Showing 15001 words to 18000 words out of 115153 words

Chapter 6 - DANGIN RABI COMPLETE

23 Aug 2025

1516

take.
Abbi yace Allah kyauta nace Ameen duk gidan Nan Abbi Khaleesat ce farin gani Kaya ta dinka Mana mun Zama Yan gayu,Fadeela ce ta tabe Baki tace ke dalla to ba ita ta siya muku ba Yaya Fu'ad ne kike wani damun mutane,dama na tsani Fadeela Bata da mutunci nace Ni dai ita na San ta bamu Kaya waye ya bada kudi ba ruwana kishi kikeyi da ita Dan Allah Abbi ko kayan daki Kar ayi Mata na kasar waje ga na gida Nigeria iri iri wannan ko taje gidan miji me ta iya Sai bacci,Dariya akayi wasu dattijan suka ce oh wannan yarinya da surutu take.

Fadeela kuwa tace wlh sai naci ubanki a gidan Nan,Mama da Momy suka galla min Harara,Ina sani nace Bacci zata dinga Yi a gidan miji ta Zama kazama dama duk me bacci kazami ne dakin miji ma masu aiki zata Bari su gyara Mata Kuma girki ma Bata iya ba,Yan gidan Sunyi mamaki da sukaji Bakuwa har tasan Halinsu,Abbi yace yawwa Rumaila Yi musu Nasiha ko zasu gyara kunji yarinya karama ta fiki hankali,nace a Haka suce suna da degree,to a wajen miji wallahi zero zaku samu,Umma tace ai kuwa dai ya kamata ku gyara,Momy ranta ya baci Ana kushe Mata Yara Tace a gidan ubanki Kika San Haka shegiya munafuka,Nace ai Ni kwana Daya nayi da mutum Ina Gane Halinsa mutum Daya ne a gidan Nan na kasa Gane Ina ya nufa,samarin suna ta dariya,Shi kuwa ya sake Bata fuska a ransa Yana cewa Lallai yarinyar Nan sai naci Ubanta ta Raina ni.

Ni dai cewa nayi a tashi lafiya ganin kowa ya Bata Rai Ana Shirin cin Ubana sai na sulale na gudu,matasan sai kallo na sukeyi suna yaba surata,Islam yace gaskiya wallahi tana da kyau matuka ga kyan sura,Shima Hakeem yace sosai ma tunda ta shugo nake kallonta dukkan su suna da kyau Amma ita ta fisu har wayewa kullum sai ta gaishe mu Kuma zaka ganta Kamar Yar gida tana harkokinta,Dariya Sa'ad yayi yace Ni Kuma Excersise dinta ne ke birgeni Yar kauye tasan motsa jiki,idan munayi da Sassafe zaka ganta ta fito watarana ma tana Riga mu Fitowa da ita muke buga tsere,dariya Suka dinga Yi har Matan wata tsohuwa Tace wannan yarinyar dai? Ae ita fa Zan Fara koya Mata wasu kalolin na Mata ma,cikin bakin mazan Suma suna ta Yaba kyawu na,Hisham yace wlh ta shiga Raina daga Nan Fu'ad yace Ni Kam Bata birge Ni ko kadan na tsaneta ma,Islam yace ai Kai dama baka layin mutane,Shut up Fu'ad ya Furta Wai shi babba,yace ayi a gama taron Nan Ina da wajen zuwa Abbi.
Anci ansha anyi Addu'a aka saurari matsalar kowa sannan aka rufe da Addua duk masu tafiya ko kwana basuyi ba sabo da kudi kawai Suka Kama gabansu Yan gida Kuma Suka tafi inda zasu,Yan aiki Suka gyara ko Ina again.

