Showing 99001 words to 102000 words out of 115153 words

Chapter 34 - DANGIN RABI COMPLETE

23 Aug 2025

1580

tafi, sai kace wasu Yan China a tare suka saki Sanduna a kasa,Yan Sanda sun Kai goma suka fito daga motar su tare da tambaya wannan makaman fa? Momy Tace ba makamai bane makamashi ne, itace ne muka ebo zamuyiwa masu kawo Amarya girki ai baza a bar Baki Haka ba,Dan Sanda ya San karya ne Amma yace Weldone kuje muma Muna jiran abincin idan mun Gama aikin mu sai muci mu tafi,dama Saddeeq yace Kar a musu komai surukansa ne sun ci Darajar Abbi,Ba shiri su Momy suka koma cikin part din Fadila,Mama Tace muyi sauri mu bawa Yan Sandan Nan su ci su tafi muyi aikin mu Kar Abbi ya dawo ya Iske Bama gida,ai Momy suruka ta dauraye tukunya babba ta daura a Gas,su Khaleesat Ana ta yanke yanke Ana Taya Momy,Mama ta wanke nama ta Dora,Ita kuwa Fadila aikin kukan bakin ciki take Yi Kawai,Momy Tace maza ki dinga kuka Gaban Amarya ta Raina ki,Wai Amaryar Yar uban wace ce? a wanne gari take? Fadila Tace ban sani ba wlh ai Baki ga kayan daya zuba Mata ba masu tsada da gani kin San Yar manya ce.

Cikin lokaci kankani su Momy suka zabga Jollof Rice ta Sha nama da kayan Lambu,wata katuwar cooler Suka cika dam,Khaleesat da Faridah Suka dauka tare da kaiwa Yan Sanda a compound,Dariya ce ta Kama Yan Sanda Amma Suka Danne,Ogan ya dakawa Faridah tsawa yace ku shiga palon Amarya ku Kai musu,Haka Suka Shiga palon sai Suka ga Yan Kauye ne gaba Daya,abincin suka ajiye suna buga tsaki,Dangin Amarya suka ce Sannu Dangin Uwar gida mun gode da wannan tabbar da gani mun San Uwar gida zata rike Amanar Amarya,kafin su Rufe Baki sai ga Dangin miji Suma da nasu abincin da ruwa na roba tare da Lemuka na tarbar Baki,sai Guda sukeyi,Farida Tace muje muga wace Amaryar,Dakin Amarya suka shiga,Rabi tana hango su ta shararan mayafinta,ai Kara nannadewa tayi cikin Mayafin ta dukunkune kanta,Suka Yi iya yinsu Amma Rabi Taki yarda su ganta,sai da suka bari Dangin Ango sun taru da mugun yawa Su Kuma su Khaleesat sunki tafiya sai sunga kwaf,Lokacin Rabi ta zare mayafinta ta dage shi sama,Kanwar ango ta saki Guda tare da cewa Allah ya yarda Amaryarmu Yar Fulanin asali Alherin Allah ya Kai Miki babbar Aunty,Salati Khaleesat ta saki,Farida Tace Rabi ce Wai ko Ido nane?Rabi tana Yanga tare da yatsina fuska Tace Allah ya yarda Na Zama matar Saddeequ, Khaleesat Kamar ta zare haka ta fita da gudu lokacin Yan Sanda sun Gama aikinsu sun tafi, Khaleesat tana Haki Tace ku fito yaki za ayi wallahi yau yakin duniya za ayi na biyu Rabi ce Amarya,Fadila Tace me? Rabin Kauye wacce aka ce mun hada dangi da su,Rabin da Saddeeq ya yiwa Fyade ita ce Amarya,Fadila Faduwa tayi kasa a sume,Mama ta Yayyafa Mata ruwa ta farfado,Safna Tace ku zo muje mu hada Mata jini da majina,gaba Daya Suka fito Dan Abin kunya,Dangin miji Dana Amarya suna kallon ikon Allah,Momy ce ta cakumi Wuyan Rabi Amarya ta fesa Mata Maruka biyu,Kanwar Babar Rabi ta Mike tare da fincikar Momy Abinka da karfin mutan Kauye Kan Momy ta Kama tare da gwarata da jikin bango ta shake Mata wuya tana naushinta a ciki,Momy tana ta ihu,Mama ta Kama wata Cikin Dangin Ango Suka rukume da Kokawa Ana ta duro ashariya da zagi Iri iri, Safna Kuwa Saude kawar Amarya tayi kukan Kura ta damki Safna Suka dinga dukan juna,Khaleesat da Farida Suma Dangin Ango Suka kama,gaba Daya dakin casuwa akeyi ba me Jin Kira,Fadila tazo ta kwakushi Amarya suka fada Kan gado,Rabi ta sauka kasa ta daura gyalenta a kugu ta samu Fadila ta kwada ta da kasa,Cikin Dangin Ango wata ta Kira Ango ta sanar masa abinda ke faruwa,shi kanshi ta waya Yana Jin Ihun Mata da Ashariya Ana ta danno ta,Yan Sanda ya turo gidan yace duk su tattara Dangin Fadila su kaisu station,Ai kuwa da Mata Yan Sanda aka zo,Suka dinga kallon abin mamaki,wasu rigar su ta yayyage,wasu ba Dan kwali wasu daurin ya karkace sun hada Zufa sai Haki sukeyi ko wacce taji jiki,Fuskar Momy duk Tasha yakushi raunuka a fuskata ko Ina,Mama kuma kunnenta Daya ya fashe,Farida an Mata kulu a goshi,Fadila Bakinta ya fashe,Safna Lebenta ya kumbura suntum, Khaleesat gefen kafarta ya fashe sabo da an bugata a jikin gadon Amarya,Dangin Ango ma wasu duk sunji rauni,Haka na Amarya ma,Yan Sanda Suka ce Ina Dangin Uwar gida Masu daraja? Su Momy sunyi zaton gaskiya za a Basu harda warewa gefe Daya Suka ce gamu,Yan Sanda Suka ce muje cikin tsawa Har Fadila aka tasa keyarsu,cikin mota aka jefa su suka tafi dasu station,Su Momy suna ta Fargaba da tsoron tsakaninsu da Abbi,Mama Tace Mun Shiga Uku ya zamuyi idan Abbi yaji? Safna Tace mafita Daya ce ku Kira Fu'ad shine kadai zai Rufa Mana asiri ba tare da Abbi ya sani ba ya fitar damu, Khaleesat Tace tab wallahi yanzu ya tsane mu babu Maganar wacce yake ji sai ta matarsa Rumaila ce kadai zata ce yayi kiga yayi Amma Indai ba ita ba wlh bazai Yi ba,Amma kuyi sauri ku kirashi kafin a kaimu sel,Mama Hannu na rawa ta latso number Fu'ad,Yan Sandan Basu kulasu ba sabo da sun San irin kudin Abbi a kasar shi yasa suke Takawa a Sannu.

