Showing 15001 words to 18000 words out of 77635 words
bari kiji inma akan bikin sane shiya sani hakan be dameni ba"ai yace yaji yagani ko?"iyakata ido"ko kabeer dake da dukiya be jajibo aureba sai shi dake talaka"shiru kawai meenah tayi aranta tana yiwa mahaifiyar tata addu'ar shiriya....
yah Abdul kuwa gidan su jidda ya nufa"yana isowa yatura yaro a mishi sallama da Abba"yaron na shiga gidan bilkisu na fitowa zata tafi islamiya"had'a ido sukayi da ita....gaban yah Abdul ya buga!be tab'a tsayawa yakalletaba sosai sai yau"bilkisu islamiya zakije?"yafad'a cikin tattausan muryanshi"Eh ina kwana?"lafiya qlau yasu ummi?"suna lafiya"to masha Allah saikin dawo ko?"kanta kawai ta gyad'a masa ta wuce"yabi bayanta da kallo"yanajin inama ace jiddace keda nutsuwar bilkisu"saidai bakin alk'alami yariga ya bushe"ko mata sun k'are aduniya yarage jiddace kawai bazai auretaba..... Abdul kaine da safe haka ?"Allah yasa dai lafiya"cewar Abba"yah Abdul yayi k'asa da kansa yaduk'a yagaishesa"ya amsa suka zauna kan dakali"Ahankali yah Abdul yace"da farko baba ina mai baka hak'uri da abinda zan fad'i yanzun"abubuwa mararsa dad'i sun faru ajiya tsakanina da jidda"da kuma wani d'an siyasa dake son ya aureta.....kaf yasanar masa komai kafin yad'ora da fad'in sbd haka gsky Abba na hak'ura da auren jidda"Allah yahad'a kowa da rabonsa na alkhairi"aganina rabuwa da ita shuyafimun sauk'i"sbd ta zab'i abin duniya akaina"an cimun mutunci da gayamun mgn sbd ina talaka"bayan kowa anan zai samu kuma yabari anan"ni bana kwad'ayin komai "zanje nasanarwa iyayena komai"nasan kayi k'ok'ari wajen kula da tarbiyyar jidda Abba amatsayinka na k'anin mahaifin ta"amma tayi nisa ason duniya da abinda ke cikinta"sbd haka na hak'ura da ita...ajiyar zuciya Abba yasaki yana fad'in banga laifinkaba Abdul"lalacewar tarbiyyar jidda dg mahaifiyarta ne abin"banine na haifi jidda ba ina k'anin ubanta amma banida k'ima awajenta "yadda mutumin nan yamaka nima haka yamun"na nuna masa bazan aminceba"yagayan mgn son ransa da fad'in banine na haifi jidda ba"zata iya bujuremun"sbd haka ni zan share maka hawaye Abdul"in har kana son y'ata bilkisu! wlh nabaka ita"hidima baza'a fasaba nan da sati 2 za'a d'aura auren ku da ita kamar yadda sauran kwanan bikin yarage"idan har baka son bilkisu karka b'oyemun komai Abdul kasanarmun"nasan dai dg wajenta tabbas bbu matsala sbd bilkisu nabin umarnina dg ita har mahaifiyarta........✍️
yanzun zamu fantsama a cikin labarin ba'a fara komaiba"yi hanzarin biyan naki domin adama dake"bbu nadama ko cizon yatsa atafiyar....
shin yaya Abdul zai amince da auren bilkisu har yafara sonya ko kuwa??
Anan gaba jidda da Alh duniya zasu mallaki juna ko kuwa? idan sun mallaka mezai faru??
magajiya zatayi nadama agaba itada goggo??
shin yaya jidda zataji idan taji k'udurin Abba na aurawa yah Abdul y'arsa bilkisu?
bilkisu zata amince da auren yah Abdul har ta soshi??"
yaya kuma zaman yah Abdul da matar aurensa zai kasance agidan goggo??
