai fa nake ko kaima kazo ne ka fad'a min Salamatu na asibiti" kai ya girgiza yana cewa "a'a nazo ne na fad'a miki an samu 'karuwa a gidana yau da asuba Allah ya sauki Binta lafiya mun samu namiji kuma ranar sunan za'a d'aura min aure da A'i" zaro ido Ramatu tai har batasan lokacin da tace "Binta ta haihu namiji na shiga uku na lalace wannan wanne irin bala'i ne da masifa kaji fa Ilyah sai haihuwa suke tayi amma kai ka ma'kalewa waccan mayyar tsinanniyar bunjinjimar matar taka wacce batasan komai ba saici kamar jaka tazo a 'kai'kashe ta samu arziki ta bararraje yanzu gashi ta zama kamar alade ko'ina bulbul ba rama ai wallahi tallahi Ilyah a satin nan saika auri Maimuna na gaji ace har yanzu baka da d'a ko daya Sabi'u 'ya'yansa uku ga Habun ma daka girmeshi gashi shima yayi biyu ehe uban me ka tsaya kallo" ran Ilyah a 'bace yace "to haihuwa ai ba ita bace kuma ba'a girma ko 'kan'kanta bane ina ga makocinmu nan malam na gabas ya tsufa tukuf amma baida d'a ko daya kuma ga d'an uwanki Hashimu inace shima bai ta'ba haihuwa ba saini zaki takurawa".

A masife Ramatu tace "dan gwafar ubanka ni kake cewa ina takura maka saboda bankad'a ta same ka"? Shiru yai yana kallon wani gun daban ganin bai tanka ba tacigaba "kasan Allah wallahi a satin nan saika auri Maimuna babu fashi kaji dai ko na fad'a maka garama ka sani" Ilyah bai sake magana ba yasa kai ya fita a gidan tsaki Ramatu tai tana bin kofar da harara mi'kewa Habu yai ransa babu dad'i da yasan abinda zaizo ya tarar kenan ba baizo ba kallon Ramatu yai yana cewa "shikenan zan tafi sai anjima ni zan koma" binsa da kallo Ramatu tai tana cewa "to ka gaida mejegon Allah ya raya" Amin Habu yace yana fita cizon yatsa Ramatu tai tana mi'kewa ta dauko gyalenta tana yin hanyar fita sai magana take ita kad'ai "wallahi Ilyah baka isa ba hauka ma kenan haka kawai kana zaune kara zube ba tsuntsu ba tarko aradu a kwana bakwai dinan saika yi aure kaga hauka.


Bara'atu na kwance a kofar d'akinsu kandiya tana gefenta ta ji'ka magani sai yi take da bakin ta akan ta tashi tasha ta'ki saboda batasan magani kallonta ta kumayi "wai bara meke damunki ne? dama kina da ciki baki fad'a ba amma meyasa kikai shiru Ilyan ya sani ne? Kai Bara'atu ta girgiza "a'a bai sani nima kaina bansan dashi ba badan kin fad'a ba" zaro ido kandiya tai tana cewa "ah lallai kam sannunki da rashin hankali wato cikin na jikin ki kice bakisan dashi ba nifa abin fitina ne banaso Dan ina tsoron jarabar Ramatu kar tace bata yarda ba bazasu kar'ba ba ya kamata kisan yadda zaku had'u dashi ki fad'a masa gara yasan kina da ciki kinji ko".

Kai ta d'aga "to zan fad'a masa saiyazo" zaro ido kandiya tai "sai yazo kuma? Anya bara kinsan me kike cewa kuwa yanzu zuba ido zaki sai ranar da Ramatu ta barshi yazo inda kike, tabdijan to bari kiji sanki 'kanin kafarki idan kina neman zaman lafiya ki tashi kije ki nemeshi ki fad'a masa inta kama kije har gidan" tashi zaune Bara'atu tai tana kallon kandiya tace "zanje amma yanzu bana jin dad'i saina ji sauki" dauko maganin kandiya tai"shikenan kar'ba kisha" kar'ba tai tasha sannan ta aje kofin tare da komawa ta kwanta.


Kwana biyu likitoci suna aiki akan Salamatu amma shiru sai uban ma'kudan kud'i ta ake ci daga ase wannan sai ase wancan gabadaya Sabi'u da habu sun gigice ciwon nata ba sauki sai gaba yake yau idan anyi gwaji ance ciwo kaza ne gobe wani dabam za'a gani hatta likitocin mamaki suke ba'a ta'ba kawo musu patient irin wannan ba.

