Showing 66001 words to 69000 words out of 77635 words
"kece babban alkhairi arayuwata"bazan miki k'aryaba na tsani jidda tsana mafi muni"sbd miyagun halayen ta"duk macen da zata nuna tafison abin hannunka"ko kuma sbd kyawunka take sonka wlh ba macen dazaka so bace"sbd zaka iya rasa kud'in"sannan kuma zaka iya rasa lafiya duk ta gujeka....hakane yah Abdul"komai yafaru arayuwa haka Allah yatsara"yanzun haka Anty jidda dai nacan wajen ummanta batama lafiya tayi accident ta karye k'afa"nima jiya yah Anas da mukayi waya dashi nakeji"tab'e baki yah Abdul yayi irin ko ajikinsa d'in nan " saima cewa yayi Allah ya kyauta"tashi ki kwashe kayan nan kizo ki shiryani na tafi masjeed dg can sai naje wajen Alh" dato bilkisu ta amsa tana tashi ta kwashe kayan ta fita"aranta tana mamakin irin tsanar da yah Abdul yayiwa jidda....fitowa sukayi dg cikin d'akin bilkisu na rik'e da hannun sa"yanata zanga wani irin fitinan nan k'amshi"yayi kyau har yagaji"yana sanye da jeans dark blue da t shirt red"yatsuke k'ugunsa da belt bak'i"takalmi sawu ciki suma bak'i yasaka"agogo ma haka"fuskarsa wasai shimfid'e da tattausan murmushi"bilkisu nata wani b'ata rai dan sosai yamata kyau"da kanta kuma duk ta masa wannan shirin"my billy bazaki dena wannan kishin bako?"inajin dad'in yadda kike kishina amma banaso abin yayi worse"duk zafin kishin mata maza sun fisu"fad'amun naji miye kikeso na miki tsaraba dashi?"yafad'a yana rungumota ajikinsa suka tsaya asoro"kanta ak'asa tak'i mgn"kinga in bacin meenah na wajen goggo da tazo ta tayaki zama ko?"amma idan kin gama wanka ga islamiya kuma ga fitarmu duk zamuyi zaki rage kad'ai ci"yafad'a cikin rarrashi"bilkisu har ranta kishin mijintane amma yadda taga yadamu da ita yanata rarrashinta saita sake sosai harda dariya suna wasansu"saida wayarsa tayi ringing sannan yamanna mata kiss yafita abinsa"tana masa adawo lafiya ta rufe gidan"koda ta koma waya tayiwa ummi aturo mata khalifa yatayata fira"anan ummin ke tayata murnan samun aikin yaya Abdul....
yah Abdul kuwa atare da Alh mukhatar sukaje har wajen aikin nasu yayi signing yaga office nashi"da time d'in zuwa dana tashi da ranakun meeting"komai dai akan tsari yake"dg nan sukaje da Alh mukhatar har gidan goggo yaganta da jiki yamata alkhairi mai yawa"sannan sukayi sallama da yah Abdul....
