Showing 36001 words to 39000 words out of 115153 words

Chapter 13 - DANGIN RABI COMPLETE

23 Aug 2025

1566

har Nayi wanka na shirya cikin Shadda ta Yar gaske fara Kal da adon dinki Kuma peach and dark blue,Me Daurin dankwali ta daura min dark blue dankwali sai na koma Kamar wata Amarya Nasha Yar make up kadan,Palo na fito Umma Tace Masha Allah kinyi kyau iri daya ke da Fu'ad sabo da Yadi goma ya siyo ya Masa yawa shine ya kawo min yardi Uku aka Dinka miki,naji dadi shike Nan za a ce shine ya Dinka Mana zasu sake sabuwar gulma,Umma kuwa wani material ta sha,Amarya lace me tsada Haka kowa gida ya cika da Yan gayu sai kamshi da kamshi,duk mazan Sun tafi daurin Auren Fadila a masallacin Unguwar,Angwaye sun zo,11am aka daura auren Fadila Suffiyan jawa da Angonta Engineer Sadeeq Igabi,Umma Tace Rumaila bani wayata wannan hoton ya Isa Haka kinyi kyau jeki wajen Fadila kice su zama Ready Angwaye zasu shugo,naga duk Yan bikin basa saka Mayafi Nima ban saka ba na tafi gaba na Yana faduwa nasan zan Sha wulakanci.

Ba karya Nayi kyau sai kallo na akeyi,su Rabi Dan Iyayi suna wajen Kawayen Amarya Ana ta tsokanar su suna kauyenci Ana musu Dariya,sannan sai aiki suke sa su suna Aiken su,Inda Fadila take Yar Aiki ta nuna min na shiga da sallama na iske Ana Mata kwalliya an ma gama nace Anty Fadila Umma tace Ki shirya Angwaye zasu shigo,Yan matan Amarya sai gayu ake Sha kowacce da Kalar nata haduwar,Lubna Tace ke Rumaila zo Nan Dan Uwarki dama Ina so na ganki ke ga Yar Iska ko jiya Ni Zaki ki Nunawa bariki? Tunaninki sonki yake Yi akan ya Miki ciki to wlh Fu'ad yafi karfin Yar Kauye irinki banza jaka Suka saki Dariya har da su Rabi,ban kulasu ba na tafi Abina dama duk sun Gama Shiryawa,Fadila ta daka min tsawa ke Dabba tsaya ki rike min wayoyi na da jakata duk Inda Nayi ya zama dole kina wajen sabo da zan na amsa waya,Ko a jikina na karbi wayoyi da hand bag dinta na tsaya tare da Yan matan kaf Muka fito sai ga Angwaye da Yan gidan maza da abokansu Har Fu'ad shima,Shaddar mu har zanen iri daya,sai bakin ciki ya Kama masu son Fu'ad da Yan Uwansa shi Bai San ma Ni aka dinkawa ragowarsa ba,kannen sa Mata gaba daya Suka lullube Fu'ad suna ta daukan hoto da shi wannan ya ja shi can wannan ta ja shi can,gaba daya Suka hadu Ana ta ruwan pics, da tsokana nace yawwa Nawan Fu'ad haska su ka fisu ka take su,sai kafi kowa kyau,ke munafuka rufewa mutane Baki cewar Lubna,Alhajin Qarami da matarsa shine Babba a gidan Amma ba a shaku da shi ba shima Ana ta pics da shi,uban DJ ne ke tashi a gidan har an kunna sai dare zasu tashi,Abbi ma anyi da shi,naje na tsaya kusa da Abbi aka dauke mu munyi kyau, Fu'ad ya shigo Muka saka Abbi a tsakiya,su Umma ma Suka fito akayi da su Anty Samha da yaranta Amaryar Abbi,kakar su Fu'ad ta wajen Uba itama an kawota dake ta Gama tsufa duk a susuce take ma bata Gane komai,su Nenen Kauye,Da ta Kano da duk wani Dan Uwa,sai Kawayen Amarya,Sai Angwaye,,Ana Kiran Fadila na Bata wayoyinta na silale na gudu,abinci na eba Dakina na koma Ni kadai na zauna Ina ci kenan Umma ta shigo tana kwala min Kira,na fito da sauri Tace Islam da su Abdulhakeem sunce kije kuyi hoto Wai kinyi kyau,plate din fried rice and chicken na dauka na tafi a Haka aka dinga daukan mu da abinci na a hannu,har aka Gama na tafi,Angwaye suka tafi Suma aka ci gaba da shagali.

