Showing 69001 words to 72000 words out of 117873 words

Chapter 24 - Masarautar Mu 1 to 4 Complete

maboya ba ta yi ba.
To me Uncle Yarima zai ce mata? Na ji auren da aka yi mana bagatatan ni ma bana so ko me? Ko ki kama kanki ni ina da mata ta da nake matukar so? Ba ta bukatar wata sabuwar muamala a tsakanin su bayan official one irin wadda ke tsakanin su a baya, cuta ce an gama yi mata tunda an hada ta da shi, don haka ta yi kememe ta yi kemadagas ta ki kunna waya. Kulawa ma yabawa ce inji 'yan magana.
Ya gaji da trying wayar Saade a daren yau, ana cewa a kashe, sosai yake son ya gan ta don ya ga da fuskar da ta karbi wannan babban alkhairin da ya same su. Yes shi a wajen sa alkhairi ne, GIANT (katoton) alkhairi ma kuwa, da bashi da yadda zai iya bayyana farin cikin sa da muhimmancin sa gare shi!
An bashi abinda ya dade yana so yana kwadayi batare da ya cancanta ba, ba kuma tare da ya furta ba kuma ba tare da ya sha wahala ba sannan cikin girma da daukaka. A ganin sa hes not worth enough (bashi da darajar da zai mallaki Sa'ade) innocent soul kaman Saade, in yayi laakari ga tarin nakasun sa da laifuffukan sa na baya. Ya dade yana sunsunar takalmin, bai san ta yadda zai yi ya dauka ba. Sabida ganin cewa Sa'ade tafi karfin sa.

