Showing 63001 words to 66000 words out of 133505 words
karba ba,Seraline tace nidai zanje ko Dan show ko banza nayi pics na dinga dorawa a status Nima a San na Zama shegiya,nace to me Zaki Kara? tace Yan matan gidan zan siyawa kayan kwalliya su jambaki da powder masu araha dai da lipgloss Suma suyi kyau,Haka Saratu ta jibgi kayan kwalliya sosai harda su ribbom da yawan gaske ta siyawa Yan Yara kayan Wasa iri iri sannan Muka koma hotel kayanmu suna mota,yau ma tare da Alhajinta ta kwana suna watsewa.
Washe gari 9pm haka muka je har daya daga cikin gidan marayu,Wanda ma'aikatan ciki ogogin basu sanni ba sabo da akwai wani Wanda shugaban gidan ne suke zuwa ganin Ina lafiya a gidan Dagaci,Muna zuwa aka raka mu inda mutanen suke yaran tsuntuwa duk dama kusan sune a gidan marayu abin tausayi Muna zuwa aka Fara bude Mana wani daki guda katon hole gaba Daya jarirai ne a ciki sabuwar haihuwa da masu kula da su,wani dakin kuma yarane Yan shekara daya zuwa biyu,wani Kuma daga Yan shekara uku zuwa biyar,wani Kuma daga biyar zuwa bakwai,daga takwas zuwa goma Sha,a Haka har Muka je dakin Yan Mata,ga bangaren samari da makarantunsu da Kuma filin wasanni da inda Kawai sana'oin Hannu ake koya musu,yaran Kuma da Basu Isa school ba sai kayan wasanni aka zube musu a dakin suna ta fama gasu nan cikin wahala duk suturar arziki Basu samu,a Raina nace bayin Allah mu dinga kaiwa na gidan marayu agaji suna bukatar taimako wasu sutura ta gagare su wasu kayansu duk sun yayyage an musu maho a agaza masu shi ba sai me kudi ba har kwance kaiwa akeyi,Kayan da Muka kawo Muka damka musu ,sannan naje na dauki wasu yaran Yan dagwai dagwai Ina musu Wasa hawaye Yana zubo min a kumatuna sabo da tausayi lallai Allah ya min niima da ba a gidan na taso ba haka Muka fito jikinmu a sanyaye amma Muna shiga mota muka saki kidanmu na Yan Nija Malam tuni mun manta Muka wuce can kudu.
Sai tsakar dare na sauke Sera a gidanmu na karuwai sannan na koma gidana,Ina zuwa nayi parking na fito Ina dagowa nayi Ido hudu da Nawwar da Baba kulu a tsaye, tuni jikina ya dauki rawa dan bala'in Nawwar har tsakar dare yana jirana hankalinsa tashe ashe ya dawo ranar,Baba kulu tace Sannu da dawowa ke Kuwa Kika barni a gida baki fadamin tafiyar kwana zakiyiba yau kwananki biyu bakya gida Kawai kin bani kudin cefane ai kya fada min sabo da rayuwa,ga Alhaji tun yamma ya dawo na fada Masa ban San inda kike ba ya zauna ko nan da can bai fita ba sai dazu yaje gida ya dawo gashi har 3am bai tafi ba yace bazai tafi ba ashe kina tafe, nidai cewa nayi kawayenki ne Suka jajibeki kuka fita tunda da wannan me tsayin kuka fita,ran Nawwar ya baci sosai kamar an Aiko Masa da mutuwa jikinsa har rawa yake,kamanninsa Suka sauya Idonsa yayi wani ja,jikina rawa yake sosai a kasa na tsuguna nayi Kneel down na fara magana Ina yarfe Hannu nace bazan sake ba na tuba ka yafe min,gabana ya tako a fusace Yana huci yace gidan ubanwa Kika je Yana karaji,mikewa nayi nace wallahi Allah kauyen mu naje na rantse na fara ja da