Showing 39001 words to 42000 words out of 115153 words

Chapter 14 - DANGIN RABI COMPLETE

23 Aug 2025

1521

ba,Muka tako har Gaban Yan Sanda da mutane,Wani Dan Sanda ya daga min ID card yace you are under Arrest, a Gaban Fadila Fu'ad ya tsaya Ina rike a hannunsa yace ke Dan Uwarki wannan ce Rumailan? Fadila tsoron yayanta ya kamata,Mari ya dauke ta da shi yace nace ita ce Rumailan? Fadila ta fashe da kuka da tsoro Tace a'a ba ita bace,Yan Sanda Suka saki Baki suna sallallami,Khaleesat ya murdewa Hannu sosai yace ke wace wannan fadawa Yan Sanda Khaleesat Tace Maryam ce karya muke ba ita ce Rumaila ba Wannan Maryam ce,dama mun tsaneta ne shi yasa muka Mata sharri,Momy tace karya ne Sir,Dan Sanda yace who said Sir? Momy ta daga hannu irin abin kirkin Nan Tace nice,yace You are very stupid kun San karya ne kuka wahalar da Yan sanda,mu abokan Wasan ku ne? Dan Kuna da kudi wlh da a police station ne sai na rafka Miki Mari Nonsense Get Out Yan iskan banza kun Bata Mana lokaci, Fu'ad Yace kaji dai daga bakinsu to ba itace Rumaila ba Rumaila Yar Kano ce kuje can ku nemeta,Kuma wlh kuka Kara zuwa Nan wallahi sai na shigar da ku Kara duk aikinku sai kun rasa Kuna biyewa Mata,Hakuri Suka shiga bashi,ya zaro kudi ya Basu Suka tashi motarsu suna zage zage Suka koma.

Murna ta kamani Ban san ma na nayi tsalle a Gaban Fadila ba nace Fuck you.....Fu'ad sai da yayi Dariya Wai Ni Yar makaranta har nasan Fuck, Umma tana kallon komai,Momy Tace Allah ya Isanki Fadila shege kwarto ta furtawa Fu'ad, Fu'ad Yace rainonki ne tarbiyyar ki ce,Iyyeeee kaiiiii Fu'ad cewar Mama,mota muka shiga ya tafi Dani,Momy Tace ai wlh Bari zamu hada plan dole Nan gaba zamu kawo wasu Kalar Yan Sanda dole fa Yarinyar Nan sai tayi zaman gidan yari,Fadila tana kuka Tace wallahi...kar...kar a barta,Nima wlh tunda ya mare Ni a kanta yanzu na fara sai Naga karshenta,Islam ya furta Dan Allah Wai me tayi muku Haka? Bai dace ba,muna Zaune lafiya Amma akan wata kun lalata zumunci gaba daya,sauran mazan ma Suka ce Bai dace ba.

