Showing 171001 words to 174000 words out of 183750 words
shiga d'akina na saka key tare da barin shi jikin kofar.
Hmm. A cikin kwana biyu na hada mishi zafin kai, zai shigo ina shirya yaran da zaran yayi min magana, zan tashi na bar mishi yaran shi, na kama wani aikin na daban, idan kuma girki nake ya shigo zan bar girkin.
Tunda ya fahimci, fushi sosai nayi sai ya daina takura min da bani hakuri ya kuma shiga tayani wasu abubuwan, tsakanin shi da matar shi kawai ya lek'ata ya fito.
Ina zaune na saka Alqur'ani a gaba ina kuka, ya shigo ya zauna tare da yiwa yaran shi wasa, a hankali Yasaka hannu ya amshi Alqur'anin ya rufe.
Sauke numfashi yayi sannan ya fara magana.
"Nasan nan kyauta ba! Amma ina ganin cewa tunda nine babba ya kamata na samu mutuntawa ki ya-ya ne.
Nasan ban kyauta ba, amma bai dace a gaya min magana kai tsaye haka ba, yin amfani da damar da Allah ya baki ai cutarwa ce. Naji nayi Kuskure shi kenan"
Wato hakuri ne bazai bada ba, amma ya amshi laifin shi, murmushin takaici nayi sannan na mike tare da isa bakin kofar.
"Don Allah! Zoka fitar min a daki, idan kuma kaki Wallahi zan bar gidan."
Yana tashi mik'ewa ya haɗa da yaran shi zai fita, kauda kaina nayi sannan nace mishi.
"Idan ka fita dasu Wallahi bazan kuma basu nono ba! In kuma kana ganin karya nake maka shi kenan"
"Ke wacece da zaki saka min doka? Nazo nayi magana tare da amsar laifina, shine zaki wulakanta ni? Ke har kin isa gaya min magana son ranki."
Rike k'uguna nayi, cikin fitsara, zan bude baki naji Linah ta bude kofar ta, sabida karar muryan shi, sake hannuna nayi. Kasa kasa nace.
"Ni budurwan da ka samu cike tam, da yan matanc...."
Kifa min mari yayi bayan ya gyarawa, Anuam zama.
Rufe kofar nayi tare da saka key.
Na dauka na wurga a bayan mirror dina, na koma bakin gadon na zauna, na shiga gaya mishi maganar da tayi min, tare da tuna mishi abubuwan da yayi min.
Idanuna sun rufe sosai, na gaya mishi Magana, da kuma nuna mishi hanyar da ya bullo yake bukatar mu zuba toh bismillah, ranar daga nie har shi babu wanda ya saka wani abu a cikin shi.
Dakyar ya ciro, key din ya fita.
Ga baki daya ya koma jikin matar shi, ina fahimtar zasu mai dani jakar su na daina girki, sai iya cikina, dake bata da kunya na gama girki na kashe gas, naji Anum tana kuka na fita dubata kawai matar nan tazo ta juye. Zata haura Ni kuma na zo zan dauki abincina.
Na ganta dashi da gudu, na haura tare da kamo gashin kanta, wanda tayi kari dashi, wallahi ina cike da yar iska, kawai na sauko wurgota kasa, tare da kwashe abincin na watsa mata a fuskarta.
"Bari kiji ko shi ba tsoron shi nake ji ba, dan Ubanki Fuck You!"
Na labta mata kafana a cikinta, dama na gama kai makura a hakurina.
Ihun da tayi tare da sake ajiyar zuciya, ya sani wurga mata filet din na koma d'akina.
Baya gidan, yana can gurin Hajiya ya kai mata kara na, ita kuma tace karya ne sune suka min abu na rama, ya dawo da haushin kin sauraron shi da tayi, yazo ya samu matar shi kwance a sume.
Shine ya dauketa suka je asibiti, har dare ban ji duriyar su ba, haka na shige nayi kwanciya ta, da asubar fari, naji yana buga kofar tare da yi kamar zai b'alla kofar.
Buɗe mishi nayi yana shiga ya rike wuyana, yana gaya min magana, ture hannun shi nayi cikin kuka nace.
"Eh na dake ta! Kuma wallahi ta kuma min Iskanci har asibitin zan bita na kuma lilisata."
Zare belt din shi yayi yana nadewa.
" Wallahi Ahmad ka Kuskura ka sanya shi a jikina, sai na kasheta!"