Ab'angaren kabeer kuwa yanason cigaba da zama da laurat ne kodan sbd ace y'ar gidan masu dashi yake aure"be kuma damu da halin da goggo take aciki ba"aganinsa k'ilan ma goggon ta kirashi ta bashi hak'uri musammun idan taga kayan abincinsu yak'are"amma sai yajita shiru"barikinsa yakeyi bai dena ba"idan yakira laurat bata d'auka"sai zagi da cin mutunci take turo masa atext message"shi kuma yanaso ta komo ya saitata"kusan sati ukku basu tare"ahaka iyayenta sukayita nemansa yazo yabada takarda"amma yak'i zuwa dg k'arshe suka makashi kotu"yana wajen aiki aka kai masa sammaci"adole ranar shari'a yaje yasaketa saki 2 akotu"dama tuni sunzo sun kwashe kayansu"tun dg lokacin yaci gaba da kai mata a gidan nashi yana kwana dasu....ayau friday kabeer na office nashi yanata danne danne a laptp aka kirashi ta waya"yaja tsaki sbd ganin me gadin gidansa ne"cikin izgili yad'aga wayar yana fad'in wai lafiya zaka dameni da kira??what?? yafad'a akid'ime yana mik'ewa tsaye cikin tashin hankali yana cewa"garin yaya gobaran yakama?"tsaki yaja yakashe wayar yafita dg office d'in aguje yaje ya hau motarsa ya nufi gidansa......abin tashin hankali har bakin get d'in gidan ciyakeyi da wuta"gaba d'aya kabeer yagama rikicewa"yayiwa y'an kwana kwana waya"saidai kafin su iso wutar tayi aiki sosai agidan"abubuwa sun kone sai katangu da filin tsakar gidan"kamar kabeer yazauce"sbd komai nasa na gidan"harda kayan sawarsa da takardunsa"da komai"Allah yaso yataho da motarsa"har ATM card nasa na gidan"gaba d'aya sabbatu yakeyi kamar tab'abb'e"aranar saidai hotel ya yini ya kwana"abin tashin hankali kuma yana zuwa office washe gari aka bashi takardar kora dg aiki"sbd an kamasu da sace kud'in campany"wanda kuma azahirin gsky babu saka hannun kabeer d'in aciki" amma gashi sunansa yafito acikin wa'anda sukayi satar"d'an k'aramin hauka kabeer yayi"ya gigice yafita hayyacinsa"wani abokinsa yajashi yace"suje gidan wani malami ko akwai taimakon da zaiyiwa kabeer"wanda gaba d'aya kabeer yashiga tashin hankali"dan dg wayarsa sai motarsa da kud'insa 160k dake acc nasa"sune kawai ya mallaka aduniya"ko kayan sawa na jikinsa kawai garesa"bayan sun iso soron gidan malamin suka zauna"kabeer kamar yayi kuka sbd yafahimci malamin ba mashiriki bane"shi yafiso aje Inda za'a masa sihiri amaidashi gun aikinsa"bayan sun gaisa abokin kabeer mai suna is'hak'a yayiwa mlm bayani"mlm yayi shiru yana kallon kabeer kafin yace"akwai wanda kasamu sab'ani dashi"d'an uwa ko iyaye ko mata ko wani aboki??"mlm matata mun rabu kwanaki"d'an uwana kuma mun samu sab'ani dashi amma mun shirya"shine nake zaton koma shine yamun asiri... subahanallahi bbu kyau ZARGI"bayan shi bbu wata matsala?"kuma miye dalilin rabuwarku da iyalin naka??bbu wani b'oye b'oye kabeer yasanar mlm sbd yana neman mata taso su rabu Kumar har gida taje ta daki mahaifiyarsa"amma be d'auki mataki ba"shine mahaifiyar tasa ke fushi dashi.... subahanallahi! ka tabka babban kuskure yaro"uwa ta wuce wasa in har kanason ganin daidai arayuwarka dole kabi iyaye"musammun uwa ,ka kuma kyautata mata"bbu shakka abinda yafaru dakai nada alak'a da fushin mahaifiyarka akanka"idan bakada ilimi game da mahinmanci uwa kaje ka nemo"shawara ta gaba shine kaje ka nemi gafarar mahaifiyar ka"sannan zancen neman mata katuba zuwa ga Allah kadena"ubangiji zai yafe maka"sannan idan baka saniba kasani uwa nada matuk'ar mahinmanci"saika bita kasamu aljannah"akwai wata k'issa ta wani sahabin annabi to (S A W) "wata ran mutumin nan ciwon ajali yakamashi aka dinga bashi kalmar shahada amma wlh yakasa furtawa gashi yayi nisa rai yakusa fita"kuma antabbatar mutumin kirkine shi mai tsoron Allah"annabi yatambayi mahaifiyarsa na raye?"akace Eh"har gunta Annabi yaje yatambayeta ko wannan d'a nata yatab'a mata wani laifi komai k'ank'artarsa??"tace ah ah yana kyautata mata itadai"akayita mata tambaya can tace"akwai dai abu guda dayake mata aranta batajin dad'i amma bata d'aukesa wani laifiba"annabi yace miye abin?"matar tace"duk lokacin da zaiyi musu sutura tofa zai kawo suturan matarsa tafi nata kyau da tsada"hakan na sosa ranta"tana tuna lokacin da takeda kuruciya tasaka sabbin tufafi yab'ata mata da kashi ko fitsari amma shine yake banbanta matarsa fiye da ita"wannan shine kawai abinda yamata dabatajin dad'i"Annabi yace tayafe masa"aikuwa tayafesa wannan sahabi ya amshi kalmatush shahada yayi.....meka fahimta awannan k'issar?"cewar mlm yana kallon kabeer"muddin kanaso kaga daidai da cigaba arayuwa tofa dole kabi iyayenka musanmun uwa"kuma yadace ita matar taka karabu da ita kodan sbd abinda ta aikatawa mahaifiyar ka....jikin kabeer asanyaye ya amsa dato sukayiwa mlm godiya"is'hak'a yamasa alkhairi suka fito"suna fitowa is'hak'a yace"kaga irinta ko kabeer?"wlh katuba kadena aikata zina"na baka shawara tuni kadena bariki kak'i"shikenan katayani da addu'a"sannan zanje yau gidan goggon saina bata hakuri"haka yaka mata kasamu d'aki acan ka zauna kafin kasamu abinyi"dato kawai kabeer ya amsa suka shige mota.....