Ranar nasan na batawa Yan matan gidan Rai ko Fitowa banyi ba Dan Kar su kamani su Zane Ni,Muna zaune a palon Nene sai ga Khaleesat ta shigo da fara'a nace sannu da zuwa farin gani ta balla min Harara tare da Mika mana karamar waya kowa Daya irin kana Yan Dubu bakwai kowa Tata kalar daban,Ihu Muka saki da murna sai tsalle mukeyi,ita kanta Khaleesat sai da tayi dariya ganin Haukar da mukeyi, Nene tana ta dariyar haukarmu,Fu'ad ne ya shigo da Sallama ganin na Fadi a kasa Ina ta birgimar murna Khaleesat Tace Wai akan wayar da kace a Basu tunda suna neman wayar aro zasu Kira iyayensu,Na tsaya cak nace wannan ma shi ya siyo Mana? Khaleesat Tace ae ai kuwa muka dinga zuba Masa godiya,nace kayi Hakuri kaji kasar Dana zuba maka a daki,ban San Haka kake ba,Kuma Ba tsohuwa zaka aura ba irin Iyata, Suleliyar Balarabiya ta kasar Afghanistan Yar shekara Sha shida ita zaka auro ko Yar Italy kaci taliya ka more wace Guda daya sabo da tsayinta sai ta cika plate,ko Yar China ka sharbi Dafgen kwadi lafiyayyu masu Zaki,kullum da safe ka karya da Kaguwa ko hantar kadangare.

Kuma Allah yasa cikin shekara uku ta Haifo maka yara biyar,duk wata biyar nasan zata dinga Haihuwa, Nan take Fu'ad ya sake cukulewa ya hada girar sama da kasa yace a ransa Wato ta maida Ni ayu Ni jarababbe ne zanta XXX da mace ba ji ba gani, Allah sarki Ni Kuma ban ma San komai akan ya abin yake ba a ganina yabonsa nayi.
Muna zaune Khaleesat ta koya Mana komai tare da saka Mana layi ciki,kowa da katin MTN na dari biyar aka saka Mana ta bamu tayi Tafiyarta.

Fu'ad Yana zaune a kujera suna Hira da Nene kadan kadan,Number Iyata na saka na Kira Bugu biyu ta daga, Salamu'alaykum waye,Da karfin gaske Kamar Ina magana da duniya nace Allahu Akabar Kaji Muryar Iyata,Iyata nice Yarki Rumaila,Iya itama da Karfin gaske tace Dan gidanku sai yanzu Zaki neme Ni? Hankalina Yana tashe,nace Iya yanzu na Samu waya ne,duk wayar dake garin a rasa me Baki aro?
Nan fa na Fara bawa iya labarin Alatu da abin Dadi dake gidan Iya tana ta dariya,Fu'ad Yana jina nace iya kullum da kaza muke karyawa wallahi Allah, nama muke ta faman ci Baki ga yanda na murza kiba ba Iya baza ki Gane Yarki ba na Kara ja, fari na ya dawo Kamar sanda Ina jaririya,ki fadawa mijinki kafin na dawo ya Sara Kofar Dakinki ta Kara Fadi sabo da kibar danayi Kofar tayi min kadan sai Fadi na ya cika ta taf, Fu'ad dai da Nene suna ji Haukar Yarinyar Nan ta isheshi shi kam, Yar karama da ita kwaila tace wani kofa zata Mata kadan,Gashin kaina na na jawo tare da Karawa a jikin wayar nace Iya gashi na kamshi Yasin shinshina kiji iya laushi,Amma sanda Ina kauye fatar jikina kamar Bayan Kada (crocodile) dariya Sai da ta kwacewa Fu'ad yayi kadan,Nace Iya babban Dan gidan ne yake ta Mana Alheri,A Haka Zaki ce Bai da kirki Ashe abin a zuciya yake Iya Imani ne dashi da Tausayi ya dinka Mana Kayan gayu ga waya kyauta me tsada iya wayar fa idan aka siyar da ita sai ta siya min Kayan kitchen na Aure,ko katuwar Akuya me ciki, Dariya ta sake kwacewa Fu'ad yayi kadan Nene Tace idan Rumaila ce zaka gaji da dariya.

Nace Iya Bari na Baki shi ku gaisa ki Masa godiya,Iya tace to,na Karasa gabansa da sauri na durkusa a gabansa tare da Mika Masa wayar cikin sigar rada nace Iyata ce Dan Allah fitar Dani kunya ku gaisa,Harara ya watsa min da mugun kallo Wanda sai da jikina ya dauki rawa Nene Tace karbi Mana karka Bata kunya,Da kyar ya karba Amma nayi mamaki cike da girmamawa ya gaida Iya ta dinga zuba Masa Addua da ruwan godiya sannan ya Mika min wayata na karba mukayi sallama,su Rabi duk sun Kira iyayensu Suma.