.yadda nayi maganar babu tsoro ya sa shi ja da Baya, musamman da idanuna suka yi wani irin juyewa cikin tsawa nace.
"Dake ni ka gani! Wallahi bazata kuma numfashi ba,, na rantse maka, kana d'aga hannunka a kaina. Sai dai wata ba ita ba.
Na rantse ka gwada ni ka gani, ba dai gidanka bane. Zan fita bar maka, kaji abinda na kasa baka."
Ina gama fadar haka na juya Closet dina, na fara kwashe kayan mu.
Kuma wallahi ba komai bane kawai makircinta ne. Shi ya haura tare da zama, ni kuma koda nayi mishi bayani ba fahimta zai yi ba, dan duka kan nayi mata ta suma.
Amma shirya wannan aikin Ba kowa bane sai Mamie....
Kuyi hakuri Nagode 🤝 sosai jiki alhamdulillah Nagode
#Mai_Dambujeee
Na kasa fahimtar halin Mahaifiyarshi da matar shi, hala so yake nayi ta korototo a gari, kawai sai na saka musu ido,
Suka cigaba da min Iskanci, idan ma gadama, sai na wuni a d'akina sai dare na fito.
Haka zan gansu, suna abinda ransu yayi musu, amma bana tab'a ganin cewa zai b'ata min rai bawai dan bana jin zafin bane kawai ajiye su nayi a gefe.
Muna cikin wannan yanayin, ya shirya zuwa kasar Afrika ta Kudu, asalin tafiyar dani ce, amma ganin naki kula shi, shine ya maida martani akan tafiya da matar shi, wallahi ban ji kome ba,
Haka suka tafi, ina zaune zaman shiru ya ishe ni. Wato a duniya Allah ya tsara kome nashi a bayyane yake.
Idan na duba sai naga ga kudin nan da kome ya bar min, amma abin takaici, babu wani farin ciki a raina. Sannan idan na kuma dubawa kome yana min cikin jin dadi matsalar uwar shi da matar shine ya hanani sukuni.
Tafiyar su da kwana biyu, Mamie tazo, tayi min tijara, da ta ishe ni da mita na shiga daki na rufe kofar abuna,
Haka na zauna nayi ta jin ciwon abinda ya gaya min, amma ban tab'a jin a raina na rama ba.
..... Buɗe Whatsp nayi a hankali sako suka fara shigo min, naga sakon shi, kamar bazan bude ba na buɗe.
Hotunar shi ne da matar shi, wasu ma kusan babu wani abu arziki a jikin su.
Abin ya bani haushi, dan haka na kirashi tmyaji dauka, sai nayi blocking mutanen da suke viem din Whatsp dina na daura shi a Status Dina.
Sannan nace.
"Don wacce ta shirya yin Wuf da Mijina ga dama ya same ki, ki dauki number shi."
Ina gama haka na kashe wayar abuna, ashe yayi ta niman kamar zai yi hauka dan hotunar da ta turo min duk na daura a kai.
Sai da Rahbeel yazo kawai ya same ni da maganar banza nace mishi.
"Malam dakata min! Abinda ake min kaji ma tab'a kawo karan dan uwanka, dake a gantale kuka same ni Bari ya turo ka kayi min maganar banzar.
..... Ya duba wayar shi, nima shi ya turo min, tunda yana son na daura ai shikenan, inda baya so maybe da bai turo min ba."
Ina gama fada mishi haka na wuce kitchen, Ina Jin Yana waya dashi. Karshe dai gaya mishi cewa.. ai yana zargin matar shi ce ta turo dan ta bani haushi, Ni kuma nayi musu ma mahaukata na daura a Status.
Dan haka ya binciki matar shi, aikuwa yana dubawa yagani, ko ya ta manta ta goge ne oho.
Aikuwa da suka fara Bala'i babu shiri ya suka dawo.
......ranar juma'a ina kallon wani korea film, Naga an shigo musu da kaya, cigaba nayi da kallona Anuam tana kan ruwan cikina, Anum tana cikin abin kwanciyar ta.
Sau daya da na kalleta, na kauda kaina tare da cigaba da cin pop corn Dina,.ya shigo fuskar nan a murtuke. Ko kallon inda yake ban yi ba, dariya suka bani amma na matsa, sai da suka fara haurawa step, akayi wani abin dariya na kwashe da mugun dariya, har da hanysilowa a a kujera, sam na manta da Anuam,
Kawai yarinyar ta fado badan na kai hannuna ba da tashi kasa.
Sake baki suka yi, Ni kuwa na cigaba da dariya na.