jin amsoshi wa'annan tambayoyin na a paid grps in sha Allah maza garzaya kibiya ta nan kar ayi babuke👇
wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number👉2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kira❌
Y'an nijar kutuntub'i wannan n👉 +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f
dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyaba
......... Nauyayyar ajiyar zuciya yah Abdul yasaki k'irjinsa na bugawa da kansa"kasa d'ago kansa yyi balle har ya kalli Abba"yasan tabbas yanada matsala na buk'atar yayi aure ayanzun"amma beso ya auri wacce bata sonsa.....kayi shiru Abdul?"kansa ak'asa yace"Abba nagode sosai da karamcinka agareni"Allah yasaka da alkhairi"na amince da auren bilkisu"Abba na murmushi yace"Alhmdllh! nayi hakane dama sbd na share maka hawaye Abdul"dan Allah ka rik'e bilkisu amana"ban tab'a bata damar kula wani d'a namiji ba"in sha Allah Abba"zan wuce gida"to shikenan bama saika sanarwa magabatanka komai ba"tundai aranar za'ayi komai kamar yadda suka sani"dato ya amsa ya mik'e tsaye yanajin kansa kamar zai rabe biyu"Abba yabishi da kallon tausayi"aransa yana yiwa magajiya da jidda addu'ar shiriya.....yah Abdul kuwa kai tsaye gidan musa yanufa sbd yasan a irin wannan lokacin yana gida"har ransa shidai baya jin son bilkisu sbd asali ko fuskarta be saniba"yadai amsane sbd bbu dad'i mutum yanuna zai maka irin wannan karancin kanuna bakaso"bayan ya iso"wayarsa yazaro yakira musa"bugu 2 yad'aga"gani nan akofar gida kafito zamuyi mgn mai mahinmanci"yana fad'in hakan yakashe wayar yana jingina jikinsa da bango yadafe kansa"ahaka musa yafito yasanesa "yana sanye da farar jallabiya ajikinsa"abokina lafiya?"yafad'a yana kallon Abdul"d'ago kansa yyi suka had'a ido"subahanallahi! mike damunka?"yafad'a cikin damuwa sbd yadda yaga fuskarsa da idanuwansa da har yanzun suke jajir"tamkar bazaiyi mgn ba"sai kuma yace"muje soro pls"okay musa yafad'a yana yin gaba shi kuma yabishi....bayan musa yakoma ciki yadawo da tabarma ya shimfid'a musu suka zauna"yah Abdul cikin wani yanayi na zafin zuciya da b'acin rai yashiga korawa musa bayanin abinda ke faruwa"harda auren bilkisu da Abba yabashi...kafin yad'ora da fad'in nazo wajenka ne neman alfarma musa"kaje kasanarwa Abba yayi hak'uri yajanye aurena da bilkisu"bazan iya auren wacce bata sona ko bana soba"sannan asali ni ko fuskarta ban tab'a gani ba"kawai abinda na fahimta banida sa'a musa arayuwa"naji natsani duk wata mace sbd abinda jidda tamun...amamakin yah Abdul sai yaga musa yasaki wani shegen murmushi yana zaro wayarsa yana dannawa"kawai ya mik'a masa wayar yana fad'i duba ka gani"amsar wayar yayi yaga vedio ne"jiddace cikin wasu y'an iskan kaya ta fito dg mota itada Alh duniya sun shige cikin hotel!tsaki yaja yamik'a masa wayar"musa yaja ajiyar zuciya yana fad'in tuni labarin komai na sauyawar jidda yadawomun akunne Abdul"ta yadda Asee baby k'awarta da babawo suka lalata rayuwar ta"ayanzun haka jidda tazama hamshak'iyar y'ar bariki"amma ab'oye takeyi"aganinta bbu wanda yasani"bariki fa kace musa?"k'warai kuwa"naso na ankarar