Showing 30001 words to 33000 words out of 117873 words
lawyer na Barrister Sadiq Rufa'i Wali.
MASARAUTAR MU 2
Ya kara tattaro dan sauran karfin gwiwar da ya rage masa, yace cikin kwantar da murya, kodayake kodayaushe muryarsa a kwance take.
"Baturiyar Asia ce, Jew (bayahudiya), ta yarda zata karbi addinin muslunci in dai zan aure ta".
Daga sarki har Ya Gumsu a razane suka dube shi. Mai martaba ya kasa cewa komai kamar an dinke masa baki. Ya mutu a zaune cikin kujerar sa. Ya Gumsu ta mike tsaye tana nuna shi da dan yatsa "....ka yi kadan Yarima, karya kake ka tozarta ni a idon duniya da idon kishiyoyi na masu son ganin faduwa ta!. Ko mata sun kare ban yarje maka auren nan ba, da yawun baki na bazan taba saka albarka ta ba!!!".
Sarki Yusufu ya ce "kana iya tafiya Yareema zamu yi shawara, duk abinda muka yanke Waziri zai kira ka". Ya Gumsu ta zaro ido tana kallon Mai Askira tamkar idanun ta zasu fado. Tunda har ya amince zai tattauna zancen nan da Waziri ta san karshen alewa kasa.....ba ya kai zance ga Waziri sai ya fara yin na'am da shi a karan - kansa. Ta fashe da kuka ta tashi ta bar falon. Yarima ya mike zai bi bayan ta. Sarki ya ce ya kyaleta sai ta huce yanzu bazata taba sauraron sa ba.
Ya koma ya zauna jikin sa a sanyaye, da wannan damar Sarki Yusufu yayi amfani ya dinga tambayarsa abubuwa akan Rose din, da yadda suka hadu, shi kuma ya gaya masa duk abinda ya kamata ya sani banda wanda bai kamata ba. Ya kare zancen sa da cewa yana mata kwadayin musulunci ta hannun sa don jihadi, sabida kyawawan halayen ta, sannan ita din ma tana sha'awar addinin muslunci a karan - kanta. Ta zabi ta bar kowa nata in dai za'a bar shi ya aure ta.
Alanguburo ya fahimce shi sabida saukin kansa, a lokaci guda yana kokawar ture nasa BURIN akan Yarima Sageer can gefe daga zuciyar sa, yana fadawa zuciyar sa ya bar shi yayi jihadin; wani ya shiryu ta hannun ka yafi a baka jajayen Rakuma tunda Allah bai haramta ba. Ba duk abinda muka yi burin tabbatuwar sa ne yake tabbata ba. Wasu mafarkan a mafarkai kawai suke tsayawa, ba sa zama REALITY yadda muke burin su. Wasu kuma Allah kan jinkirtawa bawa zuwa lokaci mafi dacewa. Ya sallame shi da cewa ya saurari kiran Waziri idan sun tattauna gobe.
****
Sarki Yusufu da Wazirin sa Ibrahim suna tattaunawa akan al'amarin Yarima bayan sun kadaice a falon ganawar sirrin su, Waziri yace su bar Yarima yayi auren su samu ladan muslunci, amma bisa sharuddan cewa zata biyo shi gida su zauna tare dasu cikin MASARAUTA a matsayin sa na Yarima mai jiran gado. Dole ya dawo gida gabadaya ya zauna cikin ahalin sa.
Lokacin da Waziri ya kira Yarima ya gaya masa hukuncin da suka yanke, Yarima Sageer yayi dan jim! Domin nan kusa bai shirya dawowa gida ba, ba zai iya rayuwar karamin gari kamar Askira ba, zai takura, ba zai shana yadda ya saba ba, sannan Rose ma zata takura, ga zafin Maiduguri, bata taba zuwa Africa ba haifaffiyar South - Korea ce. Aiki ya kai iyayenta Amsterdam. Ba abinda ya tsana irin ace shine 'mai jiran gado', bayan ba shikadai ne namiji ba, shi sarauta sam bata cikin tsarin sa, Yarima Sageer bakin bature ne kawai wanda ya rungumi affluent western lifestyle ya manta da asalin sa tsayin shekaru masu yawa, wannan kuma ya faru ne da laifin su iyayen sa da suke ganin yin nisa da gida fintinkau shine abinda zai nutsar musu da shi; don nutsuwa ya nutsu irin wanda tarin shekaru ke haifarwa da namiji, amma ba nutsuwa irin wadda su suke zato ba.
Karewa ma, ya goge ne yayi mastering akan harkar neman mata, har wadanda ba addinin su daya ba. Amma in ka gan shi a fuska tsammani zakayi wani saint ne shi din (waliyyi) sabida tsabar iya badda-kama a gaban iyaye. Abu daya Allah ya tserar da Yarima akan sa shine shan giya, ko sha'awar ta bai taba yi ba. Yana matukar kyamar ta. A cewar sa ai sai da hankali ake sallah dai-dai, kuma a yi ta akan lokaci. Hatta sigari tun lokacin tashen samartakar sa ya bar ta.