Washe Gari ma banje gaida kowa ba Ina tsoron Yan Matan Kar su Duke ni, Zama mukayi a dakinmu muna ta Hira, Nene Tace Yan Mata kuzo Palo kuyi a gabana ko ba komai nayi nishadi, bamu Dade da Zama a gefe ba can ba,wani kamshi na musamman ya dake mu mun San ma Fu'ad ne ai kuwa shine kullum sai yazo wajen Nene Yana sonta,yasha wata arniyar Shadda ruwan toka yayi azabar kyau ko wanne shiga yayi kyau yake zubawa, Kallon jikina nayi yanda Kaya Suka dameni Suka fito min da sura nace kalli gangare Ashe Ina da tudu da gangare Haka?ga tudu kalli Rabi ya Kika ga idan Muka koma kauye? Rabi Tace ai ta kofar Yamma zamubi Majalisar su Ubaliyo su kalla Haram shegu duk a rubuta musu zunubin kallo,Dama ba kallon Musulunci sukeyi ba ga gulma munafukai ai sai na sa sun dauki Alhaki suyi ta kallo mala'iku suna rubuta musu,a sanadiyar wannan sai kiji su Ubaliyo an ja su Jahannama,walakiri ya dinga buga musu guduma a tsakiyar kansu,dama sun ishe mu da munafunci munki Yin aure.

Fu'ad Yana jinsu Yana jinjina iyashegen yaran kauye kamar manya,Nene Tace tunda kuke Hira tun kafin Sallar Azahar Banga Kun tashi kunyi Sallah ba har anyi La'asar ga Abban Momy har ya dawo daga Office banji kunyi Sallah ba biyar ta wuce Shuru na lura Baku damu da addini ba fa ko bakwa zuwa Islamiyya ne? Nace Ni dai yau Allah ya gani bana Sallah na Sharo karya Dan Kar nayi bayan ko period ban Fara ba,Saude ta Dan fimu kokarin Sallah tunda tana yi sau biyu sau Uku a Rana,Sai tace karya sukeyi Nene wlh bama wata Sallah sai munga dama ko ta ganin Ido to karatun ma bamu Iya ba ko Al'ada bamu Fara ba Rabi ce ta Fara duk kawayen mu,Mamaki ya Kama Fu'ad,Nene ta saki Salati tace to me kukeyi a Kauyen? Talla Saude ta Furta wlh ba abinda Muka sani sai sirrin waken siya wajen soya Awara,Fu'ad ya girgiza Kai sannan yace su Fara zuwa Islamiyyar yaran gidan Nan wacce malami ke zuwa kullum da yamma Yana musu karatu Zan Masa magana Akan abinda ya Dace na addini su Fara sani ko ba komai kafin su koma zasu rage jahilcin Dake damunsu,Kuma Duk wacce Bata Yi sallah ba Nene ki fada min wlh sai nasa Guard ya Mata dukan tsiya a gidan nan,Ido na zaro Ni dai bana son yin Sallah,nace Alwala ce wahala kullum komai sanyi sai ka taba ruwa, Amma Haka muka yi mukus.

Washe Gari karfe Uku muka je part din da ake koyawa Yan gida karatun Addini Muka zauna can baya Muna ji kowa Ana Kara musu karatun Qur'ani da sauran littafai na musulunci,Malamin yace kune Fu'ad ya min magana a kanku ko? Ae mune Rabi ta furta,A gurguje ya dorawa Yan gidan karatu ya sallame su saura mu Uku kacal..


Malamin yace yanzu zamu fara daku daga farkon muhimman abubuwan da Addani ya gindaya da kuma abinda ya wajabta ko wanne musulmi ace ya sani. Zamu fara bayani ne akan abinda ya shafi tsarki tunda Addini baya yiwuwa sai an tsarkaka Kamar yanda Annabinmu Annabi Muhammad (SAW) ya koyar damu a cikin hadisi cewa: "Allah (SWA) mai tsarki ne tsarkakakke kuma baya karbar Aiki sai mai tsarki...." Har ya zuwa karshen hadisin. Tsarki dai kamar yanda aka koyar a cikin littattafai na Addini kala biyu ne, akwai tsarki na jiki sannan akwai tsarki na tufafi. Kafin musulmi ya aiwatar da ibada karbabbiya sai ya kasance ya hada biyun nan duka.