Da Yamma Nayi wanka na canja Atamfar Riga da skert sai magrib aka tafi Kai Amarya a motar Islam naje,su Rabi ma sun je,a ranar aka Gama biki washe gari duk na nesa suka tafi har su Rabi nice kadai na rage sai Babar Abbi Wai sai Nan da wata biyu za a maida ita Germany Likita yaci gaba da kula da ita, Yan aiki sun Gama gyara ko Ina Kamar ba ayi taro ba,yau na samu Umma a Palo na durkusa nace Umma gobe zan tafi gida Inshaallah,Umma Tace hmm Rumaila kenan ai kinzo kenan sai dai kije Kauye da yawo,Abbi yace karma ki tafi,ga cikin dake jikinki duk yasa kina Shan zagi ki zauna a Nan har ki Haihu Allah ya Baki Miji na gari kiyi aure, a Raina nace wa zai auri irina ,Nasan ko na koma kauye to abin takaici zan ta ji,dadi naji a Raina, Nayi ta yiwa Umma Godiya har Abbi na je nayi Masa godiya yace ba komai.

Su Momy suna Jin labarin a gidan zan ci gaba da zama suka ce ai dole tana Haihuwa ta Basu dansu tunda dama son Dan shege sukeyi,Islam Yana Zaune Momy ta zuba Masa rankwashi Tace sai na ci ubanka wlh idan na sake ganinka tare da Rumaila Wato harda Kai ta gidan Amarya ko algungumi,Islam ya tashi ya bar musu dakin gaba daya.
Su Rabi Ana Kauye tunaninsu zan dawo sai suka ga shuru ai kuwa sai da suka bugo waya Suka tabbatar na bar zaman Kauye,Rabi ta cizi yatsa Tace ba komai zanzo ne Watarana sai na sa an Kore ki Rumaila,kinzo kin kwace min dangi Allah ya Isa matsiyaciya, Ni kuwa tuni Umma da kanta ta kaini Islamiyya ta kusa da gidan wacce a kafa ma zan dinga zuwa 4pm to 5:30,Bata ce na dinga zuwa ta gidan ba sabo da Yaran gida zasu wulakantani,Uniform kala Uku ta Dinka min da takalma,Ta Boko Kuma wata Yoruba ta dakko min zata dinga koya min turanci karatu da Rubutu,idan na fara Iyawa sai a saka Ni a makarantar Boko,Nasha murna Kamar na mutu,Haka na fara karatu kullum Umma tana sake koya min,dake Ina so sai na dage Ina naci da kokari, Fu'ad kuwa ba sosai nake ganinsa ba Yana Office sai dare,,yau ba school Toilet na shiga zanyi Alwala sai kuwa jini ya zubo zanyi fitsari,Ihu na saki me Aiki ta fado da sauri nace Kira min Umma kice tazo nayi Bari,ciki na ya zube Ina ta murna, Fu'ad lokacin Yana gida tare da Umma me Aiki ta Fadi sako na,Umma itama Tace Kai Alhmdllh ta shigo toilet din na nuna Mata taga jini kadan,ta kawo min pad Tace shirya mu tafi asibiti,Haka nayi wanka na wanke toilet dina na shirya na saka Arabian gown tare da yafa Mayafi nta Muka tafi Umma da kanta ta tuka motar Muka wuce Asibiti daga Ni sai ita.