baya na take da gudu na bude gate zan fita ya riko rigata na kwala ihu tare da furta na shiga uku kayi min rai, ai Kuwa ya jawoni ta karfi na Fadi a kasa a haka ya jawoni kiiiiiiii har daki,Baba kulu tace baki kyauta ba ki jefa kanki a masifa kina biyewa karuwai,ai Kuwa har dakina ya jefani ya shigo waya ya jawo na tsure nayi tsalle na rungume shi,ya fisgewa amma naki yarda kuka na saki Ina cewa ka yarda dani wallahi da nayi wani abu Zan fada maka,ban taba munafuntarka ba karka manta a inda ka dakko ni na yarda na zauna da Kai bana fita ko Ina ka bari na maka bayani please,ka nutsu bazan Yi abinda baka so ba nasan abinda kake tunani ba haka bane,Ina kirjinsa na Fara Masa magana a kunne nace calm down,na sake rungume shi,abinka da shedan sai yaji wani sanyi a ransa tunda na rungume shi da kalamai na sai suka sanyaya masa jiki,gashi ji yake tsigar jikinsa tana tashi yarrrrr.....wani irin yanayi ya tsinci Kansa na musamman,yaji baya son barin jikina shi yasa ya kasa janyewa,Mu Kuwa Yan tasha dagowa nayi Ina kallonsa a hankali Idonsa ya dawo normal Ido Muka hada ya janye idonsa,nace kalleni Ina Murmushi, uhmm kaji fa Yan bariki mune mazajen,na sake cewa kalleni Sweety kallona yayi kadan a hankali na dinga matsawa da fuskata saitin tasa har na dora lips dina a saman tattausan jajayen lips dinsa nace I'm sorry,ai Maganar da nayi itace ta dawo da shi hayyacinsa samu yayi ya hankadaki saman bed na fada sai da na saki Kara,da yatsa ya nuna ni na fada Miki ba Dan Iska bane ki kiyayeni duk ranar da Kika sake taba min jiki sai Kinga me Zan miki idiot ya fice,Baba kulu tana jira taji duka sai taji luf bai fito ba tace iyyeee bariki shima na layinsu ne ai sai ta koma dakinta abinta tace su karata na daina shiga lamarinsu.
Washe gari wata tafiyar ta taso Masa zuwa Scotland,har gida yazo Yana hararata ya min sallama har yanzu Fushi yake Dani Wai na tsotsar Masa baki abinda Kawai lips Dina na Dora a nasa ba abinda na Masa Wai na shafa masa bakina da nake wa wasu mazan kiss da shi,amma Kuma ya kasa manta abin sai tunani yake da dadinsa yasan ma kiss dani zaiyi dadi,tunda ya tafi bai kirani ba amma Sabreen kullum sai ya nemeta babu fashi
Sai da ya kusa dawowa sannan ya kirani a waya,Ina ganin number waje nasan shine ko dagawa banyi ba ni sai yanzu zai kirani sabo da raini wancan tafiyar ma haka yaki kirana amma ai in matarsa ce nasan zai kirata,Kira ya sake yi naki dagawa har ta tsinke,Tsaki ya ja tare da jefar da Wayar a saman bed dinsa,Bai sake Kira ba sai dare Ina jinta tana ringing naki dagawa,washe gari da safe ma haka a daki ma na bar Wayar Kan gado,Khaleel ya Kira lokacin Yana bacci matarsa Sufia ta Mika masa wayar tace Nawwar ne,dagawa yayi hello,Dan Allah Malam ka tashi kaje min gidan Yarinyar nan ka gani lafiya take,Sabreen ko wa? Sabreen din wa Malam Rabiah fa na kirata tun jiya taki dagawa Ina Jin ba lafiya ba kaje please ka min recording maganarta ka tura min ta WhatsApp,Khaleel yace kasan Allah Nawwar ka fada so,Dan ubanka sone ya