Showing 45001 words to 48000 words out of 115153 words
na Shiga tunanin inama ace Ni da shi ne tunani na koma Yi Ina kallon Masoyan a nice da Fu'ad Ni kadai nake Jin Dadi Ina nishadi abina su Umma suna ta kallo na da mamaki sai ji nayi Naila ta kwala min Kira,firgit na dawo hayyaci na sai Naga Ashe ma sun min nisa sosai da sauri na tafi na Karasa Inda suke,Umma ta rankwashe Ni tare da tambaya tunanin uban me kikeyi sai wani dariya kikeyi ke Daya Ana kallonki a kwarkwar, Baki na bude da niyyar yin magana kenan kawai sai ga wasu masoyan daban sun fito da take away suna farin ciki,ai hankali na ne ya sake kwacewa na bisu da kallo Ina haskowa a Raina nice da Fu'ad Baki na a Bude,Umma haushi yasa tayi gaba Suka barni har Suka siyo abinda zasu siyo Ina Nan inda Suka barni Ina tunani da kallon masoya,Cikin fushi Umma tasa Driver ya maida Ni gida ta fasa yawon Dani,Hakuri na Bata Amma Tace wlh sai kin Koma gida,Dole na shiga mota Ina ji Ina gani Driver ya figi mota Ni kadai ya kaini gida shi Kuma yayi tafiyarsa wajen su Umma,Ina ta Jin Haushin kaina,maza na gani sun cika Palon Umma nasan friends din Gogan ne Fu'ad,sallama nayi kawai Ina fushi na wuce su ko kulasu banyi ba na wuce Bedroom Dina, Fu'ad a ransa ya dinga dariya yasan Dole akwai abinda nayi aka fasa zuwa dani,Abokansa Suka ga Kawai ya sheke da dariya shi kadai kallon kallo suka fara tare da tambaya lafiya? Fu'ad yace wata ce Yana ta Dariya.
Abokansa Basu tambayi wace ba sabo da sun San Suna da Mata da yawa a gidan,Islam ne ya shigo Yana Kira na mayafi na yafa tare da Fitowa Hannuna ya rike Yace fito muje yawo tunda Allah yasa har yanzu mu tuzurai ne anki ayi Mana aure muje ko na rage Tuzurantaka, bani da budurwa muje ki Dan rakani yawo,Ya Fu'ad Yana kallon mu na janye Hannu na Nace to Bari na fito...Muryar Fu'ad Muka tsinta da Gadara ya furta Umma ta hanata fita sabo da shirmenta,Kai kaje Kai daya ko ka tafi da budurwarka ko dole sai da it? Islam yace Zan sa ta gyara,Baki Fu'ad ya tabe Suka ci gaba da hirar su Ni Kuma Muka fita da Islam Ina ta murna.
Shi yake Driving da kansa Muna Hira Ina gaban mota me kamshi Haka Ina ta kauyenci Yana min dariya har muka Gama yawon mu har dare 9pm bamu dawo ba,lokacin Muna wajen Shan Icecream na kalle shi nace Ya Islam ya kamata mu tafi gida sabo da Umma zata min fada Kuma Bata San na fito ba,Ke matsoraciya ya Furta Yana dariya ba abinda zata Miki matukar taji tare muke,Umma kuwa sai Magrib Suka dawo ta iske abokan Fu'ad suna ta Hira an cika gabansu da kayan ci da Sha,Umma Tace yau Kuma a Nan aka ya da zango Kai Dan Momy Ina Rumaila? Sabo da munafuncin Fu'ad sai cewa yayi sun Fita da Islam yace sai dare zasu dawo idan anga Shuru a rufe gida yau idan ba dare ba sai ta Fadi,Umma ranta ya baci tace Amma tafi karfin ita Rumailan ta sanar min zata fita ,Umma tana ta fada ta Haura sama tana cewa bazan kirasu a waya ba Bari naga hankalinsu.