Wani private Hospital ta kaini Bayan bincike Likita yace ciki Yana Nan lafiya Kalau Period na fara dama wasu Ana samu ko suna da ciki suna yin period,Murna ta koma ciki,magunguna ya Bamu Muka dawo gida a Palo Muka Iske Fu'ad,Yace Umma yaya? Umma Tace ai Yana Nan daram,Dariya yayi Yana kallon fuskata wacce kadan ya rage na fashe da kuka,Magungunan na watsar a wajen nace Allah bazan Sha ba don Kawai yaron ya samu lfy to wlh bazan Sha ba ya mutu Dan shegen Banza,Kuma wlh a waje Zan na kwana Sauro yayi ta cizo na malaria ta Kama shi yaji jiki ya Sha wahala, ko na koma Shan ruwan rijiyar Typhoid ta Kama shi me karfi ta bubbula Masa hanji, Fu'ad Yace kanki kika yiwa mu Ina ruwan mu uban waye yace kiyi cikin,Umma ta haura sama ta barni tana Masa fada.
Bayan kwana Uku Umma Tace da Fu'ad ya fara kaini awon ciki a madadinta,Haba Umma so kike a ci gaba da zargina?ai zargi ya Kare tunda a bikin Fadila ka Nunawa mutane zahiri ka kiyayeni Fu'ad, tunda baza ka bi Umarni ba Ni Zan kaita da kaina, I'm sorry Umma Zan kaita ya furta Yana Bata Hakuri tace gobe Monday sai ka kaita ,Okay Allah ya kaimu ya furta.

Ali Me shayi kuwa ya Gama ganin take taken Iya so take ya sake ta shi kuwa yace zanyi maganinki,Duk wulakancin da Iya zata Masa sai ya kyaleta ko kulata ba yayi,Iya tayi tayi Amma Me shayi yaki sakinta,Haka Kawai dabara ta fadowa Iya sai ta dinga fita unguwa baza ta sanar Masa ba, shi kuwa ko ya ganta ko ya dawo ya Iske ta a gida baya ko cewa ya akayi ta fita Bata tambaye shi ba,Kuma bazai nuna yaji haushi ba,Kamar kullum Haka Iya zata ganshi Kuma ko Zaginsa tayi dole idan yazo dakin ta ranar kwananta to fa sai ya sadu da ita,ko ta Hana ta karfi zai Danne Iya yayi abinsa,Shi har ya fi so ma Tace baza ta yarda da shi ba sai ya sa karfinsa,Iya taga da wannan tsarin nata baiyi ba sai ta fara tsanar yayansa tana azabtar da su kullum cikin fada da kishiyarta take Amma me Shayi yace hakki a kanki Kuma wlh yara ba ruwansu Dan Haka ko a jikinsa,Ah Iya ai sai taga Nan ma baza ta bulle da ita ba,Idan ya shigo sai taci kwalarsa Tace ka sake Ni idan Kai Dan halak ne,Me shayi ya samu ya wawwankawa Iya Mari ya hankade ta ya shiga harkarsa Kuma da dare ba zai fasa ba sai ya karbi hakkinsa,Iya ta sake canja plan sai ta dinga Wayar karya tana soyayya a gabansa Wai da samari shi Kam ya Gane tana Yi Yana Dariya,sai da Iya tafi sati tana Wayar Iska shuru ba saki,ita kadai ta fashe da kuka sai an sake ta lallai,da Daren ma sai ta daina bacci Sam sai ta kwana tana kuka Kamar me Aljanu,Har mamakinta me shayi yake yi,Yau ma Yana kallonta cikin dare ta fice daga gidan ta dawo zaure ta kwanta tana ta kuka,ya fito ya kalle ta Kawai sai ta bashi tausayi yace Allah ya shirye ki,Kudi ya zaro dubu Uku ya shafa Mata a fuska kafin kace me Iya ji kake luf ta Mike Zaune zumbur tare da furta kudi ne?????? Laaaa Kudi....Me shayi ya Mika Mata yace gashi,da sauri ta karbe Tace na gode duka Nawa ne? Me shayi yace ae ki siya abinda kike so,Ya juya zai tafi Iya ta riko rigarsa Tace yau kwanana ne fa,yace na sani ai,to yau baza kaje garin shagali ba ne? Dariya me shayi yace Baki ji sunana ba Ali Shagali muje na hau hanyar Shagali na,Iya ta bishi ba kunya.