Sai Askirama-Mai Askira cikin dimbin alfarmominsa da karamcinsa da ba su taba karewa a gare shi ya sunkuya ya hutar da shi, ya dauko takalmin nan ya miko masa har inda yake.
Me zai ce da Mai Askira? Me zai ce da Fulani Bilkisu banda Allah ya ja kwanan su? Sun yi masa gatan da ya kasa yiwa kansa. Ba zai gushe yana rokon Allah Ya kara soyayya a tsakaninsu, ya ba shi soyayyar Saadatu kwatankwacin ta mahaifiyar ta Fulani ga Askirama!
Da ya gaji da trying wayar Saadatu ta ki kunnawa sai ya kira Yaa Maira. Ya san Yaa Maira ce kadai zata yi masa wannan taimakon, sabida yadda take son sa da tausayin sa, in ba haka ba shi da ganin Saadatu sai an gama biki.
Yaa Maira na dagawa ta ce,
Angon Saadatu ka sha kamshi.
Murmushi Yarima ya yi, cikin jin wani irin karin nutsuwa a zuciyar sa da ruhin sa wanda bai taba ji a baya ba, da wannan daddadan suna da inkiya da Yaa Maira ta kira shi da shi, ya ce,
ni bana kamshi Yaa Maira tunda amaryar ba ta son ganina ko kadan balle ta san min kamshin, ko murya ta bata son ji Yaa Maira. Ko kai na ya fara furfura ne ban sani ba? Kin san yammata basa son mai furfura, rabo na da ita tun ranar da muka zo, ko waya ta ki kunnawa don kar in kira ta in ji muryar ta in samu nutsuwa.
Dariya Yaa Maira ta yi, in wani ne yace Yarima ne wannan zata musa, Yariman da magana a gare shi sai dole, fitar kalma wannan tsada gareta daga bakin sa, amma yau shine yake joking, lallai Saadatu ta ciri tuta kaman uwarta, wane irin sirri gare su haka? Da suke juya zukatan sarakuna? Bata tantama in nan gaba kadan Saade bata juye kan Yarima ba kamar yadda mahaifiyarta ta juye na Askirama. Ita dai in auren Saa zai raba Yarima da bin mata ba ta da damuwa a kan hakan, ta tabbata dama ranar da ya auri matar da yakewa hakikanin so zai bari, musamman idan halittar su ta zo daya, tunda Mai Askira ya hakura da kwarkwarori tun zuwan Baggara Bilkisu,ta ce,
Amma Saadatu ba ta kyauta ba, an gaya mata miji wasa ne? Bari in je in samu Fulani zuwa anjima a shirya muku ganawa ta musamman, don in anka shiga hidimar bikin nan ba za ku samu ko ganin juna ba.
Tana kashe wayar ta nufi unguwar Fulani Bilkisu.
A falon ta tadda ta tare da mutane, nan ta nemi kebewa da Fulani, suka dan yi magana kuskus, Fulani ta kama baki cikin mamaki.
Ashe Saade ba ta kunna wayar ba? Na rasa me ke damun yarinyar nan???
Yaa Maira ta ce, Ki bi ta a hankali dai, Saadatu na bukatar lallashi har zuciyarta ta samu nutsuwa da auren, kada ki manta baku nemi shawarar ta ko amincewar ta ba, don haka lallashi ne naku ba tursasawa ba, shi ma Yarima gajen hakuri ne irin nasa, ina ce tare za su koma Abujan?
Fulani ba ta saurari Yaa Maira ba ta nufi dakin Saade cikin fushi.
Ita da Hanne ta same su tana ware sitturunta masu kyau kala-kala daga wardrove tana bai wa Hanne. Suna yi suna hira. Gabadaya ta manta da damuwar da take ciki sabida zuwan Hanne.
Ashe ba ki kunna wayarki ba Saa?
Fulani ta fada daga bakin kofa. Tana kokarin hadiyefushin ta.
Saade ta turo baki gaba irin na shagwababbun yaya, Babu caji ne, amma yanzu zan saka daman.
Ya yi kyau!.
In ji Fulani, sannan ta juya ta bar dakin cikin fushi.
Dakinta ta koma ta dauko wani dandatsetsen leshi cotton mara nauyi kalar maroon da ratsin golden, an yi masa dinkin riga da zani fitted, ta saka Fanna ta saka shi a kabbasa ya turaru tukun ta feshe su da turarukanta na musamman, ta kuma zabo mayafin da ya dace da su kalar golden sannan ta dawo dakin Saade, Hanne ta mika wa kayan,
Taimaka mata ta shirya Hanne, tana da baki daga Abuja.
Tana gama fadin haka ta juya. Mamaki ya kama Saade, ita yaushe ta yi kawa a Abuja? Kawarta daya Saidu ne, kuma Fulani ba za ta ce ta yi kwalliya saboda shi ba, watakila ya gaji da nemanta a waya ne ya taho har Askira, amma ta ya ya Fulani za ta ce ta yi masa kwalliya irin wannan?
Sai ta mikawa Hanne kayan.
Bar kayan nan Hanne, Fulani ba ta san wanene ne ya zo ba.
Hanne ta ce, Tunda dai ta ce ki saka, to ki saka kawai, baki ganin kin bata mata rai ne?.
Ta mika mata zanin, daya bayan daya ta sanya, sai ga Fanna ta shigo tare da wata mata, wadda Saade ta san ta mai kwalliyar Fulani ce during occassions, ta ce, Fulani ce ta turo ta ta yi mata kwalliya.
Haka matar nan ta zaunar da ita kan stool ta yi mata wani irin light serene make up, karo na farko da cute fuskar Saade ta ga sassanyan fentin bature, tana kunci tana komai matar bata biye mata ba tunda bisa umarnin Fulani take, a ganin ta ma fushin da Saade ke yi ya kara ma fuskar ta annuri, classique and gentle amaryar Yareema, [inji mai kwalliya cikin ran ta], bada jimawa ba tuni Saade ta fito a beautiful Princess dinta.
Matar wadda babarbariya ce ta feshe ta da tsadaddun turarukan humra, sannan Fanna ta kamo hannunta suka fito, Saade ta kasa magana bin Fanna kawai ta ke, Fanna ba ta tsaya da ita a koina ba sai falon saukar bakin Fulani na musamman.
Falon shimfide yake da kilisai na alfarma da tumtum a koina, da hoton Mai Askira cikin nadi da amawali windowsize a gabas maso kudu na dakin, sannan zagaye da golden din kujeru na zamani. Har bisa royal chairs na falon ta kaita ta zaunar da ita, ta gyara mata lullubi, sannan ta juya tana fadin,
A fito lafiya uwargijiya ta, takawar ki lafiya Gimbiya Saadatu.