Abinka da Family friends Basu ce komai ba hirarsu Suka ci gaba da yi,11pm Muka dawo gida lokacin Fu'ad ya raka abokansa sun shiga motocinsu,Umma kuwa Bata Yi bincike ba ta sa key tare da kulle part dinta gaba Daya, Fu'ad Yana ta dariya a ransa,ko da na Karasa ba irin bugun da banyiwa kofa ba aka ki Budewa,na shiga Kiran wayar Umma Bata daga ba,Hannu na Dora a Kai nace wayyo Naga ta kaina ya zanyi,diri diri na farayi a wajen har na gaji na tafi sashen Nenen kauye itama nayi Rashin sa'a tayi bacci ta kulle ko ina.
Rasa inda zanje nayi sai kawai na wuce sashen Yan aiki tare da shiga dakin Tasalluwa,Da fara'a ta ce Rumaila Hala dai kinyi dare Umma tayi fushi? Kai na daga Mata alamar ae Ina zama a saman gadonta, Hmm ya kamata dai ki kiyaye kina cin arziki karki wuce gona da iri kina gani yanda ake ta munafuncin cikin Dake jikinki kadan Su Momy suke jira sunce wlh sai kin bar musu gida,Da mamaki na kalli Tasalluwa nace yanzu Zancen cikin Nan har yanzu ba a daina ba? Waye ya fada?Murmushi Dattijuwar tayi tace Babu Wanda Bai sani ba har makwafta wlh ki taka a sannu a banza ake kallon ki ya kamata ki boye kanki sabo da Baki da daraja a Idon kowa,Allah ya kyauta na Furta cike da kunyar kaina,Tasalluwa Tace ke yarinya idan ta sake kacamewa ki Fadi gaskiya Fu'ad shine ya Miki tunda ai Fyade ya Miki Yan fashi Suka Sanya shi Dole,A Raina nayi Murmushi nace Lallai Tasalluwa Bata San gaskiya ba,ai daga baya sace Ni yayi ya min ciki ranar da Yan fashi Suka Zo ba abinda ya faru sai Bayan sun tafi ya cuce ni,a fili kuwa nace Zan fada Inshaallah ai ma kowa na gidan ya sani tunda ai kin San rigimar da aka Yi,Dan dake ciki na zai nuna za a ga da wa yayi Kama,Allah ya kyauta a Nan na kwana.
Washe Gari da hantsi sai Dana Yi wanka naci Abinci 11am na shiga part din Umma,a bedroom dinta na sameta wani mahaukacin sabon kamshi ya daki hanci na Ina Shiga na Iske Fu'ad a ciki yasha farar Shadda Yar gaske komai fari yayi kyau har ban San da ya Zan misaltashi ba,Umma ke taje Masa Sumar sa tana sa Masa mayuka masu tsada na maza sai sheki da kyalli take Yi,Yana ta Shagwaba Yana Kara Wai Umma tana Jan gashin da karfi,Naga Alama so kake Yi ka makara a meeting din Nan kasan Kuma Abbinka wlh sai kasha fada,Banyi zaton Umma zata kula Ni ba Amma sai Naga da Fara'a ta amsa min hakuri na Buda Baki Zan Bata ta katse Ni ba damuwa ki kiyaye gaba kawai ban son kina shiga sabgar Yaran su Momy kin San Halinsu so kike a kulle Miki wani sharrin kenan, Inshaallah na daina na furta tare da kallon Fu'ad kadan Yana ta uban kwalisa nace Ina kwana ya Fu'ad ba tare da ya kalle Ni ba yace karki sake kulani matukar Umma Bata Miki komai ba na hukunci kina abinda Kika dama,Dariya ce ta kamani nace ta yafe min,Umma ya kalla yace ayi Mata hukunci wlh Umma jiya ta Bata min Ranki Kuma kina bacci ta Kira Wayarki,sannan ta buga Miki kofa cikin dare sai an hukuntata .