kamaka tun wuri ka aureta Kar lokaci ya kure ma,Tsaki yaja yace shi yasa ni bana son harka da Kai ka fiye soki burutsu,to Makkah fa da ka tafi cewa kayi sabo da ita da Mami zaka je kayi musu addua, yace baza ka gane ba ni yanzu ai 'Yata ce,hhhhh wannan wlh ko a auren Kauye baka Isa ka haifi kamarta ba cewar Khaleel,Nawwar yace naji Zan biya Mata aikin hajji ma taje tayiwa kanta Addua ko ta samu ta daina abinda take Yi, sai na dan taimaketa na aureta kaga ai tayi dacen miji,Hmmm kawai Khaleel yace sannan ya furta bari naje ya zanyi
Da sassafen sai naji knocking na bude kofar Khaleel na gani ya kalleni sosai rigar bacci ce a jikina amma doguwa ce me gajeren hannu pink,Sannu da zuwa shigo na bashi hanya,ya shigo ya zauna na gaisar da shi ya amsa da fara'a yace dama Wai lafiya kike Nawwar Yana ta Kira Wai baki daga ba shine yace nazo na gani ya kike sai na fada Masa,dariya nayi nace kace lafiya lau nake kuma Ina ganin Kiran tunda ya tafi sabo da Allah bai kirani ba sai yanzu yasan da zamana,nace ya barni nayi tafiya ta ya kamani ya kankame ni ya makale yaki sakina sannan yayi tafiya ko ya kirani yace ya ji lafiya ko ba komai na samu number dinsa na dinga kiransa amma bawan Allah nan yayi mursisi yayi Shuru idan matarsa ce ai ya kirata ni kuwa ko oho dan dai Kawai Yana da kirki ne,Khaleel yace to kiyi hakuri dai ai kin San da dalili, ki Masa uzuri baki ga shi ya turo ni ba na gani lafiya,nace Allah sarki Kai ka mori aboki abinda yake yi Allah ne kadai zai biya shi,mutumin kirki Allah ya amsa Masa bukatunsa kace Ina gaishe shi kuma kace na Aiko Masa da kiss a kumatu da lips din kace ga kiss dina na cillo masaMmuahhh,Khaleel ya dinga dariya yace to zai ji bata San recording Nawwar yace yayi Masa,kafin ya bar gidan ya turawa Nawwar ta WhatsApp sannan ya Mata sallama ya bar gida Yana mamakin kyau irin na Rabiah,Nawwar Kuwa Yana online yaga Khaleel ya turo Masa recording,ya kunna Yana Jin abinda nake cewa Murmushi yayi kawai me hade da dariya yace Yarinyar Bata ji badan halinta ba na karbi kiss din dai, ya shiga harkarsa.
Sai dare ya sake kirana na kwanta kenan ya Kira kasa kin dagawa nayi Kawai na daga, dagawa ta ke da wuya ya balbaleni da masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba,sai da ya gama akan naki daga waya Wai na Raina shi,nace to kayi hakuri baza a sake ba,da yamma kina Ina sai Kira nake,tsokanarsa nayi nace Allah sarki ka tambayi Baba Kulu Wani ne yazo wajena zance wai tsakani da Allah zai aureni a nan layin yake, Nawwar yace sai me ya ja tsaki karki sake fada min wannan zancen banzan haka ya ja tsaki ya kashe wayar, dariya na dinga yi,shi kuwa a can kasa bacci yayi yace to waye wannan wai babu wani mutumin kirki Wai da aure yake sonta Naga uban da zaizo zancen,nan take ya makawa secuties waya ya turo su gidan da yawansu sai gani nayi ana gadin ko Ina ba shiga ba fita bamu San dalili ba.
Masu Sharhi Ina godiya matuka.
Masu bukatar sauraren wasu Novels Dina Audio ku duba S ZARIA TV a YouTube channel dinta.