Fanna ta fita da kamar minti biyu, angon na Saadatu ya bayyana gabadayan sa cikin falon. Yana takun sa na kasaita tamkar mai tafiya akan gajimare. Shalelen Askirama da Ya Gumsu. Kanin Ya Maira da Mairam Murjanatu. Mijin Aisha Sultana. A yanzu kuma angon Saadatu saar mata. Wato [Dr]Yareema Sageer Yusuf Askira. Kamar dama yana falon dake bin wannan tun dazu yana jira.
A yau sanye yake cikin royal attire dinsa, shudiyar alkyabba da jamfa na wani rantsattsen yadin filtex, hular kan sa Dara ce baka gashin jikinta na reto daga gefen damana fuskar sa ba karamin kyau tayi masa ba.
Tunda Saadatu ta ke a tsayin rayuwar ta ba ta taba ganin mutum maabocin cikar zati, ilhama da kwarjinin Yareema Sageer da ke tsaye nan a gabanta a yau ba. Gabadaya ya canza mata, daga wayayyen dan bokon nan da ta sani mai tsukewa cikin suit da necktayil zuwa hakikanin BASARAKE na gasken-gaske, sarautar ma ta Askira wadda duk yankin Borno babu kamarta.
Ji ta yi kamar ta narke a wurin lokacin da Yareema ya tako ya tsaya a gabanta, kamshinsa na Invictus (Paco Rabbanne) da ke hargitsa ta ya mamayi hancinta. Ta sunkuyar da kai ta kasa ko kwakkwaran motsi.Dr. Sageer ya yi taku daya, biyu, ya tsaya a gaban Saadatu, kwalliyar da aka yi mata bai taba ganin ta da ita ba haka kalar kayan jikin ta ya matukar karbar lafiyayyar fatar jikin ta, ya kara fiddo zahirin kyawun ta da kwarjinin ta na Shuwa Arab, duk wani fushi da ya zo da shi da niyyar sauke mata a kan rashin kunna waya tunda aka daura aure, sai ya ji yana melting yana bin rariya, yayin da wata matsiyaciyar soyayya ke maye gurbin sa.
Ya zuba hannuwansa duka a cikin aljihun sa, lumsassun idanun sa a kan ta, murya a sanyaye kamar ba Uncle Yareeman da ta sani ba, ya ce,
Saadatu laifin me na yi miki ki ka ki kunna wayarki? Atleast mu gaisa ko? Rabo na da ke tun zuwan mu garin nan. Kin san yadda na azabtu a kan hakan? This is sheer punishment! Ba don Yaa Maira ba kenan har mu koma Abuja ba zan ganki ko na ji muryarki ba Saadatu, me yasa? Do you know how difficult and tortured is this to me?
Maimakon ta ba shi amsa sai hawaye suka zubo. Ganewa da ta yi cewa Yarima Sageer bai cikin irin bacin ran da damuwar da ita take ciki akan auren bazatan da aka yi musu. Karewa ma ya karbi alamarin da hannu bibbiyu. Har yana fadin rashin ganin ta tun zuwan su gidan ya azabtar da shi. To dama can yana jiran hakan ne ko yaya ne? Ko dama akwai wani abu makamancin so a ran sa da bai taba nuna mata ba sabida girman kan sa? Aka dauke ta a bagas aka bashi don shi dan gatan Askira ne?
Hawayen da suka sa Yarima saurin durkusawa a gaban Saadatu ba tare da ya san lokacin da ya yi hakan ba. Ya dora tafin hannun sa akan kafar ta. Zuciyar sa cike da fargabar kada dai Saadatu bata farin-ciki da kasancewa cikin iyalin sa? Kada dai hawayen ta na nufin..bata yi naam da zamantowa matar sa wani bangare na rayuwar sa ba? Idan hakan ne a ran ta shi yaya zai yi da rayuwar sa yanzu? Ya riga ya afka a rijiyar da zurfin ta ya fi na gaba dubu. Babu mai iya fito da shi sai Saadatu.
Already Saadatu ta dade da mamaye shi, ta mamaye kowanne gurbi da kowanne sako na zuciyar sa ba tareda ya san lokacin da hakan ya fara ba…
Ya wayi gari ne ya gan shi dumu dumu a soyayyar Saade. A wannan lokacin hes helpless idan Saade ta ce bata auren sa yaya zai yi? Bai iya sakin ta! Baa saki a gidan su, ko ana yi bai taba sakin Saadatu. Ba kuma ya so ya nuna mata weakness din sa.
Ya daga hannu zai rike natafor the first time a tarihin rayuwar su don ya korewa kan sa shakkun kasancewar ta mallakin sa a yanzu, ta yi saurin ja da baya cikin matukar razana! As if lantarki ya jona mata. Tare da maida hannayen ta duka baya ta sarke su a bayan ta. Yareema Sageer Ya daga lumsassun idanunshi yana kallon Saade, a galabaice, a susuce cikin wani yanayi na damuwa da rashin sanin abin cewa.
A lokacin ne Saade ta soma shesshekar kuka a hankali, kukan da ya ratsa har cikin kwanya, ruhi da zuciyar Yareema ya hargitsa shi, ya sake kai hannu zai rike ta, ta yi maza ta sake ja da baya.

Kada ka kuskura ka taba ni, ni ba zan auri mai yin ZINA ba, Allah ya tsare ni, kuma ba zan kuma bin ka Abuja ba!.