Karka dameni duk ba Kaine ka rura wutar ba,ficewa Yayi Yana cewa sai na dawo, tunda ya fita Bai dawo ba sai dare wurin 9pm lokacin Ni kadai ce a Palo Ina kallo na Mike Zan dakko ruwa a kitchen Ina Mikewa duf ba dalili wuta dauke duf,duhu ya mamaye ko Ina bana Iya ganin komai Ni Kuma ban San Fu'ad ya dawo ba sai kamshinsa naji daf Dani ba zato naji ya min zazzafar runguma tare da kwanciya a jikina Yana cewa Umma na dawo,jiki na ya dauki rawa da sauri nace Ba Umma ba ce Rumaila ce fa,wuta ce ta dawo fal haske ya bayyana sai ga Umma ta fito daga kitchen da sauri ya sake ni ya tsuguna a kasa ya fake da gyara takalmi,Ka daina batawa kanka lokaci na ganka cewar Umma,yace ai nayi tunanin kece Umma karya kakeyi Fu'ad kana sani kasan Rumaila ce Algungumi,na sanka fa ba abinda za a gaya min a halinka,Fuskewa yayi shi fa ba Haka bane,Kallonsa nayi Muka hada Ido nace to nesa ta matso kusa kenan? Ka fadi Soyayyarka wa zai hanaka,Ni Zan rike maka sirri a sirri zamu Yi soyayyar mu bazan Tona ma asiri ba,Baki ya tsuke Allah ya kiyaye naso me cikin shege yarana su gado halin banza,Ka nemawa yayanka Uwa ta gari,ke ai ba ta gari bace,da ta gari ce Zan Iya manage dake kafin na Karo ta biyu,yanzu kuwa Nan da kwana Uku zaki ga Budurwa ta matar da Zan Aura zata zo gaida Umma,Allah ya kaimu na fada Ina Jin wani kishi a Raina.
Banyi tunanin da gaske bane Wai Ranar Saturday Uku ga Sallah sai ga Budurwa katuwar gaske Yar gayu ga tsayi ga jiki wankan tarwada,ta Gama hadewa tana ta kamshi Wai tazo gaida Umma Kuma Wai Fu'ad ne ya kawo ta,lokacin naci kwalliyar Sallah Ina niyyar zuwa gidan kawata Yar makarantar Islamiyyarmu,Ina ganin Naila tana ta wani ji da ita ta rasa inda zata sa kanta,tana cewa budurwar ya Fu'ad ce Rumaila zo ki gaishe ta kuyi Hira kafin Umma ta dawo,Yar gidan matemakin Shugaban kasa ce Amal ce,Me gidauniyar tallafin marayu.
Raina ya baci kishi naji kamar na kashe su har Nailan,Karasowa nayi na zauna Ina fushi nace kika ce Yar gidan matemakin Shugaban kasa ce? Naila tace ae Amal ba,Nace to matemakin Shugaban kasar yaci kan Babarsa,dama ke nake Nema wallahi ki fadawa Ubanki da shi Shugaban kasar hakki na Dana Iyata da hakkin Affa,Dana Kanne na da hakkin Yayye na ya fito Mana da shi,bafa za mu yafe ba,Allah ya Bamu kudinmu ta hannunsu har ga Allah a fito min da hakki na,Amal ta Bude Baki tana kallo na,Ae nace kalli da kyau,Bayan hakki na dake hannunku har wani gaishe ki zanyi? Wannan wanne irin Rashin mutunci ne Rumaila? Bakuwa ce fa Cewar Naila,nace ki cire Fu'ad a ranki yafi karfinki baza ki same shi ba,ba kalarsa bace kin Masa tsayi da fadi,kin cika Fadi kinyi banga banga,Ya akayi kika sake kika cika mudun jikinki Amal? Mudunki yayi yawa,Amal Tace ke wallahi ki kiyayeni Dan nayi kanwa biyar dake sai na bubbuga ki da kasa,nace yanzu kika Yi bayani me kyau Ashe tsohuwa ce, na dake Ina ta masifa,Naila ta Kira Fu'ad a waya ta fada Masa abinda nakeyi,gashi Naila tace na tafi naki tafiya nace sai na ga kwal Uwar daka,Nace wa aka Isa ayiwa ciki ace za a auri wata wallahi Tallahi Bai Isa ba,ya min ciki ya auri wata,to yazo ya kawo Likita a daura min ruwan nakuda na Haifo Masa bakwainin Dansa na tafi abina,Amal ta Bude Baki taga da gaske nake Bata ga Wasa ba,Tace Ciki? Nace kwarai muje asibiti a gwada ki gani da kanki,kalle Ni da kyau ba Yar Nan gidan bace zuwa nayi.
