Showing 60001 words to 63000 words out of 117873 words

Chapter 21 - Masarautar Mu 1 to 4 Complete

shi kawai, theres something fishy going on akan Saadatu da har ya sa Maimartaba ya yi masa kiran gaggawa.
Ana kiran sallar magriba suka shiga Askira. Inda Awaisu ya ji dadi shi ne kafatanin fadawa da dogarai da duk wanda ke wajen ya shiga masallaci sallah lokacin da suka iso, ba don haka ba da tun fitowarsu mota za a fara tarar Yarima da Allah ya sanya alkhairi. Yan tsirarun da suka hadu da su a hanya mata ne bayi suke wucewa. Gaishe su kawai suka yi suka wuce.
Suna shiga sassan Yarima da ke cikin gidan alwallah suka yi suka tada sallah, kafin su idar hadiman Yarima sun gama jera musu abinci. Awaisu ne kawai ya zauna yana ci, Yarima sai magiya yake masa ya ba shi wayoyinsa yana cewa, sai ya fito daga ganawa da Maimartaba.
Kawai sai jin sallamar Ya Gumsu suka yi a kansu, karkashin rakiyar kuyanginta. Daga bakin kofa suka tsaya ita kadai ta shigo sai huci ta ke kamar mesa. Yarima da Awaisu suka mike tsaye a tare har suna hada baki a tare wajen cewa, Ya Gumsu lafiya??
Kawai sai ta zauna a kujera ta sa fuska cikin tafuka ta fashe da kuka.
Yarima da Awaisu suka tsugunna a gabanta suka kasa magana, suna nan durkushe gaban Ya Gumsu tana kuka suka jiyo takun tafiyar Askirama. Daga kirarin da ake masa daga waje suka gane shi ne yake tahowa.
Ya karaso har dakin Yarima bakinsa dauke da sallama. Idonsa ya sauka a kan Ya Gumsu, ransa ya yi mummunan baci, da kyar in ba ta lalata komai ba.
Biyo ni Yarima.
Abin da ya ce kawai kenan ya juya ya fita. Yarima ya kasa tashi daga gurin ya bar Ya Gumsu da ke kuka har sai da ta dago idanunta jage-jage da hawaye, ta ce,
In ka karbi auren nan da ya yi maka sai na dauke maka albarka.
A razane Yarima ya cira kai ya dubi mahaifiyarsa, kafin ya samu zarafin ce mata komai ta tashi ta fice kamar kububuwa.
Yarima ya shiga cikin halin rudu mara misaltuwa. Kawai sai ya bi bayan maimartaba ya bar Awaisu a wajen.
Awaisu ya jinjina kai cike da taraddadin wannan alamari, bai yi zaton ya Gumsu ba za ta so auren nan ba in ya yi laakari da yadda ta ke adawa da auren Yarima na farko. Da ya tuna kishin da ke tsakanin matan gidan sai mamakinsa ya ragu, don Saadatu ta fito daga dakin Bilkisu ne wadda suke kishi da ita fiye da kowacce matar sarki.
Yarima bai zauna ba sai da Askirama ya fara zama a kujerar mulkinsa. Ransa a tsananin bace don a zatonsa Ya Gumsu ta riga ta yi masa riga-malam-masallaci. Ya yi kokarin boye bacin ransa sabida ba ya taba bari a gane fushinsa, ya dubi Yareema Sageer da ya samu wuri ya zauna daga kasan kafafunsa.
Kafin in ce komai Yareema idan na yi maka umarni, uwarka ma ta yi maka, na wa za ka bi a cikinmu?
Yarima ya kara rudewa, gabadaya sun rikita shi, ya kasa gane komai. Kawai sai ya yi shiru ya sunkuyar da kai. Mai Askira ya yi murmushi ya ce, Aure na yi maka shi ne ta ke adawa, aure na mutunci da rufin asiri, auren da na tabbatar zai dauke dukkan kwadayi da shaawarka daga kan sauran mata kamar yadda ya dauke nawa daga kan Bilkisu ko kwarkwarorina na hakura da su daga ranar da na mallaki Bilkisu, domin matan BAGGARA daban ne. Don haka ne nake da kyakkyawan zaton cewa abin da ta haifa ma zai zamo irinta ga Sarki mai jiran gadon Askira. Na aura maka diyar Bilkisu, wato SAADATU don in raba ka da kusantar zina da matan haramun. Ya rage naka ka bi umarnina ko na mahaifiyarka. Ka tashi na sallame ka, ka je ka yi tunani kan abin da ya fi dacewa da kai. Rana ita yau za a fara biki, biki irin wanda ba a yi a aurenka na fari ba, bikin aladar gargajiya na masarautar Askira. Na kai shi zuwa rana ita yau ne don kawunta da ke kasar Italiya ya samu halarta shi da iyalinsa.
A nan Maimartaba ya gaya wa Yarima labarin asalin Saade, tun daga auren mahaifiyarta da Malam Hashimu zuwa rabuwarsu. Rayuwar Saade a kauye da ranar da abokin Babanta Malam Saleh ya kawo ta Askira ya karbe ta, wahalar da ta sha a hannun fulani kafin ta amshe ta matsayin ya, da nagartattun halayen Saade da ya dade yana fahimta. A karshe ya gaya masa tun farko ya yi niyyar aura masa Saade a matsayin matarsa ta farko sai ya kawo zancen Aisha-Sultana, shi kuma ya ba shi dama don ya fita hakkinsa. Yanzu ne yake so ya yi masa biyayya da auren Saade, duk abin da suke ciki shi da matarsa ya sani, kuma wannan shi ne matakin da zai iya dauka.
Ga mamakin Mai Askira tunda Yareema ya dukar da kai bai dago ba sai da ya kai aya, da ya dago idanunsa sun kada sun yi jazur kamar an gumbuda musu borkono, labarin Saade da ya ji daga bakin mahaifinsa ya gama kashe zuciyarsa, ya luguiguitata. Tun asali kuma ya dade da wani irin feelings a kan Saadatu wanda daga shi sai Ubangijinsa suka sani. Feelings din da shi kansa bai san ma'anar sa ba, bai san a muhallin da ya sanya shi ba. Yau da ya samu wannan labarin na zamowar Saadatu halalinsa, matar auren sa ta sunnah daga bakin da ba zai taba yi masa karya ba, zuciyarsa ta ki tsugunnuwa a waje daya, sai dawurwura ta ke a cikin kirjinsa kamar za ta fito ta bakinsa tsabar contentment din da ya cika zuciyar sa da wani sabon yanayi da ya samu kansa a ciki irin wanda biro ko yawun baki ba zai iya bayyanawa ba.