AsmaBaffa
08061929616
[7/22, 11:38 PM] AsmaBaffa: 🌼'YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE
56-60
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA
Page naku ne
Khadija Dandume
Mrs Mukhtar
Maman Afrah Ik
Fairdausi m Sani oum Meenal
Mrs Aminullah
A'eesha
Aisha S Maibankeey
Mom Islam
Khadeeja Sageer(Umee)
Gaisuwa gareki
Aida Maman Tasnim
Anga rida ridan yan Mata ai ni yarinya nake tashi cikinsu,damasu Dj dinmu Muka dira speakers manya manya sun Kai goma Sha biyu kida suke badawa kamar zasu fasa gari,Inna har Yan matan kauyen ta rabawa alawa, dama mu mun Saba ba abinda ya dame mu da Kauye katon dakin da Inna ta gyara ta bamu Muka baje dayan dakin Kuma kayanmu Muka ajiye,sai da Muka tsara komai akan ba shaye shaye duk me Shan wani abu tayi hakuri zuwa kwana daya, Yan matan Kauye kasa zuwa cikinmu suka Yi dama Yara ne gidan Dagaci ne Kawai da Mairo ita Kuma Bata zo ba, komai mun siya na abinci, tun kafin muzo na turawa Bala kudin ya siyo ya Kai gidan Inna,Wani abin Kuma da abinmu Muka zo,amma Muna zuwa Inna da matar Jangudo an dafa Mana shinkafa da miyar,salat Kawai Muka yanka Muka ci Muka barta ga lemukan biki Muna ta sha,akwai abincin Kuma da Muka bayar a cikin birnin Kano za ayi Mana fried rice sai waina da miya,alala,da tuwon shinkafa miyar Agushi har na angwaye su fried rice ce da pepper chicken sai waina da miya, har fura mun bada ayi ta Yan gayu munyi order duk kudin Nawwar ne Wanda ko waya bamu yi sai da dalili,Yara sun zo gidan Inna sun tsaya Mana a Kai suna kallo sabo da Muna zuwa duk kana nan Kaya Muka saka a jikinmu ko wacce sura a bankade wani yaro ne zai Kai 13yrs ya tsurawa Wise Ido sanye da half vest da dan guntun wando gashin nan yaji gyara gata itama fara Kuma ta Kara da Mai tayi Kal Kal,wise ta kalli yaron ta Mika Hannu wuf ta kamo shi tace Dan ubanka zo na baka nono ka sha,ihu ya saka zaiyi kuka yana wutsil wutsil tace ai sai ka Sha nono shegen yaro ka tsura min ido,zuwa nayi Ina dariya na kwace shi ya fice da gudu, Star tace gobe fa sai an kawo Mana motoci biyu sabo da zirga zirga,nace karku damu za a kawo ai na fadawa Ango yace Already an kawo motocin ma har Wanda zasu kwaso angwaye daga airport Kun San Yana da mutane a nan, Inna kuwa da makwafta suna ta Shirin abincin da zasu bawa Yan Kauye mutan kauyen, Bluetooth speaker muka kunna a gidan muna ta rawa,sai dare bayan munyi sallar Isha nace wai Mandula baza ta zo bane,kin manta a cikin Kano fa gidan kawarta ta zauna itace zata taho da abincin idan an hada,sai Kuma me Make up da zata taho da ita,nace ai sai ku fada min yanzu ita za a kaiwa mota? Sera tace ae mana nace ai to an huta ma mota daya tayi ko wacce zamuyi amfani da ita? Wise tace yeah ku tashi mu dan zaga garin Mana mu gani tunda gobe ba time,wasu Hijab Muka saka wasu abaya Muka fito kamar mutanen kirki dake da wutar nepa ko Ina haske ana ta hada hada a kauyen mun fito duk inda Muka yi sai kallo harrrrrr samari ana ta cacar baki,wani me tsaurin Ido Sani ya turo yaro wai Ya nuna Yar Zabil tazo,nace inji wa? yace Sani na gidan Sale me Alewa dariya nayi nace sisi baza ki samu ba ubansa ma Alawar Dinya Madi yake siyarwa,Yar Zabil tace kut ni a kauyen nan ai duk sai dai na aike su ta ja tsaki Kai muje,Sera tace Sani guy na taba tsinka Masa Mari tana Dariya.