Amadu Affa na a bakin kasko yake Yana ta suyar fanken siyarwa Yana rike da matsamin Fanke daure da zanin Leshi milk, wasu Yan Fulani da suke kunna Dj a kasuwa Ana zuwa suna turawa mutane film Ana biyan kudi Suka saki Dj Yana suya Yana cashewa Yana wani karairaya tare da girgiza da kirjinsa Yana shewa,Ana sa wakar wani tsohon mawaki wato Na gwagwa,Affa da karfi yace Ahayye ah Subhanalla tare da Dora Hannayensa a saman Kansa Yana cashewa da kugunsa Yana murgudedeniya Yana fari da ido ko kunya baya ji,Allah ya rufa min asiri na bar garin da bakin ciki kadai ya ishe Ni,Ni Kuma ga cikin shege Kai bala'in yayi min yawa.

Washe gari Monday da wuri na shirya Fu'ad Yace na same shi a mota ya Sha farar jallabiyya Yana kamshi a wata dalleliyar motarsa fara na hango shi,sanye nake da bakar Abaya nayi Rolling,Gaban mota na bude na shiga da jaka ta a hannu,ta saman bene su Momy suna ta lekowa suna gulma suna cewa ai wlh awo zai kaita da gani matsiyaci kunga, Kai karshen duniya ya Gama bayyana sai dai mu bugawa mutanen Niger waya muce tashin kiyima yazo da Cameron da chadi ma sai dai suji a labari a wajen Yan Nigeria kafin ya karasa musu can,Momy Tace yaron Nan Mama kinga dai Ni na Raine shi wlh duk ya Gama sire min na tsane shi,Kuma yanzu ya juya Mana baya Ummansa itace Kawai Uwarsa mu Bai dauke mu Uwa ba,Mama Tace yo itama Umman tasa Baki ga ta daina shiga harkar mu ba,Dan taji munji Danta yayiwa wata cikin shege daga fadar gaskiya,Namiji munafuki ne shi Kuma Abbi yabi bayansu ya dauki son duniya ya dorawa Rumailan nan,nasan da ace ba matansa hudu ba to wlh da shi zai Aure ta,itama Amaryar tasa Samha taga Umma ta iya Munafunci tana bangarenta tare suke zumunci mu bata ganin Kimar mu,Yaranta su Suhaila gaba daya sai wajen Umma.

Baba Jummai wacce Yan fashi suka ce Fu'ad ya sadu da ita na fanshe ta,tana Mopping Tace Momy ai Ni nasan komai Nan ta kwashe labarin abinda ya faru tsakanin mu da Yan fashi ta fada musu,Tace Ina da tabbacin a Nan ya fara amfani da ita sannan daga Nan an Bude Masa hanya Suka ci gaba da mashaarsu tare har ya Mata ciki,Baba Jummai har da rantsuwa a gabanta aka Yi komai,Bayan Bata sani ba lokacin ba ayi komai ba,Momy ta rike Baki Tace cab lallai ai ke Jummai Baki da wayo Baki Gane bane na Sha kamata a part dinsa,dama na Sha Kama su shi yasa ai Tace ta fanshe ki ba Dan Allah tayi ba,Baba Jummai Tace biri yayi Kama da mutum munafuka harda kukan karya Ashe na dadi ne,Safna Tace ai Baki ga zahiri ba a Wedding Dinner Anty Fadila ba? Mama Tace kafin Azumi ai Fadila zata zo da Yan Sanda a kamata Ana zarginta da cunen Yan fashi Wai Tace Yarinyar Yan fashi ce,ranar yini sukayi suna gulma,Abbi Bai San me suke kullawa ba ya Gama shiri ya tafi Dubai daga can gaf da Azumi zai wuce Saudiyya acan zaiyi Azumi har a Gama sai Bayan Sallah da sati daya zai dawo,dama komai a hannun Fu'ad yake,Su Momy sai murna sukeyi zasu Kama Rumaila a kulle Ni.

Ni kuwa Ina motar Fu'ad sai kamshi da sanyi kida na tashi sama sama na wakokin turawa,Yana Driving a hankali baya magana Nima bance komai ba Gyada ta nake ci kadan kadan,daga cikin garin Abuja naga Mun fita,tsoro ya kamani Yana satar kallo na,Wani kauyen gwarawa ya shiga sai ga wani Asibiti Karami na Gomnati marar kyau,kafin nayi magana yace yes shi Zaki dinga zuwa awo tunda kika Yi cikin shege ai dole ki Sha wahalar rayuwa Kin karya dokar Allah kin dinga Shan azabar rayuwa kenan,murmushi nayi nace ta Kai ta kauyen mu? Ke kika sani,nace hakan ma na gode a bakin Asibitin ya tsaya tare da furta fita kije kibi layi cikin talakawa ki Sha Ranar masifa idan Kuma ruwa ya tsuge ya zane mana ke tas, ki dawo gida Kuma mura ta kamaki kiyi ta kwala tari da atishawa,majina ta Hanci ta makoshinki,Dariya ya bani na dinga kyakyatawa sosai,Dubu biyu ya bani kudin Bude File da Kuma kudin mota ya juya yayi tafiyarsa.