Lokacin da Yarima ya dago ido don ya baiwa mahaifinsa Askirama amsa, Askirama couldn't believe cewa hawaye ya gani a idon Yarima......
Hawayen da bai san na menene ba, tsakanin.... bakin cikin abin da ya yi masa, tausayin labarin Sa'ade, ko ko na farin - ciki ne kai tsaye? Ba zai iya cewa ba!!!

Mu karasa a littafi na 3.
Na yi muku alkawarin cigaban ba zai jima ba, insha Allahu.
Taku har abada;
Sumayyah Abdulkadir Takori.
27th August, 2021




MASARAUTAR MU!.





3








SUMAYYAH ABDULKADIR
takorikabara@gmail.com
babbangoro2015@yahoo.com

SADAUKARWA
Ga 'yar uwar da muka rasa a TAKORITES. Allah ya jikan ki da rahma HASNA'U yasa aljannah ce makomar ki. Ya bamu guzurin tadda ke. Takorites bazamu taba mantawa da ke ba. Da zaman amincin da muka yi tare.Muna son ki Hasna.


JINJINA
Har kullum jinjinar taku ce dukkan members na TAKORI'S ONLINE FORUM whtspp, littafin MASARAUTAR MU jinjina ne a gare ku, nagode da kauna da kwarin gwiwa, ni da ku hadin Allah ne. Allah ya bar mana zumunci har gidan aljannah.

GARGADI
Ban yarda a karanta wannan littafi a kowacce kafa ta sadarwa ba batare da iznina ba, tun daga radio, youtube, facebook, whtsp idan har ban yi izni ba, yin hakan karya doka ne kuma abin tuhuma ne daga lawyer na Barrister Sadiq Rufa'i Wali.