.bayan sun haura nace.
"Baku ga kome ba, zamu gauraya da juna."
...... Da dare ina cikin sakawa yarana kayan kwanciyar su ya shigo. Kallona yayi tare da zama.
Ban ce mishi cikanka ba, na gama saka musu pampes, na kwantar dasu.
Ban daki na shiga tare da cire kayana, kawai ya shigo min.
Ban damu ba, na cigaba da abinda nake. Ina gab da gamawa ya tawo ya rungume ni ta baya.
Juyawa nayi na zari towel ɗina na fita, haka shima ya biyo ni, hmm.
Namiji babu kunya, tsakanin shi da Allah, yazo niman biyan buƙatar kai da kai.
Banza nayi dashi, yana matsa min nan fashe da kuka, tare da cewa.
"Uncle! Kai da kake da karfin nunawa min kai namijin duniya ba, kana da karfi da zaka iya gwadamin."
Jikin shine yayi sanyi, duk yadda yaso na bashi hadin kai amma fir naki, karshe haka ya janyo ni jikin shi tare matse ni, da mugun karfi.
"Kace min yanzun ka fara amfani da ƙarfin ka gurina, amma a can kuma kamar tsoron.."
Hada bakin mu yayi, cikin mugun haushi, cire baki na nayi da karfin tsiya.
...
"Wallahi ka rabu dani, idan kuma min, Allah na bar gidanka kenan."
"Wai me yasa duk abinda zai fito bakin ki, babu alkhairi daga kice zaki bar gidan sai kice zaki yi kisa, ba zaki bani hakkina bane."
"Ai hakkin me? Naga dai tsabar rashin tsoron Allah nan ka turmushe yar cikinka bayan ka mata fyade."
"Yumnah!".
"Shiiii! Kayi min shiru ka tafi dakin matar, yadda ka shimfid'a min mari, kaje na Barka da Allah, dan wallahi ban yafe ba."
Wannan kalmar yayi mugun b'ata mishi rai, dan haka ya mike yana gyara zaman wandon shi.
Dake Allah ya daura min tsokana, nace mishi.
"Malam! Ka gyara zaman wandon ka, naga kamar Ragon ka yana waje."
Cikin jin haushi ya juya zai min magana, kawai yaja zip din shi take yaja da fatar Ragon shi.
(🤣🤣🤣🤭🙆🏻♀?)
Wani irin kara ya saka tare da juya kai, yana wani hada kafar shi, me zanyi banda dariya.
Ciki ciki yace min
"Don Allah zoki cire min, wallahi na matse fatar gurin."
Me zanyi ban da dariya kasa tashi nayi, dakyar nazo na saka hannuna, na shiga jan zip din, tare da jin yadda take harbawa, ina cirewa da karfi na juya zan koma ya rike ni gam yana sauke ajiyar zuciya.
Kwace kaina zanyi, muka ji an bude kofar, nasan Matar shi ce dan haka nayi maza na saka hannuna cikin wandon shi tare da tab'o mishi kayan aiki.
A gigice, ya sake kara yana k'amk'ame ni.
D'agowa nayi ina murmushi, dan ya manta da ita.
"Ahmad amma kasan bani da lafiya ko? Kazo gurin karuwar yarinyar nan, ka manta dani."
Cire hannun nayi na koma bakin gadona na kame, sannan nace.
"Wallahi idan baki bar min d'akina na, in na fara zane ki, sai kin gane baki da hankali maza ficce min a daki na."
Ban rufe baki ba, tayi waje sannan shima da yake tsaye zip din wandon a bude nace.
"Malam! Don Allah idan zaka fita ka rufe min d'akina sannan kayi ƙoƙarin rufe alkalinka, da yake buɗe da sauri ya rufe, tare da saka kai ya fita."
Washi gari.
Ina fitowa na same shi a falon yana kallon sunnah tv, kauda kai nayi na wuce kitchen na dafa ruwan zafin tv sai dankalin turawa da na saya da kwai.
Ina gamawa na fito, zan wuce daki yace.
"Ina nawa?!"
"Ka cewa matar ka ta sauko ta girka maka."
Nayi wucewa na, daki.
Dan dole na sauko daga fushin da nake, tunda nice a ƙasar shi.
Sai dai tun ranar da ya bini da karfi bai kuma nima na ba, shima wai dan ran shi baya buƙata ba ne, a'a kawai wani abu Mamie ta gaya mishi akan kaddi ya nime ni, idan yayi haka kuwa toh bata yafe ba.