Da Sauri na Mike tsaye nace Malam tukur Aradu ka koma makaranta tsarki biyu kacal ai tsarki da yawa zaka ce biyu,kaji karya Yaya Malam kana Babba zaka dinga zugo karya,Saude tace kyale shi Rumaila Billahillazi da a garin mu ne Yasin sai su Garbati sun goce maka kashin kafada,Rabi tace Alqur'an kuwa Saude,Kai Malam Tukur kake me dalla dalla ko Malam tukuro to ba dalla dalla ba ko filla filla kake Yi Yasin Mun ci gyaran ka a nan,Malam ya kalle su yace to Ku sanar Dani kalolin tsarki,ke Rumaila kawo min su,Mikewa nayi tsaye nace akwai tsarkin bandaki,shi bayi Yana bukatar a dinga wanke shi kullum da ruwa da Omo,akwai tsarkin dakin bacci shima Ana share shi fes,akwai tsarkin kwaryar nono da fura,akwai tsarkin ludayin Shan koko,kokon da ake lailaya tuwon shinkafa duk a dinga wanke su fes kai baza su Irgu ba,Rabi ta kyalkyale da Dariya tace Malam a koma Maiduguri a Karo Ilimin Addini,Saude tace Ko za a samu ilim kulunboto ko ka samu kudi,Kai Malam ka zauna a banza gidan masu kudi Ana biyanka kudi kadan ba gwara ka koma malamin soro ba kana yiwa masu kudi aikin tsubbu Ana kaika Makkah a siya maka gida da mota da tuni ka zama me kudi gashi nan haddarka tana ta gogewa a banza.
Dariya Malam yayi yace baku da hankali ku saurare ni zan fara muku karatu ko nayi tafiyata.

Yana karatunsa Muna surutun mu,Saude tace kinga Talaucin Nan da akeyi a Kauye bana har fa Birni Wallahi Tallahi,Yasin akwai wani Dan uwanmu a birni wannan na kano me siyarda kayan kitchen,kin San har Makkah da Dubai yake zuwa Saro Kaya Nace ae ai Yana da kudi,Saude tace ai da kuka sani yanzu ya talauce ko Sokoto baya zuwa yanzu,Kafin mu taho Nan ya siyar da shanunsa na gado Wai zai Kara gado,Ni kuwa Rumaila nace Dubai din ta ubansa ce ko ta Uwarsa da dole sai yaje ya hakura Mana ya siyi na Nigeria,Saude taji Haushi tace ke Rumaila yayan Babana ne fa kike Zaginsa,Malam Haushin ba a sauraronsa yace Allah ya Kara jahilan banza ku saurare ni Nan







Sharhi please.



AsmaBaffa
, 🎈🎈🎈🎈
DANGIN RABI
🎈🎈🎈🎈









FREE PAGE









DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM








5










NA KUDI NE

DARI BIYU 200 GA MASU SHIGA GROUP.


Account number
0175487861, Asmau Garba Muhammad, Gt bank.

Masu turo katin Mtn ko vtu ga number
08033933642.

'YAN NIGER ku nemi wannan number
+227 90 79 59 39.








Official









By
AsmaBaffa









Page naki ne ke daya
UMMIN SADDIQ














Shuru Muka yi tare da nutsuwa, Malam Tukur yace zamu Dora da rukunan musulunci Amma ciki sallah itace cikar musulmi duk Wanda baya sallah to bashi da banbanci da Arne cikakken Musulmi Wanda ya tsaida sallah,baki na bude nace sabon salo duk kalmar shahadar Dana Yi wata zanyi Kuma sannan ace na zama Musulma Kai Malam Tukur Haddakar ta goge ka koma makaranta, kullum fa sai nace laaaa'ilahailallahu,harara Malam Tukur ya watsa min tare da furta gobe gaskiya sai Fu'ad ya zauna a wajen nan tunda ba karatun kuke so ba,na gaji ku tashi ku koma ciki na fasa koya muku komai sai a Gaban Fu'ad,kun fi karfi na,Mu dai ko a jikin mu dadin mu Muke ji tare da komawa part din Nene.