Fu'ad yayi mamakin ganin Kiran Mama,lokacin Ina kwance a jikinsa a bedroom dina, Wayar ya daga tare da gai da Mama,sabo da yaji tausayinsu Mama ta fashe da kuka tana karantawa Fu'ad komai Bata boye Masa ba har auren Rabi, Fu'ad yayi mamakin Rabi Amma a ransa Allah ya Kara yayi Kuma shi Rabi ta birge shi wlh,ta nuna wayewa tunda ya Mata Fyade dama tunda da aure tsakaninsu ta kyauta ta yiwa kanta gata,a fili yace Gaskiya kunfi karfi na,abinda kuka Yi yafi karfi na,Kun San Ashe Ina da amfani a wajenku? Har Kuna da bakin neman Alfarma a wajena? Wacce kiyayya ce Baku nuna min ba,ba sharrin da Baku Yi min ba,nayi cikin shege kuka Bata min suna a wurin dangi da mutane,gulma babu wacce bakuyi ba,tarko ba Wanda Baku Dana min ba Ni da Umma sai yanzu Ashe Ina da amfani,Ni da nake Dan Iska lalatacce me Zan iya Yi muku,Dan Iska me zai Iya,ku yanzu Rabi da ita kuke fada? Rabi kawar gulmar ku,itace fa ke Nemo muku Gulma Kuna murna Kuna kaunarta,yanzu Dan ta auri Mijin Fadila ai sai kuyi murna tunda Kuna sonta,Bai kamata kuyiwa Rabin taku Haka ba,Sannan Mijin Fadila shi ya lalatata ya Mata Fyade Dan ya aure ta sai kuji haushi,Wato kin Fi so ya dinga lalata Yaran mutane akan yayi aure? Idan za a daure ku daurin Rai da Rai Ni Fu'ad bazan taba fitar da ku ba,ku nemi yayanku maza ai Kuna da su Kuma Allah ya Baku ko ku sanarwa mijinku Amma ba Ni ba,Mama Tace Dan Alla...kit Fu'ad ya datse wayarsa.

