Showing 12001 words to 15000 words out of 77635 words
sosai afilin rawar"hannunta kawai taji Anjawo"tana kallon wanda yakama hannun nata taga Alhajin dake mata lik'i ne"d'an murmushi yasakar mata takashe masa ido d'aya"wanda hakan yatabbatar masa ita y'ar barikice"muje dg waje zamuyi mgn"okay tafad'a tana biyosa"yyi saurin dakatar da body guard nasa dan karsu bishi"suna fitowa suka tsaya abakin motarsa"Ahankali yace"y'an mata miye sunan?"cikin kashe murya tasanar masa sunanta"yana murmushi yace"nice name"ni sunana *Alh sulaiman duniya*! d'an zaro ido jidda tayi sbd mamaki"dan tunda suka shigo hall d'in taji marok'a nata masa kirari"cikin k'asa da murya had'e da far da ido jidda tace".......โ๏ธ
wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโ
Y'an nijar kutuntub'i wannan n๐ +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f
dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyaba
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐น๐คฑ๐ปWATA UWAH ๐คฑ๐ป๐น
๐๐ปโโ๏ธ(RAYUWAR ABDUL) ๐๐ปโโ๏ธ
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
Story & written by
mommyn fareesa
free page 17&18
.........cikin k'asa da murya had'e da far da ido jidda tace"masha Allah! miye dalilin kirana anan to?"yana binta da mayen kallo nasu irin na y'an duniya yace"ina son zamuyi wata mgn dake mai mahinmancine"idan bbu damuwa mu shiga mota ko?"yafad'a yana nuna motar"batace komaiba ta nufi motar ya bud'e suka shiga"kalamai da maganganu na banza yadinga fad'awa jidda"atake yafahimci tanada mugun son abin duniya"acikin motar suka aikata sab'on Allah"yakuma tabbatar mata yana sonta da gske"sannan yatura mata million guda a acc nata da alk'awarin gobe su had'u"sosai jidda ta rikice da wannan kyauta tasa tana ganin yanzun gwabnatin Alh magaji yarushe agunta"tajima amotarsa kafin dg k'arshe suka koma hall d'in"ta samu itama Asee baby tayi babban kamu"sai wajen 10:30pm aka tashi dg wajen dinner d'in"jidda tabi Asee gidansu suka kwana"washe gari ta canza kaya ta saka hijab ta nufi gidansu hankalinta kwance"magajiya na d'aki"ummi na tsakar gidan tana wanki wajen 11 na safe"kallo d'aya tayiwa jidda ta d'auke kanta"sbd ko sallama batayiba ta wuce d'aki da ledoji Ahannunta"magajiya dake kwance tayi saurin tashi zaune tana kallon jidda tace"miye abin ki kwana jidda?"kin san dai halin mutumin nan da munafukar matarsa?"sharesu kawai umma"ni yanzun cikin farin ciki nake"nayi babban kamu umma" wanda yamun kyautar da ban tab'a samu ba"gwalo ido magajiya tayi tana cewa"ke y'ar nan?"wlh umma million guda"sune na ajiye na kayan d'akina"ke kuma akwai dubu d'ari 700 danakeso su Ida zama million guda saina siya miki gida"yanzun kud'in mota nakeso natara"tamkar k'aramar yarinya haka magajiya ta tashi tana shewa da rawa"jidda na dariya wayarta tayi ringing"da sauri tace"yi shiru umma zanyi waya"tafad'a tana d'aga wayar sbd ganin yah Abdul ne"anutse ta amsa sallamar sa tana fad'in sweet heart