dakai Abdul"amma na fahimci kayi nisa a soyayyar jidda"bazaka iya rabuwa da itaba"k'ilan silar aurenku da ita ta shiryu" wannan tunanin yasaka na b'oye maka"innalillahi wa inna ilaihir raju'un! cewar yah Abdul cikin wani yanayi yana dafe kansa"yanajin wata sabuwar tsanar jidda aransa......gsky ka bani mamaki Abdul! muddin ka bari bilkisu ta sub'uce maka zakayi babban kuskure da nadamar yin haka arayuwarka"sannan kayiwa Abba butulci! domin akunya yafitar dakai yamaka auren huce haushi"maimakon ka amsa da hannu biyu" ka bama bilkisu kulawa da nuna soyayya kodan sbd jidda taji haushi" sai ka kuma nuna zaka wofintar da karamcin da aka maka??"haba Abdul why?"musa bazan iyaba"muddin na aureta to banfa rabu da jidda ba"ko gidana zata iya zuwa na ganta"ni kuma na tsaneta yanzun"amanata dataci taje itada Allah"zanyi k'ok'arin Allah yafitarmun da soyayyar ta araina"shikenan tunda bakajin shawara"nidai bazanje nayi masa mgn ba saidai ka tura wani"Inda nine kai nasamu wannan damar zanyi godiya ga Allah"domin bilkisu nada nagartattun kyawawan halaye"antabbatar tun dg gobirawa zuwa Alkanchi babu yarinya nutsatstsiya mai tarbiyya da kamun kai"had'e da ilimin addini kamarta"nima tabbas ban tab'a ganin fuskartaba amma ai kai ba kyau yaka mata ka dubaba"halayenta na k'warai zaka duba"dukda raina yana bani zakayi mamaki idan kaga fusjarta"itama jiddan ai ba wani kyaune da itaba"hasken bleeching ne dana make up"amma kaje kayi tunani"nidai shawarata agareka kayi hak'uri ka rungumi kaddarar ka Abdul"in sha Allah wata ran komai zai wuce"bbu abinda ke tabbata arayuwa"nasani "kaima kasani kana buk'atar aure "to tunda kasamu ai sai kayi ko?"shiru kawai yah Abdul yayi"sbd yama rasa ta cewa"har ransa badan yasoba ya amince da wannan auren"saidai ance shi mai shawara aikinsa baya b'aci"cikin nutsuwa da sanyayyar muryansa dake nuna raunin zuciyarsa yace"shikenan musa zan wuce gida"Allah yasa haka shine yafi zama alkhairi agaremu bak'i d'aya"yauwa abokina abinda yaka mata ka fad'a kenan"zuwa jibi in sha Allah sai muje gun bilkisun muji dame dame zasuyi na event d'in biki itada friends nata??"kaga dama kana cewa abugo cards"nace ka saurara"da anbugo da munyi asaranshi"babu wata bidi'a da za'a yi musa"yini kawai sai wa'azi ko walima idan zatayi"abinda Allah yahore zamuje abata itada k'awayenta"to amma zancen lefe ai ita za'a barmawa ko?"Eh ina ga"cewar yah Abdul yana tashi"musa na murmushi yace"ka kwantar da hankalinka mutumina kafa kusa shiga sahunmu"balle yanzun sanyin damuna akeyi"gwabraye naji ajikinsu"shiru kawai yah Abdul yayi bece komaiba"dan bashida walwalar da za'a yi wata raha"shi saima da musa yayi zancen yatuna da yadda auren yake"gaba d'aya jikinsa asanyaye yake"yasan ba'a k'in shawara ubangiji yasa auren yazama sanadin farin cikin sa....dan Allah kadena tunanin nan haka Abdul"insha Allah duk tsanani yana tare da sauk'i"kaje ka kwanta ka huta"kayi k'ok'arin saka soyayyar bilkisu aranka"insha Allah nan gaba zaka godemun da shawara"kansa kawai ya gyad'a masa yabar soron"musa ya wuce ciki yana fad'in Allah ya kyauta...