Amal Tace kina da gaskiya dama Ni kawarsa ce Muna Business da juna ne,gaskiya Ina sonsa Kuma yanzu yace Dama auren dole za a Masa gwara ma ya aure Ni,shine fa zamu yunkuro da soyayyarmu,nace ba yunkurowa ba kuyi Aman soyayyarku ma baza a samu Result na
Aure ba,Ahhhh nace kuyo Amanta ma ba yunkuri ba kinji,Amal taji masifa ta isheta sai masifa nakeyi nace Haka kawai,Tace to ya aure mu biyu Mana? Murmushi nayi nace kina ganin kishi Dani zata miki kyau? Ni Rumaila Zama da kishiya babu,Amal Tace sabo da me? Sabo da ba son zaman lafiya nake ba Ni,Dariya Amal tayi tana kallo na banfi ta min dukan tsiya ba Yar karama Amma sai ji da Kai nakeyi,Mikewa tayi Tace Ki gaida Umma in ta dawo na tafi,ta tafi Na zauna Ina masifa Ina hararar Naila,ta fita tabi kawarta.
Umma tana dawowa nace Umma Sannu da Zuwa,Umma Zaki ji labari yau nayi tijara a gidan Nan,Wai wata tazo budurwar Fu'ad Amal,Zata min Yanga da kuri akan Wai soyayyarta da Fu'ad tazo Nunawa a gidan Nan sun Yunkuro zasu Yi amanta,ba kunya fa Ni Kam gaskiya na ci Mata mutunci,Umma tasan zancen Naila ta Bata labari Tace to ai ba budurwar sa bace shashasha meeting tazo sukayi su gomane Mata da maza tsokanarki Naila tayi,Wani jiki nane yayi sanyi naji kunya ta kamani,nace Zan dinga bincike daga yau na daina gaggawa Allah ya Bata Hakuri ai nayi tunanin Umma ke tazo zata yiwa rashin kunya a gabanki shi yasa nayi maganinta kafin tazo ta fara cewa Fu'ad I love you a Gaban ki,Dariya Umma tayi tasan wayancewa nayi,Tace ke da Fu'ad Kuna Raina min Hankali Rumaila a gidan Nan,zamewa nayi na gudu.
Fu'ad kam shigowa yayi ya juyo muryata Ina ta Dariya muna waya da Jauro,Nace Kai Jauro ka rage karya Kai Jauro yaushe ka Zama Dan Sanda?
Fitowa nayi Ina waya na wuce shi a Palo tare da Umma kafa ya sa min a hanya na Fadi,Kuma ya fuske Kamar ba shi yayi ba,Umma Tace kyale shi Rumaila Allah ya saka Miki,Umma Tace ke Rumaila wannan cikin naki yaki girma Abu ya tafi wata bakwai Kai gaskiya sai na kaiki babban asibiti an duba,Kina gani yarinya ta lugwigwice ta Gama lafkewa duk kamannin masu ciki gashi Nan Umma Amma kice wani babban asibiti Zaki kaita,asarar kudi dai cewar Fu'ad,Kai da kace baka kallon Mata kafi karfin ka kalle su me ya kaika har kasan Rumaila ta Gama Lugwigwicewa,Umma yanzu sabo da Allah bazan kalli mutum by mistake ba,Yarinyar da ta rainani duk abinda take min sai ace bazan Bude Ido ba sai na rufe a gabanki jiya kina gani zata wuce Ina bacci ta ja min gashi tare da kwalla min Kara a kunne,Kai kuma rannan mintsininta kayi ko ban ganka ba? Cewar Umma ta furta tana Mikewa ta haura sama,Tana tafiya yace Ke bude cikinki na gani Yana girma ko baya Yi? Nace Ni bazan Bude ba,yace to karya kike dama ba Wani ciki,nace wallahi Ina da ciki,to Bude na gani,Rigata na dage sama,shi Kuma harda Kanne Ido daya Wai duk salon kallo yakeyi Kamar wani me kallon Kallo-kallo,Yace Kai.....ya girma gashi Nan ya fara kumbura,nace Allah da gaske?Yana ta faman kallon cikin Yace a hankali da slow aeeeee....ka....Mar.....Haka......nake......ga......ni,naja rigar Zan rufe yace tsaya ban Gama gano gaskiya ba matso kusa da Ido na sabo da idona Watarana baya gani sai nasa medical Glass shi yasa Ni bana son farar mace sai baka sabo da Ido na yafi iya kallonta sosai,Harararsa nayi na matsa gaba, ban Gane wayonsa ba Ni Wai dole sai ya kalle Ni tunda yace baya Iya kallon farare,na matsa sosai nace kalli,yace da slow Yana Kanne Ido daya ai....ke....haskenki....na kashe Ido Ne dishi dishi nake gani,Tafiyar Umma mukaji da sauri yace a hankali rufe gobe Zan karasa kallo na tantance,na rufe da sauri na Fadi a kasan carpet na kwanta Kamar kallo nake Yi,Allah yasa Umma Bata ganmu ba.
