Showing 183001 words to 183750 words out of 183750 words
su laifi daya suke aikatawa.
Shi yasa kome suka yi nake bin diddingin suke yi.
----
Alhamdulillah wannan karon da kaina na haihu, inda na haifi da namiji, me kama dani, tunda Uncle Yayi min wayo, duk masu kama da shi nake juye mishi.
A can gida Gombe anyi suna a gurin mu kuma walima ya shirya mana.
....... Bayan shekara biyu abinda nake burin zama, ya tabbata cikakkiyar Lauyan me kare hakkin mata, kamar yadda nayi fatan na zama me cikakken nasara, da taimakawan mijina na zama jarumar mace, na kuma samu nasarar daukaka kimata Sosai.
Dan ko da muka dawo, Mommy nacan na fama da azabar duniya, watan mu goma da dawowa Allah ya amshin rayuwar Hajiya, mace me addini da sanin ya kamata, nafi kowa kuka.
Yarana ban tsannanta musu ba, shi yasa kome ya faru zasu zo su gaya min Ummi kaza Ummi kaza.
Duk wanda yake aikata sharri Allah ya mai da mishi abin shi, naje har Yola nayiwa Ammin Amrah godiya, sannan nace yanzun bana ganin Umma Zuljah, ta mika min godiyatabda Fatah Alkhairi.
Mijina jarumi ne, wanda ya haɗa hakuri da sanin darajata, wata asabar mun je Super market, muka hadu da wata mata, tana bin yaran da kallo.
Daga baya na Uncle ƴace.
"Dr Mayah Malik! Ga mata na, Brrst Yumnah Omar Ahmad da yaran mu, Faruq wancan, A'isha da Fatimah, Abubakar Sadeeq, shine karamin yaron mu."
Tayi farin ciki sosai, sannan ta gabatar da yarta mai suna Seerat sai karamin da tasanya mishi sunan Uncle, Shima Halwani.
Bayan mun musayan Number ne, muka dawo gida.
----
Ina kwance a jikin shi, tare da rike hannun juna yace min.
"Saura me ya rage baki cimma ba?!"
"Babu komai! Kawai ka yafewa Mommy da Linah abinda suka mana shine abinda rage min."
"Toh Na yafe musu shikenan!"
" Ba shikenan bane baka ga yadda Allah ya mai dasu bane, wallahi nashi yafi su daraja, masu kula su, dan babu yadda zasu yi dasune amma da sun gudu, shi yasa nake biyan kudi a cigaba da kula min da Mommy, toh da ta koma sai Allah, wannan ai damuwa ce, da kanka ka kirkiro abinda zai kashe ka da ranka, gashi fatar mutuwa take amma taki zuwa."
.... "Eh ai gwara ta rayu amma cikin ukubar rayuwa,"
"Kai Uncle! Mamata ce fa!"
"Toh ita Mamie baki ga bana jin kome dan ciwon sugarta na cinyeta, da a lokacin da nake bukatar ta, ta bani kulawa wallahi da haka bai faru ba.
Nono ta hanani, abinda yasa ma nake tausayin ta sabida dawainiyyar ciki da kuma Haihuwa, kinsan darajar nonon uwa ai, tunda kin shayar, me yasa idan kina Shayarwa mai damunki da akula min da Yarana.
. Sabida na rasa nonon uwa, dan haka Malama bar wadancan matan abinda suka shuka suka gurba dai-daiwa dai-da."
"Toh Allah yasa muyi kyakyawan karshe, rayuwar babu wata ma'ana da fa'ida, babu amfanin kayi abinda zai zame maka fitina a rayuwar ka, daga ni har kai mun ji jiki, da iyayen mu mata, Allah sarki Abbanah kashe shi tayi.
Ko da hakkin shi ma ya ishe Mommy ganin Bala'i a rayuwarta. Gashi dai duniyar ta samu ya tafi a banza, ta tara ya watse bata ci ba, ya lalace. Ni da taso lalatawa gashi nice a rayen tare da zuri'ata.
Ya Allah! make the Best of my life. The Last part.
And make my best deed last deed
And My best day in which I mean"
"Amin Ya Allah,Amin Yumnah! Matar Tsoho da furfura."
"Da gaske ka tsufa, toh bari naji Super J Dinka ko bazata yi aiki bane"
Dariya muka yi baki, daya.
Rayuwa ba sauki, amma idan ka nemi sauki Ubangiji yana da sauki sosai.
Salim dangin mahaifin shi na kawo shi, ganin mu ba laifi.
Tako ina kome yayi daidai rayuwa baki dayanta hakuri ce.....
Alhamdulillah Nagode sosai a nan na kawo karshen Labarin Yumnah da Halwani...
Na fara rubutawa ranar 23/ July 2020/
Na gama 29/August/ 2020! Banda matsalolin da suka shigo da tuni na dire alkalamin.......
Allah ya had'a mu a karashin Kwarkwarah, Insha Allah...
Nagode sosai Mommys and Auntie's, na gode da bani kwarin gwiwa sosai, Ni kaina nasan bazan iya tafiya babu kune nagode 🤝 sosai Gaisuwa gareku Manyan MATA 😍🌹
Ku tanadi tissue da hanky..... Domin alkalamin kaddarar Jannart.....zai iya girgiza zukatan masoyanta....
#Mai_Dambujeeeee