kamar bakajin dad'i ko?"dg d'ayan b'angaren yah Abdul dake kwance kan katifarsa atsohon d'akin musa"yayi saurin cewa"ciwon ciki ne ke damuna"duk yau banj ikiba my baby"wayyo Allah nah"sannu kaji"kana ina ne yanzun?"ina d'akin musa" kinsan tunda aka fara yimana gyara acan na koma" okay ta fad'a tana kashe wayar"ta canza kaya ta dubi magajiya dake gyangyad'i tace"umma zanje nadawo"to shikenan"jidda batace komaiba ta fita"amma aranta tasha alwashin gsky bazata iya zaman takuraba"dama agidan su kenan zasu zauna idan ya aureta?"da sake gsky"ta ayya haka aranta tana nufar anguwar su yah Abdul"kasancewar bbu nisa tsakaninsu cikin few minutes ta iso"lungun da d'akin musa yake anan ta shiga ta kutsa kanta d'akin"yah Abdul na kwance rigingine dg shi sai boxer ajikinsa bbu riga" idanuwansa arufe"alamar bacci yafara d'aukarsa"ido jidda ta tsurawa curarren gashin fafffad'an k'irjinsa zuwa cikinsa"tamkar wata mayya haka ta tsaresa da ido"gaba d'aya jitakeyi tana buk'atar kasancewa dashi....bata tab'a zaton haka yake da k'iraba"Ahankali ta shigo ta zare mayafinta ta kwanta agefensa"hannunta guda take k'ok'arin azawa samqn k'irjinsa.....kamar ance yabud'e ido"yyi hanzarin rik'e hannun"k'amshin jikinta yadaki hancinsa"yyi saurin jaa da baya yana sakin hannunta"yajawo jallabiyarsa dake a gefe yana rufe k'irjinsa zuwa cinyoyinsa masu cike da gashi"my Abdul miye haka kake rufemun jikinka?"befi sati 6 ad'aura mana aure bafa.....cikin tsananin b'acin rai ya d'ago kansa yatsareta da jajayen idanuwansa" cike da jarumta had'e da b'oye yanayin data hadda masa shiga yace"jidda second 5 na baki ki tashi ki bani waje"mekike shirin yi ada?"kina so mu amsa kiran shaid'an ko me?"daza kizo ki kwanta agefena bayan bbu aure atsakaninmu"ki tashi kije karma wani yazo yasameki anan amana wani ZARGI"yafad'a cikin kakkausar muryarsa"kayi hak'uri pls"nadamune shine nazo nadubaka"bazakije ba?"yafad'a atsawace"da sauri ta tashi ta d'auki mayafinta batace komaiba tana d'aure fuska ta fita"zazzafan huci ya furzar dg bakinsa yana dafe mararsa"had'e da fad'in yah salam!meyasa jidda zakizo ki hargitsamun lissafi??"tsaki yaja zuciyarsa na tambayarsa anya yadace jidda tazama matar aurensa??" sbd rashin da'arta yayi yawa! bazan iya rabuwa dakeba jidda"da kaina zan canzaki in sha Allah.....jidda kuwa ranta ab'ace ta shigo gidan"tasamu bilkisu na tsaye abakin k'ofar shigowa tsakar gidan"kanta bbu d'an kwali "tayi parking tumbujin gashinta atsakkiyar kanta"tana sanye da yunifoam nata na skul"dan yanzun exams sukeyi befi saura 2weeks tayi SSCE ba" ta kama kunnan khalifa ta murd'e cikin y'ar siririyar muryarta tana fad'in"ina wasa dakai dan gidanku??"dallah malama gyaramun na wuce"cewar jidda cikin nuna jin zafin bilkisu da hassadarta"bilkisu batace komaiba taja hannun khalifa suka matsa"ummi na zaune kan kujera y'ar tsugunne tana rabon abincin rana"jidda ta wuce d'akinsu....adaren ranar suka shirya da yah Abdul....