Ab'angaren Abba kuwa bayan tafiyar yah Abdul yashiga cikin gidan"kasancewar sahurace da girki tanama d'akinsa tana sharewa yashigo"amsa sallamar sa tayi tana fad'in mlm kadawo?"nadawo sahura amma da babbar mgn"Allah yasa alkhairi ce"in sha Allah alkhairi ce"yafad'a yana zama"itama ta zauna yashiga sanar mata komai"ummi tasaki ajiyar zuciya tana fad'in Allah yasa haka shiyafi zama alkhari"ita kuma Allah yashiryeta"saidai kasan halin d'an yau mlm"karfa yaga kamar sadaka muka bashi y'ar yayi k'ok'arin wulak'anta ta"Abdul bazaiyi hakaba da yatsar Allah sahura" asalima sbd nagartar halayensa yasaka nayi kwad'ayin bashi bilkisu" tunda jidda tayi sakaci yasub'uce mata"wanda ina mai tabbatar miki da cewa" komai daren dad'ewa itada magajiya sai sunyi dana sanin wannan abun sun ciji yatsa"inaso bayan na sanarwa bilkisu ke kuma ki k'ara rarrashinta da bata shawarwari in sha Allah komai zai tafi yadda yaka mata"sannan duk abinda yadace ayiwa amarya ki fara mata dg yau"komai danayi yink'urin jiya jidda na kayan d'aki saina mata"to shikenan mlm"dg haka ta tashi ta cigaba da aikinta......jidda kuwa nacan na baccinta hankalinta kwance"sai wajen 10 am ta farka"indomie da k'wai da tea mai kauri tasaka aka siyo mata wajen mai shayin anguwar"tana gama karyawa ta d'auki zazzafan wanka"tana zuba k'amshi ta fito dg d'akin su"ummi nata iza wutar iccen data aza girki dashi"yyinda magajiya ke zaune k'ofar d'akinta tana sauraron redio" ta dubi jidda tana fad'in" masha Allah jidda nah! Allah yatsaremun ke dg sharrin sa'idnawa masu bak'in ciki damu"dan na gaba yayi gaba wlh"dan wasu ko mashinshinin bbu balle Ayi felek'e"kije Allah yatsare hanya"Ameen umma nah"tafad'a tana murmushi ta fita"ummi dai na sauraronsu sbd halin magajiya ba bak'onta bane"sarai tasan ita take yadawa habaici"murmushi kawai tayi ahaka bilkisu ta shigo da sallama cikin siririyar muryarta"ummi ta amsa tana fad'in kin dawo?"Eh wlh ummi sannu da aiki"yauwa"me yarage nazo natayaki?"bbu komai bilkisu kije ki cire kayan kiyi wanka ki huta"dato ta amsa tana cire hijab d'in jikinta da face mask nata"magajiya nata kallon bilkisu bbu ko k'iftawa"gaba d'aya wani irin zafinta takeji"musammun sbd ta fahimci tafi jidda komai"dg ilimi ,kyau ,iya mgn,ladabi da tarbiyya"dandai ita bata nuna kyawunta"asalima ko k'awaye masu yawa bata dasu"k'awayen bilkisu 2"salima da Amina"wacce salima class mate natace"Amina kuma a islamiya suke"cikin d'aki bilkisu ta wuce ta cire kayanta tazo tashige wanka.....
da rana bayan sallar azahar"bilkisu na zaune d'akin umminta tana Assignment d'in da aka basu a islamiya" ummi ta shigo d'akin tana cewa"ke kije Abbanku nasan mgn dake"haka nan bilkisu taji fad'uwar gaba"dato ta amsa ta d'aura d'an kwali nta ta fita"Ahankali tayi sallama d'akin Abba ta shigo ta zauna k'asa"Abba yayi gyaran murya yace"bilkisu amatsayina na mahaifinki"wanda dolene kimun biyayya"hakan yasa na yanke hukuncin d'aura miki aure da Abdul" sbd jidda ta bujuremun akan bazata auresaba tasami mai kud'i..... d'ago kanta tayi arikice suna had'a Ido da Abban cikin rawar murya tace"ni kuma Abba?"Eh mana"ko bakya sonsa ne?"k'asa tayi da kanta"k'wallah na cika Idonta"itafa wlh tsoron maza takeyi"shiyasa batada saurayi"take b'oye fuskarta bbu wanda ke ganinta.....kinyi shiru?"bazaki fitar dani kunyaba bilkisu?"kayi hak'uri Abba na amince" Alhmdllh! Allah yayi miki