Amma da ya duba wannan alfarma da iyayen sa suka yi masa wadda bai taba zaton zata zo masa da sauki haka ba, sun bar shi ya auri zabin sa dai-dai da ra'ayin sa, sannan sun toshe kunnuwan su daga duk abinda zasu ji akan auren nasa, auren da a tarihin masarautar su ba'a taba yin irin sa ba, sai ya ga cewa ya zama dole shima ya amince da tasu bukatar na dawowa Askira tare da matar sa. Kafin nan zai roke su su bashi lokaci, ya kammala phd din sa, ya tattaro kasuwancin sa zuwa Nigeria ya kuma nemi aikin da zai rike shi in ya dawo, ba zai zo ya dogara da mahaifin sa ba kamar yadda akasarin 'ya'yan sarauta ke yi.
Koda ya yiwa Waziri wannan bayanin take ya amince, ya kuma ce sun bashi shekaru biyu ya kammala komai, ya dawo tare da matar a musuluntar da ita a daura auren su. Awaisu was shocked lokacin da yaji labarin nan domin bai taba zaton iyayen su zasu amince da zancen Rose ba, haka bai taba zaton Yarima is serious akan maganar Rose ba, ya dauka yana fada ne kawai for fun irin nasa. Shikam tuni Ba'ana ta zaba masa mata 'yar kanwar ta mai suna Asiya suna dawowa za'a hada auren nasu lokaci guda shi da Yarima, don yarinyar bata kare sakandire ba ma.
Kwanan su bakwai suka koma Amsterdam with nostalgia (cike da begen gida) a yadda suka tsammaci masarautar ta su sai suka tarar akwai cigaba na zamani sosai fiye da yadda suka tafi suka bar ta. Suka kuma fara tunanin hanyoyin da zasu kara kawo mata daukaka da cigaba na zamani ta kara zama zakaran gwajin dafi a masarautun jihar Borno tsararrakin ta. Tuni Yarima ya tsara sababbin gine-gine da za'a kara cikin masarautar, da yadda za'ayi renovating din ta daga kamfanin gine-gine da tsare-tsaren gidaje na COSIMCO na kasar Amsterdam (Neitherlands).
Yana komawa abinda ya maida hankali akai kenan, wato project da cosimco akan masarautar su. Daga can suka taho suka fara ayyukan su a masarautar Askira. Gininnika na zamani masu tsayi da nagarta suka kara fiddo da martabar masarautar Askira. "Lallai dan zaki an girma" Sarki ya fadawa Waziri cikin murmushi a lokacin da suke zagaye cikin masarautar da wajen ta, suna kallon renovation din da Yarima ya tsara da kansa ya kuma turo COSIMCO construction company suka yi. Waziri da sauran 'king-makers' sai albarka suke sanyawa Yarima, fatan su bada jimawa ba ya dawo ya karbi sarautar mahaifin sa tun yana raye. Wanda basu sani ba wannan baya cikin tsarin Yarima Sageer ko kadan. Bar shi dai a gogaggen dan bokon sa. Awaisu ne kawai ya san hakan.
****
Hutun su Sa'ade na karewa suka koma makaranta, ashe wani abin alhini ke can yana jiran ta, shiru-shiru tana zuba idon ganin dawowar Raheema amma har ta share sati biyu da komawa Raheema bata dawo ba.
Sa'ade ta kasa sukuni, ta kasa walwala ta kuma kasa cigaba da harkokin karatun ta yadda ta saba a dalilin babu Rahima, ta kuma rasa wanda zata tambaya ko ya san abinda ya hana Rahima dowowa don kowa ita yake tambaya. Ga wani kuskure data yi bata taba karbar adireshin Raheema ba, sabida tana ganin ko ta karba babu wanda zai kaita, Fulani bazata taba barin ta ta je ba.
Da abin ya isheta sai ta tafi ofishin principal, tayi gaisuwa ga principal sannan ta soma share hawaye. Principal tace "what's wrong Sa'adatu Hashim?" Sa'ade ta idasa fashewa da kuka a gabanta sannan ta gaya mata yau sati uku kenan Raheema Kyari bata dawo ba.
Principal tasa aka yi bincike akan rashin dawowar Raheema, nan malamin dake kula da dawowar dalibai ya sanar da ita sakon da mahaifin Raheema ya aiko na cewa sun bar kasar Najeriya. Wanda ke nufin Raheema ta bar makarantar gabadaya.