Asabe na zaune ta zuba tagumi tai shiru sallama Markah tai amma shiru bata amsa ba mamaki ya kama Markah saida tazo saitin kunnenta ta sake rafka mata sallama a firgice Asabe ta d'ago ganin Markah yasa ta sauke ajiyar zuciya batare da tace komai ba sai kallon bahon dake gaban ta tai waken 'kosai ne data sayo ta zuba masa ruwa harya kumbura ya tsotse tana tunani bata sani ba tsaki tai tana sa 'kafa ta ture bahon tana huci zama Markah tai tana sake karantar yanayin Asaben tace "ya akai ne kawata naga kin zauna shiru ko har yanzu maganin bai ciba Balaraben baizo ba ne"?.

Kai Asabe ta d'aga tana cewa "ina yazo kuwa dama yanzu gurin ki nake shirin zuwa Markah na gaji har yau ba wani labari gaskiya muje ki kara rakani gurin bokan nan kila ma baiyi aikin ba kawai kud'i na ya cimin wallahi bazan ta'ba yarda ba saiya biyani tashi muje" katseta Markah tai "a'a Asabe dan Allah ki saurara kiji na tabbata bazai cinye miki kud'i ba 'kadaga aikinsa mai kyau ne" mikewa Asabe tai "a'a nifa banason dad'in baki kawai in zakije ki tashi muje" markah zatai magana yaro yai sallama yana cewa "wai inji wani mutumi wai yana sallama da Asabe" da sauri asabe tace "wani kuma ya sunansa"? "Nima ban sani ba amma yace Balah" da mamaki Asabe tace "Balah kuma wanne balan kenan? Shikenan dai jeka kace ina zuwa" fita yaron yai daidai Asabe ta dauki gyale tace "ni waye Balah a garin nan Markah"? Kai Markah ta girgiza "nima ban sani ba Balah dai daya ne baban Tanko kuma ya mutu saboda ba'kin cikin abin da d'an sa ya aikata bayansa bansan wani ba amma kije ki gano ko Balarabe ne" zaro ido Asabe tai "Balarabe kuma anya? Gaskiya da kamar wuya" "to kije ki gano man ina jiran ki" shikenan bari na dawo Asabe ta fad'a tana fita kamar a mafarki ta ganshi tsaye a jikin bishiyar kofar gidan tabbas Balarabe ne amma anya ita yake nema amma bari ta jarraba 'karasawa tai tana masa sallama ga mamakin ta sai taga ya washe baki yana amsawa "am kaine kake nema na"? "Eh nine fa Asabe kinji mamaki ko kiyi hakuri dan Allah abinda ya faru ranar da kikaje gidana nazo ne muyi magana" numfashi Asabe ta sauke tare da sakin murmushi abun yazo kwarai aiki yaci kallon tai tana cewa "to ina jinka Allah yasa lafiya ina d'iyata Indo"? Da sauri ya amsa "d'iyar ki tana gida lafiya da'kyar ma ta barni na fito sai rigima take wai sai ta biyoni" kai Asabe ta jinjina a ranta tace "humm da dukkan alamu akwai sha'kuwa da so mai karfi tsakanin ka da 'yarka kuma saina rabata.

Abu fa yayi nisa tun Markah tana zaune har ta gaji ta fara gyangyad'i a kan kujera karshe ta kwanta ta kama barci ta dauka abun na wasane taga har ta tashi a barci Asabe shiru to kodai tayi wani wurin ta barta ne tashi tai tana le'ka kofar gida hangosu tai suna tsaye suna hira 'kara murtsuke ido tai ganin da gaske Balarabe ne yasa ta koma tana dariya tace "kai Masha Allah kawar burin ki ya cika saura nawa azo aban alkawarin dubu hamsin cascas nima naje na shana wallahi yau kaza ce abincin darena" tana rufe baki Asabe ta shigo bakinta kamar zai 'bare tana jefar da gyale ya yarfa gud'a tare da tafi tai tsalle ta dire tana rawa tace "ke Markah albishirinki wallahi da gaske Balarabe ne yazo kinsan abun mamaki yadda ya sake yana zuba min zance harda ban hakurin wulakancin da yai min a gidan sa kinsan yana jana da zance karshe sai cewa yai yana sona dan Allah na amince ya aureni kinji

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login