Ni kuwa yau murna na rasa inda Zan sa kaina,Yana Driving ya juyo ya kalle Ni kadan tare da maida hankalinsa kan tukinsa yace Wai ya naga cikin ki kullum a shafe ne yaki kumbura,nace kaima dai ka fada Kuma watansa yafi biyar ba,irin cikin Nan ne dani me teba kaga kibar da nayi ce ta shanye shi fa shi yasa ai naji dadi kaga na huta idan nayi aure ba Wanda zai San ciki gareni,Baki ya tabe yace uhm ke kika sani,nace Wai me yasa baka soyayya ne ban taba ganin ka Dan ko kalli wata ta birge ka ba,kwantai nayi sai ki Nemo min ai kisa nayi auren dole tunda ke Uwa ta ce,Baki na Bude nace Allah baka Hakuri daga magana,Ameen ya furta yace tunda kika zo gidan Nan kinbi kin Sa min Ido ni Ina Sa Miki Ido Ne? Kiyi rayuwarki nayi tawa aikin banza Ni fa na tsane ki Bari kiji tunda kikai cikin shege ba ruwana da ke,Naji zafin Maganar sa na Danne nace yo Dan ka tsaneni Ni dama cewa nayi ka so ni? Ni Nace sai ka so ni? Cikin waye yayi idan ba Kai ba Malam zaka dinga pretending,Sitiyari ya daka yace ke dama Haka kike da sharri? Ni a Ina muka taba haduwa har nayi Miki ciki? Tsoro ya bani yanda Naga har ya canja Yana huci,ba shiri nace Wasa nake maka,Harara ya balla min yace wlh da a Nan zanyi parking na zaneki a gefen titi,ko na maidawa su Fadila ke su daure ki,shuru nayi ban sake magana ba naga masifa yake ji,Office dinsa Muka je na Sha kallon haduwa Kai fada ma Bata Baki ne,Har wani Palo ne da bangaren wasu kujeru na Alfarma,Sanyi da kamshi ke tashi,maaikatan dage Building din suna Aiki karkashinsa sai kwasar gaisuwa sukeyi,a kujera na zauna Yana ta aikinsa ,Yar wayata na dakko Ina ta Game,1pm yunwa ta kamani dama ban karya ba sai ga Abinci Umma ta Aiko Driver ya kawo a Basket,Ni na fara eba naci na koshi sannan nayi Alwala a toilet dinsa me kyawun gaske,Sallah nayi tare da adduoi na,Yace an tsaida Sallah ne? Tun yaushe naji wuyar duniya ban San Sanda na tsaida ta ba,ya fiye Miki ai,yaushe Jauron naki zai zo zance ne Wai? Yana magana Yana buga Stamp a takardu.
Ai kar yazo ace Ina kwashe kwashe,a'a mene ne ba ruwanki da wani Kawai idan yayi Niyya yazo mana,mamaki ya kamani ya akayi yake so yazo? a jiki na naji Kamar da matsala nace bazai zo ba sai idan naje ganin gida Kauye zamu hadu, Fu'ad da wayo yace to ba Kya sonsa Kawai Amma ai saurayi yazo zance shine magana,nace Watarana zance yazo,Bai sake cewa komai ba Nima haka.

Bayan komai ya lafa ban sake Jin komai ba bana ko fitowa daga part din Umma sai wajen Nene Ina zuwa, Har ciki na ya wuce wata biyar Amma ciki Sam Bai ko dago ba abin mamaki,Ga awo Ina zuwa ance yaro lfy yake, Umma da kanta ta sani a makarantar Boko me tsada ganin Ina da kokari Kuma na iya karatu da Rubutu turancin ne Bai zauna sosai ba sai a hankali,na Kara wani wayewa na goge,gashi Umma sai Kaya take Dinka min,ga Ready made etc,Naila ta shirya ta tafi Kano wurin kanwar Nene zata Dan Huta,Mama Kuma Ana saura kwana Uku Abbi yace ta taho Saudiyya suyi Azumi tare,Su Momy Suka ce Allah kaimu Bayan Sallah kafin su dawo sai dai suga Rumaila a prison,kafin ta tafi Momy,Mama da Fadila sun Kira Abbi sun fada masa komai akan cewar Rumaila Yarinyar Yan fashi ce,sannan Fu'ad shine ya Mata ciki, Abbi dai Bai yarda ba Amma yace bincike Yana da dadi ya fasa zaman Saudiyyan gida zaizo yayi settling komai sabo da Haka Umma ma Bata tafi ba.