Acikin kwana 3 kacal yah Abdul da billy sun gama shirya zuwansa office agobe monday"wanda saida bilkisu tasaka rigimar sabbin kaya kala 10 zai siya"kuma da ita sukaje boutique d'in ta zab'ar masa kaya masu kyau"ajiya kuma yah Abdul yabiya kud'i millon 3 da rabi na wani had'add'en get house sabo gal"maishi lalurar kud'i yakamashi yasiyar millon ukku da rabi"amma idan kud'i za'a masa zaiyi million 4"yah Abdul be sanarwa billy ba"yabari sai angama siyayyar komai da sukeyi shida musa wanda za'a zuba agidan"dan soyakeyi kafin k'arshen sati su koma can"sannan ayau yaje ya amso motarsa"dama kuma ya iya driving tuni....tun safiyar yau bilkisu keta jin dad'i sbd yau tagama wanka 40 days cif"sai murna takeyi abinta"yah Abdul da musa nacan zasu amso motarsa"da kanta bilkisu takoma goge kayan nasa ta jeresu a ward rope"ga sabbin takalmi sawu ciki da have cover duk yak'ara siyowa"kusan siyayyar kayan sawa da takalmi 400k yayi"tana zaune atsakar gidan tana latsa wayarta dan yau ko abin sana'arta batayiba"horn d'in mota taji"sai kuma wayarta tayi ringing"sweet heart! shine sunan data gani ya bayyana kan screen d'in wayar"tasaki murmushi tana d'aga wayar"hellow my billy fito kiga motar mu"yafad'a yana murmushi yakashe wayar yanata danno horn"bilkisu na murmushi tace"oh yah Abdul ba sabonba andameni da horn"ta fad'a tana d'aukar mayafin jallabiyar dake jikinta ta zura plate shoes nata ta fito k'ofar gidan.....da wata had'add'iyar mota bak'a k'irar Mercedes C230 tayi cin karo"afili billy tace"wow masha Allah! ta fad'a tana nufar gefen motar tana shafata"yah Abdul na murmushi yabud'e k'ofar front sit yana fad'in zonan ki shigo muyi driving d'in a tare"yafad'a yana mik'a mata hannunsa"nok'e kafad'ar ta tayi tace"wannan sit d'in yamana kad'an yah Abdul"kinsan Allah kizo koni nazo"yafad'a yana tsareta da ido aransa yana mamakin kyawun jikinta"shifa Inda bai santaba zai zata y'ar budurwa ce"tana murmushi ta iso gefensa yakamo hannunta guda yashigo da ita ciki yana azata samqn cinyoyinsa"billy na dariya tanata kallon motar tace"Allah ubangiji yasa alkhairi yah Abdul"Allah yatsare wannan mota tayi kyau sosai wlh"da gske my billy?"eh wlh"kinga yanzun zamuje dake gidan goggo ki ganota da jiki"sai muje gidan ummi"dg nan muje musha ice cream ko? d'an murmushi tayi tace"to bara naje na rufe gidan na cqnzo takalmi da hijab"ah ah bana son wata hijab kidai canzo takalmin"yafad'a yana kissing gefen kumatunta"dato ta amsa tana barin jikinsa ta fito ta wuce ciki"aranta tana mamakin meyasa besan tana yawon saka hijab"ta fahimci duk abinda yashafi wayewa yah Abdul na wajen"turare takoma fesawa"ta sanya hula samqn kanta"sannan ta yafa mayafin rigar"ta canzo takalmi ta d'akko baby nokia d'in ta tasaka a y'ar post nata ta fito ta rufe k'ofar gidan"yah Abdul na zaune amotar yana waya da wani abokinsa"billy ta bud'e gefen me zaman banza ta zauna"yakamo hannunta guda yana wasa dashi yana wayar"itadai tayi shiru aranta tana godema Allah kamar wasa abin"wai wannan motar ta yaya Abdul ce?"my sweet billy yaya dai kinyi shiru?"yafad'a