Malamin nan ya kwashe duk abinda Muka Yi Masa tare da sanarwa Fu'ad,Shi kuwa gogan yace kyale su zanyi maganinsu zan nemeka suka Yi sallama,Ni kuwa muna komawa na fara Shirin yin Awara sabo da Nene tace basu Iya ba Ana so a gidan Amma ko anyi Bata dadi kamar ta Wanda suka kware.
Bayan na dafa na matse awarar sai na koma bedroom dinmu na shiga toilet nayi wanka fes na saka doguwar rigar da Naila ta bani kwance nayi kyau,kitchen na koma na fara soya ta da kwai naji hayaniyar Maza da yawa a palon Nene ina soyawa ina bawa me Aiki tana kaiwa part part har wurin Abbi an Kai Masa ance Inji Rumaila ya dinga godiya,Nene ma tazo ta eba da yawa Gaban su Fu'ad ta ajiye musu da yaji masu Aiki suka kawo musu ruwa da lemuka, Fu'ad da abokansa su biyar gaba daya yan kwalisa ne irinsa akwai ji da Kai,Kamar baza suci ba sai da suka fara ci dadi ya kama kunnensu cikin su wani Khaleed cike da iyayin maganarsa yace wow so sweet waye yayi Nene? Nene ta Harare shi Jin iyayin da yake zubawa tace kwaji da shi idan zaku ci abu kuci sai shegen girman Kai,Dariya Nene ta basu.

Har Fu'ad sai ci sukeyi har na gama na zuba tawa a plate da yaji na a gefe na fito fes da Ni kamar ba nice nayi ba abinka da ba wutar itace bace bare ayi wujiga wujiga a fita a hayyaci, Khaleed ya kalle ni tare da furta Dan Momy wace wannan me kama da Kai ko kanwar ka ce gaskiya ina ciki ta hadu.

Fu'ad ya dage gira daya tare da yatsina fuska furta Amma ka gama Dani wannan nayi kama da ita? Ko a dangin Kauye Bamu hada jini da wannan ba da kugu kamar an daurawa Sanda zani,Dariya suka saki ba'a bata min Rai ba komai ke bani haushi Amma na tsani dariya watarana,ban San Sanda nace da nayi niyyar gaisar daku Amma na fasa wallahi ko sannunku bazan ce ba,Wani Hassan da yafi zakewa lebensa baki wuluk da gani kasan Yana zuka hayaki,Nace Kai ai ban damu ba Dan kayi min Dariya ba gaba daya kalar Dan wiwi ne a Sha a hankali dai kar Wiwi ta taba maka bargo ta zuke shi kana ji kana gani wanka ma za ace sai an maka ko yaro karami Yana dafa ka aga ka Fadi,idan ka sake ka haifi yara suna rikeka suna Oyoyo Kawai sai sai aga ka fadi gaban yaranka, ai gwara ni da Kai da kake wani yaye katon baki kana dariya sabo da Kawai Allah ya yika a birni anyi Ni a Kauye ai ba kaunarka Allah yafi ba Kuma.....kafin na karasa Fu'ad ya Mike a fusace idonsa ya canja plate din na ajiye zan kwashe da gudu sabo da na gama tsorata.

Nene ce ta fito da carbi a hannunta na fada dakin Nene ko ta kanta ban bi ba,ganin Nene idan ta gane zata hanashi dukana sai ya fuske ya murmusa yace Nene kicewa yarinyar can ta kawo min zobe na,Nene ta wani washe baki tace Ja'ira Rumaila tana birgeni ba duhun Kai gashi naga taku tazo daya ko da ita za ayi ne?Bari na karbo abina ya furtawa Nene tare da shigewa dakin,Ina Bayan labile na boye kamar ya sani nan Kawai ya nufa Yana lalube na a ciki zai kamani Kawai Bai sani ba ya cafki albarkatun kirjina Wanda ban

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login