Kwana daya tsakani sai ga Abbi ya dawo lokacin Kuma su Momy again sunje sun sanarwa wasu Yan Sandan daban tare da jika su da kudi,a ranar Abbi ya Tara kowa na gidan muka hallara kaf,Abbi ya kalli kowa duk Muna kasa shi kadai ne a kujera a zaune,yace ba sai nayi bayani ba kowa yasan dalilin zuwa na,Fadila ance kece kika San komai,to mene komai din akan Rumaila? Fadila har da mikewa tsaye kamar a makaranta tayi bayanin barazanar da Rumaila tayi,sai Bayan ta Gama kaf Momy itama aka Bata dama ta Mike tayi Karin bayani Tace yau Zan daina boye boye kowa yasan gaskiya,Ni dai na Sha Kama Rumaila a part din Fu'ad,sannan Bayan barinta gidan Nan da wasu lokaci ta fara laulayin ciki,Bayan an Mata test aka tabbatar tana da ciki na wata Uku,idan aka tantance lokaci ya nuna tabbas ba a Kauye tayi ciki ba a Nan gidan ne,Abbi yace waye Hujjar ki? Momy Tace a Kira Baba Jummai,Nan take aka Nemo Baba Jummai,Abbi yace Baba Jummai me kika sani tsakanin Fu'ad da Rumaila,Baba Jummai ta kwashe komai daya faru lokacin da Yan fashi suka zo fashi gidan sannan Tace ta fanshe Ni Kuma nasan fansa ta da tayi dama sun Saba masha'arsu da Fu'ad badan Allah ta fanshe Ni ba,na kalli Baba Jummai nace kiji Tsoron Allah Baba Jummai ki tuna Allah Yana kallonki,Da Ubanki ne yake kallo na,Ni zaki yiwa rashin kunya,Abbi yace Jeki Baba Jummai,Bayan ta tafi ya kalli Momy yace sauran shedunki Zaki kawo min,Nan take Momy ta Kira Wayar Rabi,Bugu daya Rabi ta dauka,Momy ta sa waya a handsFree kowa na ji,Abbi ya karbi Wayar yace Rabi Abbi ne, Nan take ta gaida shi,yace tambaya Zan Miki me kika sani game da cikin Rumaila? Dama can Momy sum Gama hada Baki da su Rabi,ai Rabi Tace Ciki Kam tayi shi Kuma Fu'ad ne yayi Mata ciki,tunda Muka zo gidan Nan kullum sai taje part dinsa tana fakewa da gyara Masa part dinsa,daga baya Kuma har cikin dare sai muga ta sace jiki ta fita cikin talatainin dare,Har binta mukeyi a baya sai muga Fu'ad da Kansa ya Bude Mata kofa ta shige,Watarana har rungumeta ya Sha Yi a Gaban mu,munyi munyi ta daina Mun Mata fada tace ba ruwan mu, Kuma ranar bikin Fadila kowa ya gani a kunna maka video din bikin zaka ganta a saman cinyarsa wannan ita ce sheda babba,.

Abbi ransa ya baci yaji kamshin gaskiya Amma duk da Haka yace a kunna Masa video dama mama ta tana da abinta a waya sai ko ta kunnawa Abbi ya kalli zahiri,kan Abbi ya kulle ya rasa ta ya zai warware abin Nan a sirri ba tare da kowa yaji ba ko ba komai Dan ya rufawa dansa asiri duk da Bai yarda ba Amma ba a shedar mutum,Amma Sam Bai yarda Dansa zai yiwa wata ciki ba musamman Fu'ad,Itama Rumaila Sam baya Jin ma ko a jikinsa zata zama Yarinyar Yan fashi Sam bazai yuwu ba Amma dai duniya ko danka ne ba a shedar sa sai anyi bincike.

Umma Kuka takeyi tun tuni,Abbi yace to duk naji Haka ya Isa,Ke Rumaila tsakaninki da Allah ya abin yake Fu'ad shine ya Miki ciki? Ina Hawaye na tausayawa Umma da shi kanshi Fu'ad a dalili na ake ta Masa sharri Ana Bata Masa suna,da suna zaman su lafiya a dalili na Abu ya lalace,Kawai Nace Abbi ba shi bane,to idan ba shi bane ya zakiyi da Maganar Jummai? Nace wallahi Jummai da kanta ita ta nemi Alfarma akan kar su Bari muyi a gabansu Suka amince Muka Shiga bargo,kayan mu Kawai Muka cire suka karba Dan su tabbatar munyi wani Abu har komai da Mukayi kamar Shirin Film Haka Mukayi, yace naji to Maganar su Rabi fa? Nace Allah shine shaida Bai fi sau Uku ba na taba shiga part dinsa Kuma Ni gyara Masa dakinsa nayi shine har Momy taga na fito daga ciki, Amma wlh in Banda a biki Fu'ad Bai taba rike ko da yatsa na ba,to waye ya Miki cikin kenan? a Nan na rasa me zance Kawai Dan na Kare Fu'ad Nace wani saurayi nane Jauro,Ina Gama fada Abbi yace zauna,Kai Fu'ad fa duk abinda Rumaila ta fada gaskiya ne? Fu'ad Yace a'a Abbi, yasan karya shima zai yiwa Abbinsa Bai San ya sadu da wata mace ba a duniya Kawai yace nine nayi yiwa Rumaila ciki kareni tayi,Abbi ransa ya baci yace Kai Ni Wai ya zanyi ne da wannan kullun masifa haka,Kai Fu'ad idan Rumaila ta Haihu dole sai ka aureta na Gama magana daga yanzu ka sani wallahi sai na Daura maka aure da ita tunda ka amsa laifinka,ka bani kunya banza shashasha kaci sa'a daya ta Umma wallahi da sai na daureka Nasa an maka hukunci me tsanani,Rumaila Ina godiya da karar da kika nuna min da Umma kin San Dan mu ne Amma kika boye gaskiya sabo da kunyar mu na jinjina Miki Allah Kuma ya Miki Albarka ya Kara shiryar mu baki daya.