Ni kuwa ciki na Shiga da tambaya nayi komai da ake bukata aka Bude min file da komai,Likita ya dubani har da scanning komai lafiya Dana Kuma Namiji ne, duk ranar laraba Zaki dinga zuwa awo,Bayan na Gama na fito naga masu siyar da kayan ciye ciye iri iri,kwadayin me ciki yasa na tsaya na siyi Data,na siya Aya,na siyi kwakwa da dabino da sauransu,wata rigar jariri ce ta birge Ni na siya na hada kayana a katuwar bakar Leda sannan na shiga Taxi na koma gida.
Umma ma Bata Nan taje biki,Na boye kayana a daki,nayi wanka tare da gabatar da Sallar La'asar na ebo abinci naci abinda nake so.

Washe gari da safe 11am sai ga Fadila Amarya da motar Yan Sanda mota Guda a gidan.









Masu sharhi Ina matukar godiya,Kuna birge Ni wlh.










AsmaBaffa.
🎈🎈🎈🎈
DANGIN RABI
🎈🎈🎈🎈









FREE PAGE








DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.








NA KUDI NE

GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE


ACCNT NUMBER
0175487861,ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK.

MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER DA ZAKU TURA
08033933642

'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER
+227 90 79 59 39










26-30








Official








By
AsmaBaffa
Page naku ne

BEAUTY BOSS
UMMU AYMAN
M BELLO
NANA FIDDAUSI BELLO
RAKIYA YUSUF OZEGYA
PRETTY DEEJARTH
MARYAM ABACHE
OUM SAFWAN
SHAMSIYA BASHAR
FATIMA ZAHRA BINTU











Allah yasa naji hayaniya Kawai na leka ta window Naga Yan Sanda da yawa,Sai ga Umma ta shigo da Sauri tana cewa Rumaila bi ta Kofar baya ta kitchen ki koma part din Fu'ad ke akazo za a Kama fa, ai ban ma tsaya ji ba na fyalle da gudu na Sha kwana tuni su Safna suna hayaniya tana Ina bauraniya ki fito Ina jinsu a hankali nace baza a fito ba,Nene ta fito tana Hawaye tana basu Hakuri sunki ji Yan matan suna sai Mun daure ta Wallahi Khaleesat harda tsalle,Allah yasa ban hadu da kowa a hanya ba na fada cikin palon kasa na fita,Karo naci da mutum gaf, kamshinsa ya daki Hanci na,Ya Gama shiri zai fita Office,Ina Haki nace ka taimakeni Police dasu Fadila zasu kamani za a kaini gidan yari wayyo Masifar tayi min yawa Wallahi bazan iya daukan wannan ba,wannan dai bazan iya ba kaddarar me girma ce, Fu'ad yasan kan zancen dama, yace ke Calm down kwantar da hankalinki,Kinyi wanka? Na daga Masa Kai Alamar nayi,Ya kalle Ni yace kayan Nan naki sun min local bazan iya fita da ke ba Haka,Dan Allah ka taimaka nasan iyayinsa ne Amma shaddar bikin Fadila ce a jiki na irin tasa nayi kyau Kuma,shi kuwa kana Nan Kaya ya sha,Muje to,nace Na'am? Muje zasu kamani muje nace ko? in bakya so Zan tafi,shahada nayi na jera da shi Muka nufi inda Yan Sanda suke Ina ta cewa Yan Sanda fa wayyo,Hannu na ya rike Kam cikin nasa,Momy da yatsa ta nuna mu tana Officer gasu can,Duk Yan gidan har maza suna wajen da Yan aiki an cika, Fu'ad ba mutunci ya Bata fuska kamar Bai taba Dariya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login