***************
kwanci tashi bbu wuya a wajen Allah "ayau sauran 2weeks bikin jidda da yah Abdul"an kammala aikin shashensu agidan goggo"baffa Aminu yakawo masa kud'i 150k yacika yyi lefe"har kukan farin ciki yah Abdul yayi"acikin kud'in yafitar da kud'in sadaki"yakuma Ida had'a lefe dasu"goggo da kabeer ko sisi basu bashi ba"musa ma yataka rawar gani"ayau kuma za'a kawo lefe"wanda mazane zasu kawo lefen"sbd mlm mamman beson bidia shine yatsara hakan"lefen na gidan goggo dayakai mata ta gani"acan za'a d'auka akawo gidansu jidda"wanda magajiya da kawo lefen da rishinsa duk d'aya ne awajenta"hidimarta kawai takeyi"kamar ba ita bace uwar biki"ko tsinke bata siyaba na auren jidda"yyinda itama jidda bata kaiga siyaba sai next week"kuma tanada kudurin haya zata kama musu na get house akaita" amma ba gidansu yah Abdul zasu zaunaba"aganinta ta wuce zama irin wannan gidan"
Atsakanin jidda da Alh sulaiman duniya da Alh magaji"bbu abinda yacanza"kowa tana hud'da dashi"batama sanar musu zatayi aureba"sannan tafi kula Alh duniya sbd yafi sakin kud'i"ayau tun safe take wajensa a hotel suna aikata masha'a"tanaso ta tafi yak'i barinta ta tafi"sbd yau takeso suje wajen bokan dazai musu aiki akan yah Abdul"cike da shagwab'a tace"sweet heart nifa amaryace ! Ayau ma ake kawo lefena! yaka mata ka barni naje....da sauri Alh duniya yatashi zaune yana fad'in da gske kikeyi baby?"Eh mana"tafad'a tana saka kayanta"ni kuma kinga inaso na aureki"sbd danaci kujerar d'an majalissa mutafi Abuja"to ai kaga aikin gama yagama"kinga shi wanda zai aureki yanada kud'i ne?"ah ah takakane kamarni"tab'e baki yayi yace"kice matsiyaci zaki aura kina babbar yarinya?"to zan ganshi naji idan zai barmunke na aura saina biyashi ko nawane"zuwa y'an watanni saina sakeki"saiya aureki"anya zai iya amincewa?"kumafa gsky ina sonshi"tab'e baki yayi yace"iyayenki zasu yarda?"mahaifiyata batada matsala saidai k'anin mahaifina da shine marik'ina kuma mad'aurin aurena" sbd babana yarasu tuni"okay zanje nayi magana da maman"tunda shi zaki iya bujure masa azauna lafiya"gsky nidai bazan fasa auren Abdul ba"ai dama ni bance ki fasa ba"kawai alfarma zaimun yabarmunke Ayi auren dani zuwa bayan wasu watanni saina sakeki "time d'in nayi kane kane akujerata"idan kika amince zan siya miki mota ta million 3"zan baki million 2"sannan zan siyawa mahaifiyar ki gida"sannan zamuje london muyi Honey moon namu...jidda tazaro ido tana fad'in da gske kakeyi sweet heart?"zan miki k'arya ne?"wlh na amince sweet heart"amma pls kamar bayan wata 8 haka saika rabu dani"bazama ki kai yakaba"to amma baka sanarmun kokai waye ba"tab'e baki yayi yace"nasanar miki inada mata2 da yara 8"sannan nasanar dake anguwar danake dana iyayena"miya rage ?"bbu sweet heart"yanzun kije anjima zanzo gidan naku nayi mgn da iyayenki"idan shi marik'in naki yanuna taurin kai" sai nayiwa shi yaron mgn"idan basu yardaba zaki iya bujurewa shi marik'in naki sbd bbu dole"ko baki zai miki bazai biki ba"jidda jiki na b'ari tace"to shikenan my one bara naje sai munyi waya"tafad'a tana d'aukar mayafinta da hand bag nata ta fita.....