Ina zaune a gidan, amma cikin rayuwar aure na babu dad'i bawai daga gare shi bane, a'a daga nice.
Tun wani fita da nayi, naje gidan Mama Hussaina, ina dawowa na samu dakin a birkice, na zauna na gyaran amma na dawo na sami Mamie a gidan.
.... A hankali na fara jin wani irin yanayi a cikin dakin idan na kwanta zanji kamar za a falla min gadona, tare da jijjigani.
Sai na sauka sai naji an kwashe da dariya, a hankali na fara ramewa, gashi da ina jin muryan Umma Zuljah, yanzun kuwa bana jinta.
Bana kaunar dare yayi, domin yana yi bani ba barci, da safe kuwa ina idar da sallah zan dukufa da karatun Alqur'ani, shine nake samun nutsuwa.
Yau ina karatun naji shigowar Mamie.
"Ke wato kin dogara da taurin kai ko? Hmm! Dole ki bar min D'ana!"
"Ai waye dakin naki? Halwani! Wai toh yayi kyau, Hajiya Mamie gurguwa!" Ina gama fadar haka na juya abuna na cigaba da abinda nake.
. Tunda na maida hankali na, addu'o'in da saukar Alqur'ani, ai ba sai na nemi taimakon wanin Allah ba, Insha Allah Ubangiji yana sane dani.
Ko sati Uku banyi ba na daina jin kome a dakin, kawai sai kukan duji, wato Owl, bana barci sai na tsiro sallar dare.
Alhamdulillah, dan naga fa'idar haka, take na daina jin kome, sai me kwata kwata.
Na rasa gane kan mijina, idan ya shigo zai fita da sauri yace na fito falo yayi magana dani.
Na zata samun guri ne, sai da na fahimci ko dakin shi bayan son na shiga, idan kuma na fita unguwa zai bani kudin abin hawa.
Nayi tambayan duniyar nan meye na mishi dan wasa wasa, mun shafe wata kusan goma bai rabe ni ba, dan yarana suna niman shekara daya kenan, ina buƙatar mijina babu halin hakan.
Idan na tambaye shi sai yace min babu!
Kai karshe dai haka na zuba mishi ido, da naga zan cutu na mishi magana akan hakkina sai ce min yayi.
"Idan bazaki iya hakuri ba, zaki iya tafiya Allah ya bamu Alkhairi."
Fidda idanu nayi waje, ban san lokacin da mike tare da mika mishi hannu ba nace.
"Bani?!"
"Kinga bani son Damuwa me zan baki?" Ya tambaye ni tare da tsare ni da ido.
"Sakina!!"
Na fada a hankali, zuba min ido yayi a rikice, dan bai tab'a kawowa zan tambaya ba.
"Kinga ni?!"
"Halwani! Don Allah ka rabu dani kawai sallame ni, tunda ban maka kome ba, hakkina a lissafi na, ten months Kenan ko? Don Allah karka sani na fara abinda zai sani kuka har karshen Rayuwata."
Riko ni yayi muka fita, zuwa daki na, tare da ɗaukar yaran bayan ya umarce nie, na shiryar.
Muna fita ya sauke ajiyar zuciya, abin tausayi, d'akina da Ni kaina ne aka hada mana mugun Sharri, na karya dayawa abin da suka saka, wannan ne dai bazai tab'a iya kusantar inda nake ba, ko da kuwa dakin shi na shiga matukar a cikin gidan nake.
Shine ya kawo ni gidan su, a dakin shi na cikin shashin Hajiya ya ajiye yaran da suka yi barci.
Janyo ni jikinshi yayi tare da sauke ajiyar zuciya, kuka ne ya taso min, sabida yadda yake sauke numfashi, birkitani yayi samar shi, muna kallon juna, Hajiya ma bata san mun dawo gidan ba.
Cire hijab din da yake jikina yayi, yana kallon wuyana yadda na koma.
Shafa wuyar yayi cikin rauni yace.
"Kiyi hakuri!"
Kifa kaina nayi a kirjin shi.
Batun gaskiya, daga ni har Linah bamu fahimci, halin shi ba, tunda ta dawo da tana da hankali da ta rabu dashi, domin babu abinda ya haɗa su a dangane da rayuwar auren su.
Banda hoton da suka yi a can Afrika ta Kudu, toh babu abinda ya kuma, hada su dan kullum ta nime shi ce mata yake bai warke ba, tsabar