yana ta kallonta"babu komai fa yaya Abdul"okay yanzun idan munje gidan goggo lalle meenah zata miki zuwa ko 3pm sannan yayi sai muje gidan ummi idan anyi la'asar muje amiki gyaran kai...kai bazakaje amaka aski ba?"kinaso amun?"yafad'a yana sakin hannunta yafara bama motar wuta"adai gyara maka fuska dai"to shikenan saiki rakani anjiman ko?"to shikenan tafad'a tana kwantowa jikinsa"kanta agefen kafad'arsa suna fira yana driving d'in"da haka suka iso gidan goggo"aran bilkisu tana tuna rayuwarsu ta baya agidan"wacce bata fatan ko a mafarki su koma rayuwa wannan gidan"bayan yagama parking suka fito yayi lock d'in motar"anutse yah Abdul yakamo hannunta suka jera"ba k'aramin kyau sukayiba"shima dai k'ananun kaya ne ajikinsa"yah Abdul kacikamun hannuna mana"my billy wlh zakija na d'aukeki koki barni"bbu yadda ta iya ahaka suka shigo tsakar gidan da sallama"meenah aguje tazo ta rungume bilkisu tana murna"goggo dai na d'an murmushi kanta ak'asa tanajin nauyin abinda tayiwa bilkisu abaya"wanda kallo d'aya ta musu tasan suna cikin kwanciyar hankali"uwa uba yadda billyn tayi y'ar k'iba da haske"dukda meenah ta rungume bilkisu hannunta na cikin na yah Abdul yak'i cikata"meenah acikamun baby nah hakanan"ina fatan kin had'a komai na lallen??"yafad'a yana janyo billy jikinsa"na had'a yaya ku kawai nake jira"okay kije waje motata na nan ki ganta"kai Alhmdllh! bara naje nagani"cewar meenah tanayin waje"sosai bilkisu taji kunya"tayi dai k'asa da kanta suka nufi cikin baranda Inda goggo ke zaune"kan tabarma suka zauna"goggo na fad'in maraba da bilkisu"yauwa goggo ina wuni?lafiya qlau ya kuke?"Alhmdllh"ya jikin naki?"jiki da sauk'i sosai"masha Allah"yah Abdul sai asannan shima yagaishe da goggo"bilkisu dan Allah zan k'ara baki hak....dan Allah goggo adena zancen tuni komai ya wuce awajena"fatanmu Allah yabaki lfy"cewar billy kanta ak'asa"Ameen yah Allah nagode sosai Allah yayi muku albarka"suka amsa da Ameen cikin farin ciki"meenah ta shigo gidan da fara'a tanata santin motar da masa fatan alkhairi"kafin tace"kiyi alwalah anty billy nasamiki salataf dana gama samiki sai kiyi sallar azahar sai asaka lallen"dan yanzun d'aya saura minti 20"dato billy ta amsa"tana k'ok'arin tashi yah Abdul shima yatashi tsaye yabiyota"meenah dai na murmushi tana kallonsu cike da burgewa"da kansa yazuba mata ruwa abuta"tafara alwalah d'in bayan ta gama ta yarfo masa ruwan hannunta afuska tana masa gwalo suck suka mik'e tsaye"duk meenah da goggo na lura dasu"yah Abdul na murmushi yakalleta yace"haba yarinya zamu had'e agida"kaima fa yah Abdul kana watsamun ruwa in kayi alwallah"bbu ruwana ni zamu had'u"eh naji bbu komai nima na iya mugunta ai"tafad'a tana murmushi"haka yayi daidai da shigowar kabeer tsakar gidan"da alamar ladabi da nutsuwa yashigo"ba kamar abayaba dayake shigowa yana shan sigari.... had'e rai yah Abdul yayi yana nuna masa k'ofar fita da hannu yace"kai! b'atan hanya kayine?"ko kuwa rayuwar ce ta maka k'unci shine ka d'ebo jiki kazo mana anan??"maza ka fita ko kuwa wlh jikinka yaga maka"dan Allah yaya na tuba