Gidan Dagaci Muka shiga nace a nan na girma,Dagaci suna tsakar gida suna gulmata na kawo karuwai, sai gamu da yawan mu mun shigo dama tsokana nazo ba gaishe su nazo Yi ba,Dagaci Yana ganinmu ya mike da masifa ku fitar min a gida Kar ku lalata min tarbiyyar iyali ku tafi can gayyar tsiya,Star ce ta kalle shi da hularsa tasa Hannu tayi fatali da hular Dagaci tayi fatali da ita na sa kafa na take hular, tace Kai dalla rufe mana baki,nace tunda ka Mana you must collect nayiwa kirjin Dagaci kwass na rankwashi kirjinsa ,yace kuyi abinda zakuyi shegu tambadaddu sai nasa hukuma ta Kamaku ,Malika ta furta da kuwa ka taro bala'i wallahi da sai na sa an kwace sarautarka karka cika Mana baki muke da masu fada a kasar nan,nace ni da kaina sai nayi maganinsa mark my words,Mairo ce ta mike tace iyyeee anje birni anyi clean an tsinci turanci a kwalta to wallahi ke baki Isa ba ke din banza banzaye karuwai an zo ana mana burg....Mari taji tas tas tas har uku tuni Wise ta Gama da ita,hawaye ta saki da kuka, Star tace kina sake magana wallahi sai mun tara Miki gajiya baki san waye mu ba,ta nuna Dagaci tace Kai Kuma Muna nan zuwa kanka yanzu gidanka Muka zo amma nan gaba zaka ji mu karka manta bama gaggawar daukan fansa, Azzalumi an baka amanar marainiya kaci tunda kaci amanar Rabiah you must see shege, Gwaggo ce ta taso da bala'i Yar Zabil taci kwalarta ta hankadeta ta fada Kan Aunty Amarya tace yanzu biki Muka zo zamu dawo Kun tabo bala'i sai mun hanaka Shan ruwa a garin nan wlh wannan Dagacin sai an kwace zaka ga masifa,na kalli Gwaggo na furta idan Gaji ta dawo kuce ta shirya nace muje dan Allah dama kawoku nayi mu isar da sako,Wise ta dinga foli foli da tukane da kwanika a gidan da kafa,na nuna Dagaci nace dan gyatimarka akan na hanaka local government dina cikin dare kake zuwa gabanka a dage ya kalli samaniya kana rokata na baka hadin Kai shine kuka min sharri kuka bata min suna wallahi Allah sai ya bimin hakkina Kuma sai na ci takashin uwarku Dan me dirkawa uwarka ciki Ina bala'i harda hawaye naci gaba me chemist din da kuka sa ya rubuta Ina da ciki sai Kun karyata kanku na karasa Gaban Gwaggo da Amarya nace sai kun bada sheda a gaban kowa kafin ku bayar a lahira,Aunty Amarya na tugewa dankwali na wullar da shi nace ubanki ne yayi min cikin Yar gidan Ubale me tsire,ubanki Ubale shine ya min cikin? Aunty Amarya ta mike ita ga marar kunya nace wallahi kina magana sai nayi tsirara naci ubanki a nan sai na miki tsirara,komawa tayi baya tayi mukus,Gwaggo ta mike ta cakumoni nace ku barni da ita na dauki Gwaggo dama ba kiba nayi sama da ita na watsota waje Dagaci ya kasa motsi bai taba ganin jaraba irin wannan ba,Mero ta fito tana zagina Sera ta kamata ta dinga jibgarta Kamar ta samu jaka,Gwaggo ta mike ta rukuma kokawa dani ita ga Yar bala'i tana cewa Yar tsuntuwa Yar cikin Shege
Dama munzo da Santana mutane da makwafta an cika ana kallo,Santana ya falfalo Yana ihu ya dora Hannu a ka Yana cewa na shiga Uku za a kashe Mana Yar uwa Yana gyara daurin zaninsa a saman Jallabiya ya kalli Su Wise yace kun tsaya za a kashe Mana Yar uwa ya dakko dutse wani Dan karami Yana yarfe Hannu Yana furta wash nauyi ya jefawa Gwaggo a hankali ya rike hannunsa da sauri Yana fari Yana karairaya ya furta na Shiga Uku zata min illa hannuna wooo, su Wise ne Suka hadarwa Gwaggo Muka lakada Mata duka,wasu Kuma Suka tafi wajen Aunty Amarya ta fada dakinta tana ihu Suka bita ciki Santana yace ko karkashin gado ta shiga ku kamota,Dagaci abin yafi karfinsa yasan shi kanshi Yana magana Karuwan zasu ci ubansa,Santana Yana ta