Momy ba haka suka so ba burinsu a Kori Rumaila ko a kamata sai Tace to Maganar Yan fashin fa?Abbi yace wannan zancen banza ne daga bakin mutanen banza....kafin Abbi ya rufe Baki Yan Sanda masu yawa bataliya Guda sun cika palon tare da Nuna Rumaila,Ogansu yace You are Under Arrest,Rumaila ta Mike tsaye,Abbi zaiyi magana sukace baka da damar magana idan Kuna so ku bi mu station,sai ayi magana Amma ku idan kun yafe Mata mu hukuma dole sai munyi bincike a kanta sosai,idan Bata da laifi zamu sake ta Amma baza mu bada Belin ta ba sai Mun Gama bincike a kanta, Fu'ad ya Mike yace ai ba Haka doka tace ba,Abbi ya kalle ni yace kiyi Hakuri Rumaila za a dinga Kai Miki abinci Ana kula da ke Allah zai isar Miki Kuma Inshaallah zanyi wani Abu,Kawai bin Yan Sanda nayi muka tafi.
Cikin Sel suka sakani tare da kulle Ni Bayan sun karbe wayata da dankunne etc.

Ni kadai a ciki na zauna kamar marainiya tunanin rayuwata ya dawo min na daga kaina sama Hawaye ya shiga sintiri a kumatuna, Fu'ad kuwa Abbi yabi Yana cewa Dan Allah kar a kulle ta ka bada kudi masu yawa a saketa idan kayi magana abin zai fi,Abbi Dan Allah a samo hanya,Abbi yace Fu'ad ka Dame Ni Wai ko dama son Yarinyar kakeyi ko kuwa sha'awarta kake? so kake a fito maka da ita kaci gaba da Yi Mata wayo? Shuru Fu'ad yayi yace Abbi gwara ma ka fito da ita wlh Dani za a kulle a Sel din,Abbi ya zaci Wasa Fu'ad yakeyi yace to ai dole sai anbi a hankali ta karkashin kasa kasan case din babba ne,a Bari suyi bincike Mana ai dole gaskiya zata Yi halinta, Fu'ad Yace Abbi su Momy ne fa za suyi ta Basu kudi Ana azabtar da ita,so kake kafin a Gama bincike Yar mutane ta mutu,Kuma tana da ciki? Abbi Yana sani yace to Ina ruwanka Wai? Fushi Fu'ad yayi Ya koma wajen Umminsa yayi Mata rada a kunne ta Dan murmusa ya tafi,wanka ya dauka cikin wata arniyar Shadda sea blue Yana kamshi yasa Driver ya kaishi police station inda aka kaini,Ina ciki kamar marainiya,Wurin Dpo ya Shiga ya zauna,ya buga ya buga yaki bada Belin Rumaila,Takaici ya kama Fu'ad ya zaro kudi masu yawa ya ajiye masa a saman table ya cire agoginsa me tsada ya Mika musu yace Bude min inda take na Shiga ka hada ka kulle Dani,Dpo kuwa yace Fine ya Kira yaronsa Suka tafi da Fu'ad har cikin Sel,Ina ganinsa farin ciki ya lullube Ni tunani na fitar Dani za ayi sai Kawai naga an bude Masa ya shigo shima an maida kofa an Rufe dani da shi a ciki Dan Sandan Yana cewa Soyayya dadi,Amma fa ka birgeni a kulle budurwarka ka shugo a hada da Kai harda biyan kudi akan kulle ka kaima,to wannan a kanta zaka iya kashe kanka ma.