Damuwar Sa'ade sai ta nunku akan ta da, me ya sa Raheema za ta bar kasar ba tare da ta yi mata sallama ba? Laifin me ta yi mata? Amincin dake tsakanin su ya fi gaban haka. Bata san ta yi mugun shaquwa da Raheema ba sai yau data wayi gari babu ita cikin kwalejin El-Kanemi. Rayuwar Sa'ade gabadaya sai ta sauya a makaranta ta zama ba umh ba umh-umh. Haka ta dukufa yi wa Raheema addu'a ba dare ba rana kan Allah yasa tana lafiya, tana kuma rokon Allah ya sake hada su cikin gaggawa.
Sannan a fannin karatu ta kara dagewa, don yanzun shi kadai ne abinda ke debe mata kewa. Tana yawan tunanin Zarah da Fulani, amma kullum tana sawa a ranta Fulani bata son ta don haka is a waste of time yawan tunanin ta data ke yi, har addu'a take yi a kowacce sallahr farillarta Allah ya rage mata son da ta ke yi wa mahaifiyar ta Fulani Bilkisu!
****
BAYAN SHEKARA BIYU!
Abubuwa da yawa sun faru cikin shekaru biyun nan, wadanda yawanci rigingimu ne na kishi a cikin gida tsakanin Ya Gumsu da Fulani Bilkisu. Sun ki zama lafiya da juna, amma kashi 80% na rigingimun in ka bincika zaka tarar laifin Ya Gumsu ne, tana kishi da Fulani Bilkisu ba dan kadan ba, a bisa abubuwa da dama; muhimmi shine son da Askirama ke mata wanda ya zarce na kowacce cikin matan auren sa, kuma ba ya iya boyewa. Yayin da ita Ya Gumsu a wurin ta ita ta cancanci wannan fifitawar a matsayin ta na uwar Yarima kuma uwar manyan 'ya'yan sa.
A haka dai ake rayuwar, da dadi ba dadi a gidan sarkin Askira, kamar kowanne gidan sarauta, duk wani babban gida ko ba na sarauta ba ya gaji haka, girma na kara kama kowaccen su, kamar kuma suna girma ana kara rura wutar kishi a tsakanin su.
A yau Litinin, gidan sarautar Askira an tashi da hidimar shirin tarbar Yarima Sageer wanda zai sauka a yammacin yau tareda matar da zai aura, 'Rose Hathaway'. Labari ya gama baza cikin gida na inda Yarima ya nemo aure. Surutu ba irin wanda ba'ayi a sassan kowacce daga cikin matan gidan in ka dauke unguwar Fulani Bilkisu, ita kadaice ta goyawa Yarima baya akan auren da yake so kuma bata yi Allah wadai da zabin nasa ba, ko dama kusan koyaushe ra'ayinta na zuwa daidai dana maimartaba ne.
Yamma lis Yarima Sageer da dan uwansa Awaisu da Rose wadda ta sha doguwar riga har kasa da mayafinta kamar balarabiya suka iso masarautar Askira karkashin rakiyar dogarawan fada masu yawa, wadanda suka dauko su daga filin jirgi daga Maiduguri a mota civilian ta Askira Emirate.
A wannan lokacin Sa'ade na makaranta tana zana jarrabawar shiga aji biyar SS 2. Ya Gumsu ta yi tsalle ta dire tace ba dai baturiyar Yarima a sassanta ba, babu ita babu wannan auren koda za'a sa mata wuka a makoshi. Don haka Mai Askira ya ce a kaita unguwar Fulani Bilkisu ta zauna karkashin kulawar ta.
Dakin Sa'ade ta sa Fanna ta gyarawa matar Yareema, duk abinda zata bukata Fulani ta tanadar mata, to saidai hira ta gagara tsakanin su don Fulani bata iya turanci ba, saidai ta yi magana da Yarima a waya shikuma ya kira Fulani ya gaya mata abinda ta ce. Kwanan su biyu da dawowa aka musuluntar da Rose a masauratar Askira aka daura auren ta da Yarima Sagir, babu wata gayya ta kunya da sarki yayi iya jama'ar gari ne kawai da king-makers suka shaida auren Yarima Sagir, bai gayyato 'yan uwan sa sarakuna ba, shi kansa bai san meyasa a can kasan ran sa baya farin ciki ko kadan da auren ba, duk da cewa bisa amincewar sa da yardar sa ne. Ya dauka Rose zata zo tare da wani nata, sai ya ganta zikau daga ita sai jakar kayan ta... sai ya soma tambayar kansa ranar da 'ya'yan Yarima suka tambayi dangin mahaifiyar su me zai ce musu???
Ko dai uwar Yareema, Ya Gumsu, ta fi shi gaskiya ne???