albarka"to amma Abba shine yace"zai aureni?"tambayar bashida amfani"kece da kanki amatsayinki na y'a mace zaki janyo hankalinsa gareki"tashi kije"Allah yayi miki albarka bilkisu"in sha Allah nan gaba zakiyi alfahari da wannan auren "kiyi hak'uri da abinda zaki gani ayanzun kinji?"kanta ak'asa ta amsa da to gabanta nata fad'uwa"wani irin mugun tsoron yah Abdul d'in ya d'arsu aranta"jikinta asanyaye ta wuce d'akin ummi"tana shigowa ta fad'o jikinta tana kuka"ke lafiya kike kuka?"ummi Abba zai auramun saurayin Anty jidda"bayan baya sona kuma"ni kuma bana son aure y'ar yarinya dani"dubi shashashar yarinya"miye aibun aure?"to kima dena wannan zancen kina jina?"tafad'a tana janyeta dg jikinta"kafin taci gaba da cewa"zancen so dakike mgn bilkisu da kanki zaki janyo hankalin Abdul wajenki yasoki"ta hanyar kyautatawa da faranta masa rai"kina dai ganin yadda nakeyiwa mahaifinki biyayya inaso kima fini bilkisu"ki manta da cewa yatab'a son jidda"kiyi k'ok'ari wajen mantar dashi ita"ki zauna tsakaninki da Allah dashi"in sha Allah kece da nassara"nasan zakice batun karatunki" anan gaba in Allah ya amince saiki cigaba bilkisu"islamiya kuma Abban ki zai masa mgn week end zaki cigaba da zuwa"amma karki koma kuka"kuma karki yarda ki nuna masa k'iyayya kina jina?"dato ta amsa tana share hawayenta"duk idan ta tuna nanda 13 days ta zama matar aure sai gabanta yafad'i"ayinin ranar nasiha da shawarwari ummi ta yini tana bama bilkisu"wanda hankalin bilkisun yad'an kwanta amma k'asan ranta tana tsoron auren....
***************
tunda wannan al'amarin yafaru yah Abdul yadage da addu'ar zab'in alkhairi"har istihara yayi amma alkhairi yake gani ga auren"hakan yasa hankalinsa ya kwanta"saidai yayi shiru be sanar kowa nasa ba jidda bace amaryar"yabari in an d'aura auren kowa yagani"har yanzun idan yatuna da jidda shi kawai yasan meyakeji"addu'a kawai yakeyi Allah yafidda masa sonta aransa"duk idan yatuna da bilkisu sai yaji fad'uwar gaba"ahaka aka shud'e kusan kwana 5"wanda ayau saura sati 1 daidai d'aurin auren su da ita"jidda kuwa kwana 3 da suka wuce Alh duniya yaturo magabatansa sun kawo kud'in neman aure"Abba kuma ya amsa sbd wasu dalilai"an basu rana nanda kwana10 su dawo asaka biki"jidda kuwa son yah Abdul da sha'awar sa nanan aranta"saidai son abin duniya yadanne komai"har gwada kiran Abdul d'in tayi taga yayi blocking nata"ayanzun haka Alh duniya yasiyawa magajiya gida had'add'e ,ita kuma jidda yasiya mata mota"gaba d'aya kanta ya Ida fashewa"duniya ta dawo musu sabuwa"jiya Alh duniya yazo har nan gidan yagaisheda magajiya"yajibgo siyayya iri iri yakawo mata"amma bbu abinda ta d'ibarwa sahura abiyar zamanta"sai habaici kawai take saki atsakar gida"tun wayewar safiyar yau magajiya keta aikace aikace ita da wata k'anwarta atine"sbd yau itace keda girki"suna atsakar gidan da marece yaro yayi sallama yana fad'in ance bilkisu tazo inji Abdul"ummi data fito dg bayi tace"gata nan zuwa"azabure magajiya tace"wane Abdul d'in wai??"banza ummi ta mata ta wuce d'aki"umma taja tsaki tana fad'in"takara za'a yi damu kenan?"ada ko kare bai zuwa sbd yanzun anga y'ata zata auri mai arzik'i shine itama zata fara fita fira"yo Allah natuba ai naga yayi gaba na baya sa labari "bazata tab'a samun kamar miji irin na jidda ba wlh....afusace ummi ta fito dg d'akin tana fad'in kinyi kuskure dakika fad'i haka magajiya! Ahaukanki mai