na bika nabi goggo"ku rufamin asiri ku yafemun dan Allah"yafad'a yana duk'awa gaban yah Abdul"bilkisu tabar wajen da sauri ta nufi parlourn goggo"yah Abdul yahad'e rai sosai yana fad'in magiyarka d'in banza"kai bakana ganin kai kazama d'an iskaba"mahaifiyarmu itace abin wulak'antawa agareka ko?"ah ah wlh nadena kuma na rabu da laurat d'in wlh"yafad'a yana rik'e k'afar yah Abdul yana kuka"goggo dai tayi zaune wani b'acin rai ne ketaso mata"dan yanzun ta tsani koda ganin kabeer"Allah yasa har cikin ranka tuban gsky kayi"cewar yah Abdul yana mik'ar dashi tsaye yace"kaje ka duk'a ka bama goggo hak'uri da alk'awarin bazaka koma b'ata mata rai ba"jiki na kirma kabeer yanufo goggo yana kuka kamar k'aramin yaro"karka k'arasomun a nan dan ubanka! saida duniyar ta juya maka baya sannan ka tuna dani zaka zo wajena?"ai na d'auka banida daraja awajenka laurat da uwarta na haifa ma kai"to Alhamdllh! bakai kad'ai na haifa ba"wanda ada nake k'i nake tozartawa ashe shine wanda zai adanani"ka d'auke k'afa agidan nan fin wata guda"kana ganin ga goggo me bakin kwad'ayi k'ilan kiranka zanyi na rarrasheka ko?"to kayi kuskure"kaduba gidan nan kagani ban rasa komai ba"jikina Alhmdllh! me gyara yafad'a nanda sati 6 zan cigaba da tafiyata"to goggon daka sani ada ba ita bace yanzun...kuka yafashe dashi yarik'e hannayenta"ta fisge tana harararsa"yah Abdul dake tsaye yace"goggo kiyi hak'uri dan Allah kiyafe masa"bazai koma ba yayi nadama ta gsky da alama"shikenan Abdul tunda kasaka baki"na yafe masa ubangiji yashiryamin ku"shi kuma yabashi mace ta gari kamar matarka"dukda da wuya yasami kamar bilkisu"amma wlh muddin kanason zaman lafiya dani tofa dole kayiwa Abdul biyayya"in sha Allah goggo"yafad'a yana gyara zamansa yazayyano musu halin dayake ciki"da zuwansa wajen malami da nasihar daya masa"innalillahi wa inna ilaihir raju'un! kaji dai darajar uwa ko?"to ubangiji yasa haka shiyafi alkhari"Inda rabo gsky tayi halinta saisu mayar dakai"bariki kuma karka fasa idan ka d'akko HIV kai yashafa" cewar goggo tana tab'e baki"wlh nadena goggo da gske"idan na sami mata aure zanyi"dan Allah yaya ka rok'ar mun gafarar matarka bisa abinda nayi yink'urin yimata abaya"tab'e baki yah Abdul yayi dan haushin kabeer yaji"yana ganin kamar yanzune abin yafaru"Allah ya yafe mana gaba d'aya"kaje ka bud'e wancan d'akin ka gyara ka zauna aciki kafin Allah yasa aga me gaba zatayi"sannan nima nasami aiki"Alhmdllh! yaya natayaka murna Allah yasa alkhairi"ko motar dana gani awaje takace?"Eh in sha Allah"masha Allah Allah yatsare"ya amsa da Ameen"goggo tasanarwa kabeer key d'in part d'in su Abdul na kan fridge yaje ya d'auka"ya amsa dato yanufi wajen fridge yad'auka ya wuce"yah Abdul yanufi parlourn fuska asake yasamu har billy tayi sallah anfara samata lallen"yana dg tsaye bakin k'ofa yace"my billy sannunku"tana murmushi ta dubesa tace"kaje kayi sallah kadawo"to shikenan gimbiya am gama"duk sukayi dariya itada meenah"yah Abdul yajuya yafita dg gidan......goggo kuwa kabeer ta k'walama kira yazo yataimaka mata tayi alwalar sallar azahar....