Iya ce ta sa Ali Shagali a gaba Yana Zaune kamar TV a gabanta ta zura Masa ido tana far far da idonta Wai a dole fari take Masa na soyayya sabo da jiya ya Bata kudi dubu Uku,Kamar sabon kamun hauka,Ali Shagali yace a gaskiya Ni na gaji Iyan Rumaila Haba tun kina kallo na da marmari har sai kin koma kallon Muni na,tun safe da hantsi kin hanani fita Kuma kince ba kwanciya ba tsaiwa sai dai na zauna a gabanki kiyi ta kallo na,tun kina ganin kyawuna ai sai kiga Muni na,Nima Kuma tun Ina kallon kyanki gashi kin jawo na gano Sam Baki da kyan Hanci Haka Hanci kamar gajeren wando shi yasa aka ce Rumaila babanta Tayo shi yasa ita kyakyawa, Haba Iya ga gashin girarki daya tafi daya tsayi Taya akayi Haka? Iya fuska ta Bata tare da cewa to Kai kyan ne da kai? Dan ka samu ma nace Zan maka kauna yau dama Kai ba Dan goyo bane Kuma wallahi zaka dawo da daddare ne tashi kasan inda dare yayi maka,me shayi yace Alhmdllh na gode Ni Kam na gaji da kaunar Nan gaba daya, Abun hauka ne? yo idan Haka ake kauna har abada ma na Yi ta,ai ko auren bazan Yi ba,kin zaunar Dani Kamar talbijin sai wani fikil fikil kike min da Ido ke ga Abu Kamar an Dan yanka da Reza,da Allah ki samo sabon salo wannan Bai Yi ba,idan an girma Dan Allah Iya asan an girma wannan ai shashanci ne tsohuwa dake me ya rage Miki yanzu,me kike Nema a duniya,da budurwa ce tayi min sai nafi ganin birgewa Amma....Iya Tace to Dan tijara Kai kamar kwallon Mangoro,dan Kauye ai dama Kai Dan gargajiya ne,baka San komai ba sai jahilci,Ni Dana Yi aure har a birni na San takan wayewa,Me shayi yace naji ya fice Yana cewa na tafi gona,Iya tace aikin kenan Dan gona Kawai abinda ka sani kenan ya za a shuka dawa da masara in Allah ya yarda sai sun daina tsada sun karye a kasuwa muga ta tsiya ku Fadi rasha rasha,ai kuwa ba kya Sha Miya da kifi ba,Kuma ba kudin da Zan Baki babu Kuma saki ko Uwata Zaki zaga wallahi Iya kina Nan Dole kici gaba da dafawa yarana tatsotse.
AsmaBaffa
ππππ
DANGIN RABI
ππππ
KARSHEN
FREE PAGE
DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
NA KUDI NE
GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE
ACCOUNT NUMBER
0175487861,ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK
MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER DA ZAKU TURA
08033933642
'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER
+227 90 79 59 39
36-40
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne masu Sharhi na ko wanne Group Ina matukar Godiya,Wanda ban bawa pages ba kuyi min afwa idan kun samu damar siya sai mu hade a paid Groupπ
π
Me shayi ba a Dade ba ya girbe masararsa a gona yaci riba sosai ba karamin kudi ya samu ba,Ya bawa matansa dubu goma goma,zo kaga Murna wajen Iya,Iya ta Irga kudin Nan yafi sau goma tana irgawa tana cewa Alhmdllh ga Allah ya Gama bani arzi ga arzin 'ya'ya ga na kudi,ga yara ga boza wohoho