Kallonsa Nayi Ina Wasa da sumarsa Jin Yan Uwansa ne ban ce komai ba,Kallo na yayi yace Baki tambayeni su waye ba?nace naji matsalar family ce me zai sa na shiga,okay nufinki Bamu Zama daya ba? Abinda ya shafeni Bai shafe ki ba? Ai ba a shiga tsakanin Yan Uwa,Cizo na yayi kadan a kunne na saki Kara,Yace kawarki Rabi tayi aure,Nace wow Haka bakatatan? Yace Mijin Fadila ta aure,Na kyalkyale da Dariya nace Alhmdllh Allah na gode maka Yan Iska marasa mutunci gwara da ta musu Haka,sunje sunyi dambe da Dangin Amarya an kwashe su zuwa police station,Mikewa Nayi na dinga taka rawa Ina kida da Baki na ganji...gan....ganji...gan.... Fu'ad Yana ta Dariya yace to muguwa,nace tashi da Allah ka kaini gidan bikin Nan daga Nan mu biya ta police station nayiwa su Momy jaje Allah kiyaye gaba, Fu'ad yace bazan je ba,nace Dan Allah ka tashi mu shirya,Rokonsa na dinga Yi yace to Amma idan mun dawo Sai nayi Second Round nace har Third ma ba damuwa.
Wanka Mukayi tare ya shiryawa Cikin wata Danyar shadda peach,Ni kuwa Lace nasha me tsadar gaske Milk and Brown,takalmina me tsini da jakata da Mayafi duka milk nayi kyau, harda saka Glass brown me shegen kyau na zuba kyau.

Fu'ad Yana Bina da mayen kallo yace dole ki mallake Ni,shi yasa Duk abinda kika ce bana musu,nace gashi zaka kaini nayi gulma,idan ba ke ba wa ya Isa yasa naje gidan wata Rabi,Muna mota Muna Hira Yana Driving ya kaini gidan Rabi yace kiyi sauri 10mnt na Baki,shiga nayi Ina Taku dai dai,Me gadi ya nuna min bangaren Amarya,na shiga,su Saude sunyi mamakin ganina,sai wani Sannu da zuwa suke min,dama Dangin Amarya sun Sanni,kauyenmu Daya sai kallo na sukeyi sunga na Zama Hajiyar birni, gaisawa Mukayi Ina musu Allah Sanya Alkhairi,Naga wasu duk da rauni a fuskarsu,Dangin Ango kuwa Yan Birni tambaya sukeyi wannan Yar gidan wannne hamshaki ce Haka? Aka ce ai matar Fu'ad ce yayan Uwar gida,sai yabo na sukeyi Yan matan cewa suke kinyi kyau Ina cewa na gode,kowa cewa yake gaskiya tana da kyau Allah yayi Halitta,ga Miji kyau matar kyau za a ga Yara masu kyau,Rabi Algunguma harda rike Hannu na Tace Amaryar Fu'ad Ashe Zaki zo min?gani Kuma na furta Tace na gode Rumaila Dan Allah kiyi hakuri,Ido na kyafta Mata nace Yi Shuru Ni bana rike mutum,abinci aka kawo min Dangin Ango suna ta ji Dani Kamar sun Sanni,15mnt Fu'ad ya dinga Kiran wayana, Sallama na musu nace Oga Yana jira,Hajara ce ta rakoni da Saude,suna ta bani labarin fada Ina ta Shan Dariya har mota,Saude Tace Gaskiya na tausayawa Safna Kinga wata hambara da na Mata a makoshi saura kadan ta Suma Muna ta dariya,suna gaida Fu'ad muka Yi Sallama sai police station.

Saddeeq kuwa tuni ya sanarwa Abbi komai a waya, Fu'ad Abbi ya Kira yace Kar ya sake yayi Bail nasu ko uban waye yazo sai idan yazo da Kansa,Suna Sel a tare gaba dayansu sunyi jungum jungum, Fu'ad ya nemi Alfarma a barmu muje Kofar Sel din mu gansu muna daga waje suna daga ciki,Kamshin mu Suka ji Basu San waye ba da sauri Suka Mike suna ganin Fu'ad rike da Hannu na Momy Tace Alhmdllh Ni San Fu'ad me tausayi ne bazai Bamu kunya ba,Dan ma Yana tare da waccen shegiyar me bakar kafa anzo birni an waye shegiya sai kiba takeyi tana Kara kyau duk ta tsafe Fu'ad ko Ina zai je sai da ita,shima shashasha ne yaushe zai biyewa wannan Yar talakawan cewar Mama,Safna da karfi Tace to Yan Sanda Dan Ubanku sai kuzo ku fitar damu,Wani Dan Sanda yace zaku ci Ubanku Bari bakin su tafi,Khaleesat Tace Yan wahala matsiyata Kun San ko mu su waye Bari mu fita sai Mun sa an Kore ku a Aiki dan Me cin babarku ta furta da Muryar Yan jagaliya wai ita tsagera yanda tsageru ke yiwa yansanda idan an Kama su.