MASARAUTAR MU 3
Cikin raunin murya marar amo da rashin karsashi kamar ta wanda ya sha duka sabida yadda tayi kasa sosai, Yarima Sageer ya duka gaban mahaifin sa Askirama tamkar zai shige cikin sa, ya soma magana cikin sanyin murya da hardewar harshe.
Allah Kawun jo (Allah ya baka yawan rai) amma me ya sa tun lokacin da na dawo daga Amsterdam din, na kuma zo da bukatar auren Sultana baa tambayi raayi na a kan Saadatun ba? Allah ya ja da ran ku da a ce kun bayyana min kudirin ku akan mu tun farko, tun a wancan lokacin, a kan zabin da ku ka yi min, zan hakura ne da nawa zabin duk son da nake masa in karbi zabin ku. Saboda na san duk wani hukunci da za ku yi a kaina alkhairi ne wanda ni duk yawan shekaru na ba zan taba iya hangowa kaina ba!!!.
Sai hawaye suka fito sharr! Daga idanun Yareema Sageer, wadanda a yanzu Askirama ya tabbatar na farin-ciki ne ba na komai ba; hawayen wani irin contentment da Dr. Sageer bai taba ji a rayuwarsa ba.
Sai ya ji rayuwarsa a yau ta cika, ta zama cikakkiya, duk wani gibi dake cikin ta ya cika, amma a baya incomplete yake jin ta somehow shattered. duk da tarin dimbin achievements din da ke cikin ta. kamar akwai wani wawakeken gurbi a can kasan zuciyar sa da a da can, yake jira a cike, gurbin da bai san ko na menene, ko kuma na wanene ba, ya samu aka cike masashi yau unexpectedly. A yanzu ya gane cewa ya jima yana jiran shigowar Sa’adatu cikin rayuwar sa, he'spatiently waiting for her to come to his life ba tare da ya sani ba, sai a yau ya gane hakan.
A can baya kafin zuwan wannan ranar jin sa yake tamkar bashi da komai tamkar bai taba mallakar komai a rayuwar sa ba, duk da ba abinda bai mallaka din ba a rayuwar tasa including ASIAN WIFE.
Amma a yanzu da yake durkushe gaban Mai Askira yana yi masa wannan bushara sai yaji tamkar Askirama ya mallaka masa dukkan mulkin matan duniya, da mulkin dake cikin duniyar, mulkin da ya fi na garin Askira girma da ilahirin El-Kanem Borno Empire, da duk wani nau'in farin cikin dake cikin duniya da dan adam ke burin samu da ya mallaka masa Saadatu diyar Bilkisu da Mallam Hashimu.

Na gode da wannan gatan Mai Askira, Nagode ZAKIN Askira, ina mai rokon Ubangiji da ya fi ni godewa, na kuma karba da hannu bibbiyu. Ina rokon Allah Ya sa daga yau ba za ku sake jin wani abu a kaina wanda ya jibinci laifuffukana na baya ba.
Hakika na sani Askirama ni Sageer mai yawan laifi ne, mai saba muku ne, mai ketare tarbiyyar da kuka yi masa, amma hakan bai sa kun yi fushi da ni ba, kullum burin ku da fatan ku shine in dawo hanya madaidaiciya, wanda hakan yasa a kullum nake cikin tuba da neman gafarar Ubangiji. Ina rokon Allah ya fidda ni kunyar ku, Ya ba ni ikon rike muku yar ku da amana.
A yi min godiya wurin Fulanin Sarki (yana nufin Fulani Bilkisu), kodayake bari in je in same ta da kaina.
Askirama sai gani ya yi Yarima Sageer ya mike cikin wata irin azama, jikin sa har bari yake, gabadaya ya zama ba cikin nutsuwar sa ba, ya rude saboda excitement din da ya samu kan sa a ciki. Wanda Mai Askira zai iya rantsewa bai taba ganin sa cikin kwatankwacin irin wannan farin-cikin ba.
Sai Askirama ya mika hannu ya kamo hannun sa, kada ya je ya yi abun kunya a gaban bayi da kuyangin Fulani Bilkisu, kuma dai Fulanin ta gaya masa Saade ta dau fushi tun jiya ta kulle kanta a daki. Wanda ke nuna ita bata murna da auren ko kadan. Kamar yadda nasa dan ke neman shidewa sabida farin-cikin hakan.
Zo zauna in kirawo Fulanin ka yi mata godiyar nan a gabana, kada ka je sassan ta yanzu har sai bayan biki. Baa zuwa. Zuwa lokacin Saadatu ta huce daga laifin da muka taru muka yi mata.
Yareema ya yi murmushi yana sosa kai, laifi? Auren sa ne ya zamo laifi ga Saade? Kodayake bai kamata hakan ya zamo abin mamaki ba a gare shi duba da cewa daga shi har ita respect ne a tsakanin su, babu wata magana bayan wannan, koda ace akwai din ita a gareta babu komai tunda bai taba furta mata ba, ko nuna wata alama da zata gane cewa he sincerely admires her tun farkon rayuwar ta a gidan sa.
A lokacin suka hada ido da mahaifin sa wanda ya kura masa ido kawai yana murmushi, yana karanto duk abinda yake son karanta. Yareema Sageer yayi hanzarin dawowa daga duniyar tunanin da ya fada cikin jin nauyin kaifafan idanun Askirama. Kada dai ya zamanto cewa Mai Askira ya gane a rude yake gabadayan sa? Kuma already a rijiya yake? A rayuwar shi babu farin cikin da ya taba ruda shi irin na yau, kai mawuyaci ne wani abu yasa ya kasa mallakar kan sa amma yau? Saadatu a matsayin matar sa! Wani al'amari ne da bai zata ba. It comes abruptly. And it touches him more than he can imagine. Wani abu ne da bai taba kawowa zai samu da sauki haka ba, duk da zuciyar sa ta dade tana buri, kwakwalwar sa na kiyasta masa, ruhin sa na kwadayi da mafarkin kasancewar hakan.
Ba don bashi da gatan samun ta ba, sai don yana ganin hes not worth enough ga mallakar ta matsayin mata, in yayi laakari da tarin aibubbukan sa.