Time d'in da jidda ta iso gidan har ankawo lefen"yana tsakar gida dangi da mak'ota nagani"akwati 3 ne duka sai leda babba"wacce aka saka takalmi da hand bag kala bibbiyu aciki"kayan sawa kala 12 ne" sai dogayen riguna kala2"mayafi da hijab duk kala bibbiyu aka saka"sai kayan bacci da inners da kayan shafa....wani shegen kallo jidda tayiwa kayan tanajin haushi da b'acin rai"datasan wannan tsiyar zai kawo datace yabata kud'in tayi ciko ta had'o da kanta"amma ai angama tunda maida mishi za'a yi"tafad'a aranta tana nufar d'akin magajiya"tana jiyo abokan wasansu nace mata amarya amarya! ta musu banza"tana shigowa d'akin tasamu umma zaune tana ninkin kayan Aliyu"umma wai yanzun wa'acan banzayen kayan sune lefe?"ahab ba kece kikaji kika ganiba"?nidai wlh ko kawosu yayi d'akin nan bazan amsaba"yabarsu can d'akinsa"dubeki son kowa k'in wanda yarasa za'a kawo wa'annan y'an kayan amatsayin lefe"to ai umma kwantar da hankalinki"tafad'a tana zama ta shaida mata komai....shewa magajiya tayi tana fad'in duniya tadawo sabuwa jidda"kice bana dani za'a keta hazo?"in sha Allah umma"to nidai na amince"nasan dai mlm da taurin kai"amma tunda zancen kud'i ne zai iya sauyawa"kinga ni kisanar masa na amince bama saiya zoba"yadai samu Abdul d'in"yabiyashi saiya nuna masa kawai yajira d'in zuwa wani lokaci"inbe aminceba sai yayi magana da mlm" sbd yadda yake fakiri da wuya yak'i amincewa yaji zancen kud'i"to shikenan umma"dan wlh dana rasa wannan damar gara na hak'ura da Abdul duk son danake masa"sbd mota fa da million biyu zai bani" sannan azo Ayi hidimar biki komai yyi na kece raini"kuma baya buk'atar komai namu dg ni sai kayana za'a kawoni"to aimu haka mukeso"aduniya harka da maishi nada dad'i wlh"kai haihuwar ki yamun rana jidda....jidda ta kama dariya"Abba ya yaye labulen d'akin yana fad'in ina magajiya?"gani nan lafiya??"kizo ki kwashe kayan can ki maidosu anan duk wanda yazo saiya gani"ka barsu acan gunka mana"ko sadda kasaka ranar auren kayi shawara dani ne?"tsaki Abba yaja yace"kici gaba da mugun halinki karki fasa" aure bbu mahaluk'in daya isa ya hana ayishi" yana fad'in hakan ya yakice labulen yayi gaba abinsa"jidda da umma sukaja tsaki atare.....
Da dare misalin k'arfe 8:11 pm yah Abdul yagama shirinsa cikin wani dark blue d'in yadi"yayi kyau masha Allah"yanata zabga k'amshi"gaba d'aya yana cikin farin ciki"wajen jidda yakeso yazo yaga zatayi farin ciki da kayan da aka kawo"wanda dukda kayan basuda yawa,amma ba k'ananu bane"ak'afa ya iso gidan"saidai abin mamaki wata mota na fake agaban gidan"front sit abud'e, gefen mai zaman banza"kasancewar akwai nefa anguwar"wayarsa yazaro yafara kiran jidda"harta tsinke bata d'aga ba"kallon motar dake gaban gidan yakamayi yana nazarin kamar yatab'a ganin jidda ta fito dg cikin motar.....be gama wannan tunanin ba"ya hango jidda tafito dg cikin motar ta nufosa.....