Muna karasawa Mama Tace Fu'ad Sannu da zuwa, Fu'ad har da rusunawa ya gaida su sabo da ya sa musu Rai,Ni kuwa cewa nayi Ashe Kuma Haka Abu ya faru? Kai Abu baiyi Dadi ba,yanzu Babyna ya kaini gidan bikin naji abinda ya faru,Bai kamata ba ai Allah Yana tare da masu Hakuri, Haba Fadila da hankalinki kina Uwar gida kin zubar da mutuncinki,Na nuna Momy nace ke Kuma gododo Uwar Fadila ace anyi doke doke da ke Haba Kamar zamanin jahiliyar farko,Haba Bai Dace ba Mama a dinga Aiki da hankali,Rabin ku ce fa,Yar Uwarki
U,me dakko muku rahoto,Rabi ta bangarenku,wlh Kun bani kunya Rabi da kuka ce Yar Kauye,Bata ishe ku kallo ba Yau shine ta tsone muku Ido har da jiwa juna rauni Haka akan Rabi Yar yarinya ta Kauye wacce Bata waye ba Yar talakawa,Ina birnin naku? Ina kudin da kuke takama da shi?me gulmar Rabi ta Kara muku?Baki suka Bude suna kallo na,Momy Tace Dan Ubanki da ke muka Yi ? Ina ruwanki munafuka,ki Bari muyi magana da Danmu, Fu'ad yace lallai bakuyi nadama ba,Baku Sha dauri me kyau ba,Ku tunanunku fitar daku zanyi? Ai Abbi ne ya turo Ni Nace lallai a Kara tsananta muku dauri,Sanda kuka yi nadama sai a fitar daku,kuka su Khaleesat Suka saki Tace wlh munyi nadama Dan Allah Yaya ka taimaka,Dariya nayi nace Sajan....Dan Sanda yazo da Sauri,kudi na zaro masu yawa a jakata,tunaninsu fitar da su za ayi har sun fara murna,Dan Sandan na mikawa nace duk wacce ta fada muku bakar magana ku tura Yar Sanda ta chasa ta,Jiki na rawa ya karba Yana cewa angama, Fu'ad yace Uwar gida ta Gama magana,da ace Rumaila Tace na fidda ku da wallahi yanzu zansa a fidda ku Kuma na Bawa Abbi Hakuri ya kyaleku Amma Tace a'a,muje ke ya juyo tare da rike Hannuna muka tafi,Ina Jin Khaleesat tana cewa Dan Allah Rumaila ko Albarkacin Wayar Dana koya muku Sanda kuka zo daga Kauye,ko kulata banyi ba musamman idan na tuna wulakancin da suka dinga min da zagi,da abinda Suka yiwa su Iya.

Sai washe gari sannan Dangin Amarya Suka koma Kauye lafiya,Dangin Ango ne Suka Kara gyara ko Ina na gidan sai dare suka tafi,10pm Ango ya shigo,bata ji wani dar ba sabo da ya rigada ya mata Fyade tun farko ta Gama Shan azabar ta,Kaji ya Bude Musu da kayan Sha,Rabi ta cikin Mayafinta sai kyallo Ido daya takeyi waje tana kallon kaji wani farin ciki ya kamata yau zata ci dadi Haka abinka da ba a saba ba,Mayafin ya cire Mata Yana kallon Amaryarsa cike da farin ciki da kauna,daukanta yayi ya zaunar da ita a carpet Suka sa Naman a tsakiya Rabi sai satar kallon Kaji takeyi ta Matsu ma ya fara Bata taji irinsu taga sai wani maiko sukeyi sun Sha Mai, Bismillah ya Furta Rabi tayi Bismillah Amma kunya ta hanata ci,shi ya ballo Cinya Guda da Kansa ya bawa Rabi a Baki ta kafa Mata hakora tare da yaga,tana ci wani Dadi taji har kwakwalwarta,Ya Bata na biyu tana ci Tace Wai Gurguwa ce Kazar? Yace ban Gane Gurguwa ba? Tace Kajin gidan gona Wanda ake kiwatawa na bature Wanda ake cewa Brolas zaka ga idan Suka girma da yawa kasa tafiya sukeyi sabo da kiba wasu har karyewa sukeyi sabo da kiba tasa sunyi nauyi da yawa ai su ake cewa Gurguwar kaza, Saddeeq Dariya ya dinga Yi yace lallai kinji dadin Kazar Nan harda Santi,Rabi tana boye fuska Tace ai Ni dai ba Santi nake Yi ba Allah,yace sabo da Allah Naga Abu a gashe Ina Zan tantance Gurguwa ce ko me kafa? Rabi Tace gaskiya ka tambayo min me gasawar Nan.
Suna ci Rabi Tace Nan gaba idan Allah ya hore maka Dan Allah ka Bude min wajen kiwon kaji gidan gona Ina so na dinga kiwatawa kaga mun huta idan zanyi Miya Watarana Kawai sai mu kamo daya na dannewa shegiya wuya na yankata mu jefa a Miya, Saddeeq Yana ta cin dariyar Santin Rabi yace to Princess za a bude Miki Inshaallah,Rabi Tace na gode Allah Kara budi Amma karka Bude min a garinmu Yan Uwa su yo min caaaa kowa yaji kwadayi yace Rabi Dan Allah Gurguwa Daya, Saddeeq yace to a Nan za a bude Gina miki kusa kusa Tace to.