Maimartaba ya kira Fulani ta wayar hannun sa, suka yi magana ya aje, ya dubi Yarima wanda jikin sa ke ta (tsuma) ya kasa nutsuwa a waje daya, ya zama very upset, bai taba ganin dan sa Sageer cikin kwatankwacin irin wannan halin ba.. daga haihuwar sa har girman sa. Wanda ke nufin....(already Sageer na son Sa'adatu)!!!

Ba abin da ya furta a zuciyar sa sai godiya ga Ubangijin talikai, ya ce da Sageer a hankali cikin muryar sa ta girma da sanyawa dan adam nutsuwa, yana murmushin kasaita irin nasa ta kyakkyawan gashin bakin sa da farin gemu ya zagaye;

Be a Prince!". (Wato ya koma Yariman sa).
Yareema ya dafe goshin sa yana yar dariya da jerarrun hakoran sa bakidaya a waje, wannan ma wani abu ne da Mai Askira bai taba gani ba, iyakacin sa murmushi ga duk abinda yayi impressing din sa, sannan ya kuma koma cikakken Yariman sa ta hanyar kokarin sarrafa kan sa da komawa cikin nutsuwar sa.
Sai ga sallamar Sarauniya Fulani Bilkisun Askirama cikin kwalliyar ta ta kasaita, ta shigo ta kofar da suka saba shigowa bangaren Askirama ita da sauran matan sa, kowacce akwai kofar da ta bulla unguwar ta, zuwa turakan Mai Askira. Takun ta kadai abin kallo ne ga mijin ta.

Yarima na ganin shigowar ta ya dukar da kai kamar tsohon da ya yi wa sarki karya. Surukuta sosai yake nunawa yau ga Bilkisu. Bai taba jin kunyar ta matsananciya ba irin yau. Kafin zuwan wannan ranar, jin ta yake kamar Yayar sa Yaa Maira, ba matar mahaifin sa ba.
Alal hakika yana son matar nan ba tun yau ba, sau-tari, mantawa yake kishiyar Ya Gumsu ce sabida kirkin ta, mantawa yake da duk wani sabani da ke tsakanin ta da mahaifiyar sa sabida son da yake mata da kulawar da itama take bashi. Ashe Allah ya rubuta Kakar yayan sa ce masu zuwa nan gaba cikin kudurar Ubangiji.
Jinin su ne zai zo ya cakude wuri guda ya kara binding din su together. A can gaba. Ya kara dunkule su matsayin iyalin Sarki Yusufu Mai Askira. Ya kara nutsuwa a wurin da yake tankwashe zaman Rakuma akan kafafun sa, sannan ya gaishe ta da sassanyar murya, bayan ta zauna kusa da Mai Askira tana zolayar sa.
Ango! Ango ka sha kamshi.
In ji Fulani cikin murmushi.
Maimartaba ya juya gare ta yana tambayar ta,
“Fulanin Askira Me ku ke shiryawa ne game da biki?
Fulani Bilkisu ta gyara zama,sannan ta kaskanta murya cikin yanayin ladabin da Askirama kadai take yiwa magana da shi ta ce.
Alanguburo, ai ni rabon da in ga Saade tun jiya da na gaya mata. Ta shige daka ta kulle kofarta, watakila idan ta ji mutanen Tsanyawa sun zo ta bude, kuma dai dama bukukuwan gidan nan Ya Gumsu ce ta ke tsara su ga shi kuma tana fushi da ni a kan laifin da babu ruwa na.
Maimartaba ya ce, Zan turo Yaa Maira (babbar yarsa) ku tsara komai, Murjanatu ma tana kan hanya za su zo su same ki. Wannan kiran kuma na Yarima ne ba nawa ba, shi yake son ganinki, zai bi ki unguwarki na ce ya bari in kirawo ki nan, na ga yana ta bare-baren jiki kada ya je ya yi abin kunya a gaban bayi.
Dariya Fulani ta yi, shi kuma Yarima ya kara dukar da kai, murya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login