kud'i shine kad'ai miji nagari?"kicanxa tunani"niba kwad'ayayya bace irinki"burinah y'ata ta auri d'an k'warai mai tarbiyya ba mai tarin dukiyaba"wanda watak'il wasu masu kud'in bama ta halattacciyar hanya suka sammesuba....ahh dole kice haka mana tunda da alama matsiyacine wanda ya aiko yana sallama da y'ar taki"cewar magajiya cikin d'aga murya"ummi ta nufi d'aki tana fad'in na miki u zurin jahilci da kwad'ayi nadamunki"bilkisu data fito dg d'akin ta girgiza kanta ta nufi k'ofa"tana sanye da hijab har k'asa light blue"tanata k'amshi tasaka plate shoes atattasan k&afanta"asoro ta saka face mask"sbd tafiso saima ta aureshi yasan fuskarta"yah Abdul da musa na zaune kan dakali"sun sha gayunsu"dan musa tursasa mutumin naku yayi yad'auki wanka"harda sabon aski da gyaran fuska aka masa"wanda ba k'aramin kyau yayi ba"yahad'e cikin yashi bak'i riga da wondo"kansa bbu hula"fuskarsa bbu walwala"cikin siririyar muryarta ta musu sallama"musa dake dg farko ya amsa yana fad'in ranki yadad'e amaryarmu"dan murmushi tayi tana cewa"ina wuninku??"tafad'a tana satar kallon yah Abdul...aikuwa yajuyo da nufin ya kalleta yaganta da face mask"d'aure fuska yayi yana kauda kansa yace"lafiya qlau yasu ummi?"kasan ransa kuma yana cewa"meyasa yarinyar nan bataso aga fuskarta?"kodai tanada wata matsalane a fuskan?"horn d'in motar dayaji yasaka yakalli gefensu"wata farar motace tayi parking"aka bud'e driver sit jidda ta fito dg ciki"ta dad'e da eye glass bak'i afuskarta"tana sanye da atamfa riga da siket sun kamata"gabanta yayi wani mugun fad'uwa sbd ganin datayi bilkisu tsaye agefensu musa da yah Abdul"wanda yah Abdul keta kallon bilkisu yana murmushi da gayya sbd ganin jidda da yayi"cikin rufewar ido da son ta gane miye ma'anar tsayawarsu atare ta nufesu.....✍️
wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki ta what's app n d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika fitarmun Allah ya isa ban yafeba
......Tunda jidda ta doso wurinsu musa yatsareta da ido sbd yaga meye zatayi idan tazo?"yah Abdul kuwa nunawa yayi kamar ma be gan taba"cikin isgili da rainin wayo ta zare eye glass d'in fuskarta tana kallon bilkisu tace"ke miye kikeyi anan?"ko kuwa cusa kai kike Inda bakida muhalli?"da mamaki bilkisu ke kallonta kafin tace"abinda kika aiko ni yi shi nakeyi"ta fad'a agadarance dan itama bata d'aukar raini"cikin tattausan muryanshi mai dad'in amo yace"my sweet billy bance ki koma mgn ba..sweet billy fa kace my Abdul?"cewar jidda tana zaro ido tana kallonsa da mamaki"musa yakece da dariyar rainin hankali"yah Abdul yadubeta yana yatsina fuska kamar yaga abin k'yama yace"karki koma kiran wannan sunan agaban matata nanda sati 1 in sha Allah"ke bakiji kunyar fad'in my Abdul ba agabanta?"koda yake banyi mamakiba sbd jakar brain ce dake"yafad'a yana jan tsaki"still musa na dariyarsa"bilkisu kuma batayi mgn ba"jidda kuwa sosai taji ta muzanta awajen"kamar ta tsaga k'asa tashiga haka taji"ga wata iriyar zazzafar soyayyar yah Abdul datakeji aranta"doguwar tsuka yakoma ja akaro na biyu"yana duba agogon dake d'aure adamtsen hannunsa kafin yace"musa muje kawai anjima madawo muyi mgn"tunda nayi bak'in gani yanzun banida sukuni sai zuwa anjima"musa na k'ok'arin mgn jidda tabar wajen da sauri ta shige cikin gidan"jikin bilkisu yayi sanyi"saidai batace komaiba amma tasan laifin jidda ne"amarya zamu wuce inji