Ab'angaren su jidda....✍️
wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki ta what's app n d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika fitarmun Allah ya isa ban yafeba
....... Ab'angaren su jidda suna isowa anguwar gobirawa kai tsaye gidan Abba sukayiwa tsinke"gaban magajiya nata fad'uwa ahaka ta tura jidda dake kan wheelchair suka shigo tsakar gidan da sallama"ummi na tsakar gidan tana alwalar sallar la'asar"Abba kuma yatafi masjeed na anguwar yayi sallah"d'ago kanta tayi cike da mamaki sbd jin muryar magajiya"kallo d'aya ta musu itada jiddan ta d'auke kanta tacigaba da alwalah"tana tuna ranar dataje ganin lefen jiddan magajiya taci mata mutunci"dama kuma sunsan abinda yafaru da jiddan"ummi na gama alwalah d'in ta mik'e tsaye ta amsa sallamar su batare data kallesauba"suna ta k'arema gidan kallo"magajiya tayi tsaye tanata kallon k'ofar d'akinta nada dake a rufe"ina wuni ummi?"cewar jidda"lafiya qlau"magajiya ina wuni ya gida??"magajiya jiki na kirma ta amsa tana fad'in mlm na nan dan Allah?"ah ah amma k'ilan yashigo yanzun idan angama sallah"dg haka ummi ta wuce d'akinta"magajiya ta zauna kan takalminta tayi tagumi"dg ita har jiddan kowane da irin kalar tunanin dayakeyi"ahaka ummi ta fito tsakar gidan ta zauna kan tabarma tana lazimi"kusan minti 5 da zamanta"Abba yashigo rik'e da ledoji Ahannunsa"saidai yana ganin su magajiya ya gimtse fuska"be koma kallon gefensu ba"ummi ta amsa sallamar sa tana masa sannu da zuwa tazo ta amshi kayan hannunsa tanufi d'akinta"Abba na k'ok'arin binta magajiya tayi saurin cewa mlm wajenka muka zofa"fuska ad'aure ya juyo yanadaga tsaye yace"ina jinki meke tafe daku?"nabaku minti 5 ku fad'amun abinda ke tafe daku ku ficemun dg gida"k'wallah ta zuboma jidda"magajiya tayi k'asa da kanta tace"mlm dan Allah gafaranka muka zo nema nida jidda"nasan kasan meya faru da ita"amma rashin zuwanka dubata nasan yanada alak'a da kuskuran da mukayi abaya"dan Allah kayi hak'uri ka yafe mana"sannan ka mayar dani d'akina dan Allah.....jidda na kuka tace"wlh muntuba Abba ka yafe mana dan Allah" Alhmdllh masha Allah! ni nayafe muku"kowa yatuba dan wuya tubansa be yiba"ai dama duniya fad'i ce da ita"saida tayi juyin waina dake kika san dani magajiya?"kefa kikace barka za'a miki sbd kin rabu dani"takardar sakinki na nan na ajiye tuni"nakuma sha alwashin duk rintsi bazan bakiba sai kinzo da kanki anan gidan ki amsa"wato ranar da YAU DA GOBE tayi aiki akanki"waye ni awajenku dama zakizo neman gafarata?"duk abinda ka shuka shine zaka girba komai daren dad'ewa"nayi mamakin yadda kukayi saurin nadama da wuri haka"jidda y'ata ce yanzun halak malak sbd mahaifinta muna ciki daya dashi,kuma ya rasu yanzun"amma kinsa ta bujuremun sbd hange dason abin duniya irin naki"duk abinda mijin jindan yamuku yadawomun da irin korar karen daya muku ayau"....kuka magajiya tafashe dashi itada jidda suna bashi hak'uri"ummi ta fito tsakar gidan