Cikin wata irin razana Yarima Sageer ya wara manyan idon sa ya dubi Saadatu, da iyakacin girman su, a ina ta ji wannan maganar? Ya bude baki zai yi magana, ga dukkan mamakin sa maganar ta makale ta kasa fita, kafin ya ankara Saadatu ta mike ta nufi kofa da zummar ficewa.
Da wani irin zafin nama Yarima ya sha gabanta, ya kama duka kafadunta biyu ya girgiza ta da karfi. Sai da kashin kafadar ta ya amsa. Bata san sanda tace,
zaka balla ni!. A kausashe Dr. Sageer yace.
“Kin san da wa ki ke magana Saadatu? Are you scolding me?
Hawayen da ke tare cikin idanunta suka idasa gangarowa akan kuncin ta, ta ce cikin karyayyar murya marar amo da rashin karsashi.
Im not scolding you. Kawai ina gaya maka abinda na dade da sani ne a kan ka. Na san da wa na ke magana mana; Yarima ne, Yariman Askira, Yarima Sageer mai jiran gadon Askira, amma ba mai halin real Askirama ba
Shi Askirama ba ya zina, matan sa ba sa shan giya, ba sa zuwa Bar, sannan suna yin sallah”.
Ta bude dukkan idanun ta dake jike da hawaye ta cigaba da cewa A gidan Yarima duk ana yin wadannan abubuwan dana lissafa, don haka babu ni a wannan gidan. Matattarar shaidanu da sabon Allah.
In kuma aka takura min sai na bi ka, wallahi zan gudu! Ba za ku kara ganina ba, da ma ba ku san daga ina na zo barana daya kawai kuka ganni a gidan ku, don bani da gata ubana talakane kuma ya mutu, ni sai a yi min aure ba izini na.
Saadatu ba ta yi aune ba idanun ta bakidaya a rufe, tana ta zubda rashin kunyar ta ta hanyar fadin duk abinda ya zo bakinta wa Yarima, ta hakan ne kawai zata amayar da kuncin dake zuciyar ta, tunda in ba shi din ba wa zata iya gayawa wannan? Burin ta ya ji haushi ya bar musu sassan su, in yaso kada ya kara dawowa.
Ba zaton ta ba tsammani ta ji Sageer ya janyota jikin sa gabagadi da wata irin azama da zafin nama, jikin sa na shaking [tsuma] kamar kamar bai taba rike mace ba a tsayin rayuwar sa sai wannan karon. Har kuma ran sa da zuciyar sa abinda yake ji kenan a zahiri. Kafin ta yi kokarin zamewa ko kwacewa sai jin taushin bakin Yarima Sageer ta yi ya sauka a kan nata ya sima sumbatar ta in an abrupt manner, wanda hakan ya rufe sauran bakar maganar da ta ke so ta furta. Cewa ita a rasa wanda zaa aura mata sai mai yin zina? Ba gara Saidu ba? Kafin ta tantance what is going to happen next? Dr. Sageer ya soma hawaye, bai taba nadama ba akan rayuwar sa irin yau, gabadaya jikin sa yayi sanyi da kalaman Sa'adatu, ba tare da yayi shawara da zuciyar sa ba ya fara sumbatar ta gently, expertedly, and then by dragging her closer, sai ya cigaba da kissing dinta softly, then a urunce wato [da sauri da sauri].
Tun daga karkashin zuciyar sa sautin sumbar take fitowa tana bada sauti. Duk kokarinta na kwatar kanta hannun Yareema ta kasa sai da ya yi sumbar mai isar sa tukunna, ya sanyata cikin jikin sa a hankali ya rungumeta tsam-tsam ta hanyar hada bugun zuciyoyin dake cikin kirjin su wuri guda, inama zata iya jin tari nadamar dake cin ran sa daga bugun kirjin sa? Yana yi yana sauke kakkarfar ajiyar zuciya. Sai kuma ya bi hawayen fuskarta yana dauke su tsaf da lips din sa. Ya dago fuskar ta da hawaye kadai ke zuba tana kakabin abinda ke faruwa a mafarki ne ko ido biyu?
Dr. Sageer ya sanya fuskar ta cikin tafukan sa, sannan ya sake ta ya ja da baya kadan yana jifanta da wani irin sassanyar kallo, wanda Saadatu ba ta taba gani a tare da shi ba. Gabadaya ya rikide mata ya koma tamkar ba shi ba. Ga dai nadama ce fal da tsoron rasa Sa'ade a ran sa tunda ta san ko wanene shi, amma abinda ya furta ba lallashi bane ba kuma nadamar dake baibaye da shi bane. Yarima Sageer is always bold, baya yarda ya nuna weakness din sa a komai.
Kin fara da kissing mai yin zina Saadatu, kafin ku sha giyar tare ke da

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login