****
Babu wani shagalin biki kamar ba auren Yarima guda ba, haka aka dauki amaryar aka kaita gidan da Maimartaba ya ginawa Yarima wanda ke gefen masarauta. Gida ne tankarere ginin sarauta kuma ginin zamani, wanda ya lashe miliyoyin kudi har ya zarta ginin masarauta tsari sabida an yi amfani da hikimar kamfanin cosimco. In ka ji ana aljannar duniya to gidan Yareema Sageer ne. Auren Awaisu sai bayan shekara biyu don matar da aka bashi bata gama makarantar sakandire ba.
Rayuwar Yareema da amaryar sa Rose wadda ta karbi suna (Aisha - Sultana), sun dora ta ne daga inda suka tsaya a Amsterdam, wato rayuwar nasara zallah, don su kan manta cikin masarautar Askira su ke, Yareema na matukar son Sultana yayin da ita kuma ta karbi muslunci ne don son data ke wa Yareema ba don tana ra'ayi ba, don ya ce mata shine kadai hanyar da iyayen sa zasu yarje mishi auren ta.
Don haka kusan zamu iya cewa addinin ta karbe shi ne kawai a baka, amma daga sanda suka bar cikin gida zuwa nasu gidan ta jinginar da sallahr data fara a sassan Fulani Bilkisu, ta gayawa Yareema ita bazata iya kullum ba, akwai wahala sai ta saba tukunna, yayin da Yareema ya nuna ba zai lamunci hakan ba sai take yi a gaban sa, in baya nan kuwa a hadu a gaba.
Sati hudu ana barzar amarci, an cika musu gida da bayi da hadimai, Sultana sai a lokacin take lakantar ko wanene Yareema Sageer Yusuf Askira? Ashe a baya bata san komai a kan shi ba? Banda kasancewar shi abokin shashancin ta, ta fahimci a yanzun tana sahun gaba na mata masu sa'a a rayuwa, domin Sageer daya ne cikin dubu, wanda irin sa ta fannin nunawa matan su soyayya tsiraru ne a cikin al'umma.
He's genius a halayya da dabi'a, superb a rayuwar auratayya, splendid a tafiyar da matar sa.... Ko don ta cigaba da rayuwa da Yareema zata cigaba da zama cikin rigar addinin sa mai wahala, amma ba don ya dadata da kasa ba.
Watanni ukku Yareema ba ya komai sai neman aiki ta yanar gizo ba da sanin maimartaba ba, sai amarci da mai jan kunnen sa, Fulani Bilkisu ta zama uwar dakin Sultana ita ke kula da komai da ya shafe ta don Ya Gumsu ko gaisheta tayi bata amsawa, haka Ya Maira bata taba takowa gidan ta ba sai Humaira da Naja'atu, mazan kam suna zuwa sosai wajen Yareema musamman Ashgar wanda ya maida gidan wajen hirar sa sabida yadda Yarima ke jan sa a jiki, don yana tsananin tausaya masa, kuma yana samun sauki sosai daga rehabilitation din da Yarima yasa shi ya samu a kasar Amsterdam.
Ayyuka har biyu Yareema ya samu a lokaci daya, NTNU (Nigerian Turkish Nile University) dake Abuja sun bashi aikin koyarwa (lecturing) kamar yadda ya zaba a tsangayar (Pure and Applied Chemistry), haka OAU (Obafemi Awolawo University, Ile-Ife) suma sun dauke shi da gaggawa, tun kafin dawowar sa ya yanke shawarar komawa academia wani professsion da 'ya'yan sarauta basu fiya karba ba. Kamar yadda komai nasa yake daban da na sauran mutane, haka tunanin sa ma ya ke. Ba ya danganta kansa da sarauta ko kadan kamar yadda mahaifin sa ke so, a ganin sa tana hana 'yanci, sannan takura ce. Gashi shikuma mutum ne mai tsananin son rayuwar da babu takura, kuma babu matsantawa a cikin ta.
Mutum ne mai (tsinkaye) da tsantseni a cikin dukkan mu'amalolin rayuwar sa, mai son dogaro da kai, mai zafin nema, mai zafin nama, sannan mai nasara a kan duk abinda yasa a gaba. Bar shi dai da son matan sa (his only shortcoming) abinda zamu iya kira nature a jikin maza jinin sarauta, wanda zamu iya cewa tun bayan auren nan wata irin nutsuwa ta saukarwa Yareema Sageer Askira; Mata suka rage burge shi banda matarsa Aisha-Sultana. Haka ya zauna yana deleting numbobin mata kala-kala yare daban daban dake kan wayar sa, ya na fadawa kansa da kansa; yadda ya bar Amsterdam gabadaya, haka ya baro ta tareda dukkan matan da ya baro cikin ta.
Kasuwancin automobile din sa ma ya maido shi gida Nigeria ya dora Awaisu akan komai. Yanzu kuma da ya dawo sai ya hada da biyu daga cikin kannen sa wadanda suke