Duk da Haka naji dadi ko banza Ina ganinsa mantawa nakeyi da damuwa ta,Bai min magana ba nace kaima kamaka sukayi? Ae Kawai yace min,Murmushi nayi nace yunwa nake ji Allah yasa Umma ta kawo Mana Abinci sai kuwa ga Umma da kanta tazo aka fito Dani Kawai Fu'ad Yana ciki,muka gaisa Umma Tace ki Kara Hakuri kinji very soon Zaki fito Abbi zaiyi maganin komai nace Inshaallah na gode Umma,Abinci kala kala aka bani a kwando Umma ta tafi Ni Kuma na shiga da shi ciki sabo da Fu'ad ya biya kudi ba a takura Mana,Sel dinma daga Ni sai shi aka barmu ya biya kudi,Abinci na Bude na ebi yanda zai min,nace Kai fa? Yace sai dare kici naki Kawai,Zama nayi Ina ta ci Yana kallo na,tunani na tafi Hawaye ya zubo min nayi saurin gogewa,Mene na kuka Kuma? Iyata nace Ina Hawaye Ni gwara na tafi kauyenmu,Abincin ya karba tare da daukan spoon din ya ebo abincin yace Ahhh Bude bakin,Murna ta kamani har ban San ma na daina kukan ba nace Da gaske kake Yi? Yace ae kina Bata min lokaci,Nace Dan Mazon Allah fa? Yace Uhmmm Zan fasa,da Sauri na Bude Baki na fararen hakorana Suka bayyana ya zuba min jullof rice din da Naman rago,nace dake hannunka ne sai ya karawaa girkin dadi,yace kaji karyarki ko Ni baza ki yaudareni ba yarinya,Yana ta bani a Baki sai da na cinyes tas Nasha ruwan roba me sanyi,Magriba na Yi,Suka Bude mu Muka Yi Alwala tare da sallah,Har Isha Mukayi Basu ce mu koma ciki ba sai Bayan Isha sannan Muka koma Suka kulle mu,Abincin ya zuba shima zai ci nace kawo Nima na baka a Baki? bana so ya furta yaci gaba da cin abincinsa ya koshi,Kasa kwanciya yayi ba shimfida bare pillow,Kwanciya nayi ya gaji ya kwanta shima tare da Dora kansa a cinya ta Ina daga kwance shuru muka Yi a Haka bacci ya kwashe mu.

Jin Fu'ad ya kwana a police station Abbi da sassafe yabi ta sama manyansu ya kashe case din gaba daya,aka Kira su momy aka ja musu kunne Nan ma gwiwarsu tayi sanyi,Bamu San anyi ba muna kulle sai gani Mukayi Yan Sanda an bude mu Ana ta Bamu Hakuri,na fito nace da karku bude mu Mana wallahi ku gani,wani katon ciki cikin Yan Sanda yace Iyyeee kaji Yar fici har da ke Wato kin Isa ko? Nace ae har nayi yawa,Wayoyinmu da komai namu suka Bamu muka fita Uban Izzar Ana ta takama Yana wani kumbura,Taxi Muka Shiga sai gida.

Bayan komai ya lafa Abbi duk tafiya aikin Hajjin ma fasawa yayi a gida kowa zaiyi Azumi,wannan Azumin shine Azumin da zanyi talatin cif a duniya,tunda aka fara Azumi a garden dukkan Yan gidan suke taruwa kowa da kowa Kuma kowa da carpet dinsu daban,Nan sunyi rukuni can ma Haka,wacce ke da girki itace ke Zama a shimfidar Abbi, Fu'ad kuwa shi kadai ne a carpet dinsa Kato,Yanzu Yan gidan ganin Basu da sauran abin da zasu Yi min sai dai tsangwama da hantara,ko da na fito wajen na nufi carpet din Yan matan tun kafin na karasa Safna da Naila Suka min alama da hannu na koma,Umma tana tare da Abbi,matansa su Momy nasan ma bazan rabe su ba Kawai sai na juya na koma wajen Fu'ad shima Ina tsoro kar ya Kore Ni sai kuwa gashi Bai ce komai ba na zauna kasan kafafunsa.

Zamu fara cin abinci kenan Khaleesat Tace je ki karbo min yaji,to nace na Mike Zan tafi Fu'ad ya daka min tsawa zauna idan ta Matsu taje da kanta,ai kuwa na koma na zauna,Na fara cin abinda nake so a cikin kayan Shan ruwansa kowanne abinda ke so yake ci,idan Ina son wani abin ma wajen Su Islam nake ebowa ba ruwansu Dani har Hira mukeyi da su,a nutse kowa ke ci

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login