Cike da nishadi Suka Gama ya Bata Yogourt tana Sha Tace an Dade Ana cutar mu Muna can kauye,Anya wannan da nonon Saniya akayi? Saddeeq yace Rabiat da bakya zuwa Nan garin ban San ya zakiyi ba ma,Dariya tayi Tace to ai abin ne Ni naka na musamman ne ko Dan Ni Amarya ce ne? Saddeeq yace ai sai abinda kike so Rabi kiyi ta Addua Allah yaci gaba da Buda Mana Zaki Zama Kamar kawarki kema Rumailan Fu'ad Rabi Tace to ai zanje na Bata Hakuri Watarana tunda ka min fadan Nan abinda nayi naji nasihar ka na canja Hali na, Saddeeq yace yawwa shi yasa kaddara ta fada Mana na Miki Fyade hakkin Rumaila ne zamu je tare Watarana ki Bata Hakuri,Rabi Tace to na gode Nima da kayi min nasiha,duk abinda kaga nayi ba daidai ba ka dinga sani a Hanya kaji yace to Rabina,Wanka tayi sosai da Brush,Ta sa kayan baccin da Kanwar ango ta zabo Mata gaba Daya tsirara take,Rabi kunya tasa taki dawowa dakin Saddeeq,sai da ya gaji yaje ya riko Hannunta ya dawo da ita dakinsa Dake part dinta,Hijab da zani ta daura ya jasu Sallah Suka idar tare da adduoi,Sannan ya dauki Rabi Kamar tsinke yayi saman Bed da ita,yace ya naji kinyi Shuru gimbiyata? Rabi Tace tausayin kaina nakeji,murmushi yayi yace Haba a hankali Zan bi Dake,Rabi Tace to Ni lashe lashen Nan naka ne yake tsuma Ni,Rumaila Tace Wai kace wa Fadila Bata lasar maka kunne? Saddeeq ya dinga dariya kamar me, yace wannan Rumaila kwai Yar tsegumi a Ina taji? Bari kiji me nake nufi,Nan ya fara Wasa da Harshensa a cikin kunnen Rabi salo salo,Rabi Tace wayyo naji hankali na zai gudu wayyoo....kamar ana shawagi Dani a sararin samaniya....Idonta yayi luuuuu ya lumshe Rabi Tace ko Azara'ilu ya Hauro katuwar katangar Nan takane? Saddeeq ko jinta bayayi,Rabi ya zarewa kayanta,Yace duk abinda nake Miki kiyi min kinji? Rabi Tace yo Kai kana da nonon da Zan taba maka ne? Ni kana ta shashafe Nawa Kai baka da shi wannan ai cin zali ne sabo da Allah fa, Saddeeq ko Bai so Bai San Sanda yake kwasar Dariya ba,yace ae naji kiyi min Haka,Rabi ta kumbura Baki Tace Allah Ni bazan taba fata ba,Ni Nawa ai me laushi ne da girma Kai fa,Kissing din Rabi Yake Yi sosai.

Rabi tun Bata tayashi Tace Kai kaji Abu Ina raina shi Ashe Dadi ake ji,Bata ma San ta fara Taya Angon nata ba,Tace kace nayi duk abinda kake min na maka Irinsa ko? Muryar Saddeeq na rawa Yace Yeah,Rabi Tace ya naji muryarka Kamar an kunna tsohuwar Radio Tasha tana gocewa?

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login