โ๏ธhanzarta ki biya naki domin jin yadda wannan chakwakiya zata warware..... free page yak'are ๐
wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโ
Y'an nijar kutuntub'i wannan n๐ +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f
dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyaba
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐น๐คฑ๐ปWATA UWAH ๐คฑ๐ป๐น
๐๐ปโโ๏ธ(RAYUWAR ABDUL) ๐๐ปโโ๏ธ
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
Story & written by
mommyn fareesa
Last free page ๐
๐
ฟ๏ธ19&20
.......kallon jidda kawai yah Abdul keyi bbu ko k'iftawa"bbu wata alamar damuwa atare da ita ta tsaya gefensa tana fad'in sannu da zuwa! be amsaba sai cewa yayi me kikeyi a waccan motar??"yafad'a yana tsareta da ido"tab'e baki tayi tace"dama yanzun zan kiraka koda kai bazaka zoba"sbd zamuyi wata mgn dakai ta fahimta"sai gashima kazo"shiru yayi yak'i mgn sbd gaba d'aya zuciyarsa acunkushe take da ganinta da yayi ta fito dg cikin waccan motar"ga wani zato ya d'arsu aransa"k'asan zuciyarsa kuma wani bak'in kishi ne yakeji yana taso masa"tana tsaye agefensa tana k'ok'arin masa mgn"Alh sulaiman duniya yafito dg cikin motar yanufosu"kasa mgn jidda tayi tana satar kallon yah Abdul daya tsare Alh duniya da ido"sbd yanaso yagane kamar yasanshi"Assalamu Alaikum"sweet heart kin barni inata jiranki"yafad'a yana kallon jidda"da tsantsar mamaki yah Abdul ke kallon jidda"sbd jin agabansa wani k'ato na kiran wadda zai aura nan da sati 2 da sweet heart"jidda ta k'ak'aro murmushi tace"eh muna mgn ne dashi"okay kin masa bayani ne?"ah ah yanzun zan masa dai.....jidda! yah Abdul yakirata cikin dakakkiyar muryarsa"wacce bbu alamar wasa acikinta"idanuwansa har sun canza kala"fuska bbu annuri yace"kiyi gaggawar fahimtar dani meke faruwa??"tab'e baki Alh duniya yayi yakallesa ashek'e"agadarance yace"ba wani abu bane inaso ka hak'ura da aurenta sai zuwa wani d'an lokaci"kabarmun ita na aura"idan nasaketa saika aureta"idan ka amince da haka zan baka million 2"kaga kaima kaja jari ka fantama kafin lokacin"sanin kankane bazan tsaya nayi jayayya da talaka fatararre irinkaba"asalima taimakonka nayi"sbd kasan kowaye ni agarin nan"in ma baka tab'a ganina ba to katab'a ganina a TV ko a jarida ko a calendar...wani irin bugu zuciyar yah Abdul keyi"idanuwansa sunyi jajir kamar garwashin wuta"fatansa ace mafarkine yakeyi bada gaske ba"amma yadda yakejin kalaman sun wuce ace mafarkine"kayi shiru my Abdul? cewar jidda"yyinda Alh duniya ke danna waya hankalinsa kwance"wani irin mugun kallo yah Abdul yabita dashi"yana huci yace"hakik'a jidda kingama cutar dani"kin ci amanar soyayyar danake miki"inajin wasu labarukan halayenki ban Aminceba sbd ban tabbatarba"wasu kuma ina ganinsu da idona amma ina miki uzuri"ni zaki kira awulak'anta sbd banidashi?"nafi k'arfin na siyar da soyayyar danake miki"ke mai bakin kwad'ayi kije ki siyar da tawa soyayyar"kai kuma kana tak'ama da kud'i ko?"in sha Allah yadda baka kashesu ta hanyar alkhairi ba zakayi nadama marar amfani ta mallakarsu"yafad'a yana kallon Alh duniya"kai wawa! talaka wulak'antacce"ka isa ka gayan mgn"kasan koni waye?"pls sweet heart ka barshi kawai sbd ni"yah Abdul yakalli jidda yace"Allah ya isa tsakanina dake ban yafe miki ba"yafad'a yana laluben hanya sbd jirin dake damunsa yanajin kamar zai fad'i"yayin da kansa ke barazanar tarwatsewa"jidda kasa mgn tayi gabanta nata fad'uwa"sosai kalaman sa suka tsaya mata arai"batace komaiba tana kallonsa yana tafiya kamar zai fad'i.....Alh duniya yaja tsaki had'e da cewa"inane gidansu natura y'an daba su saita mun shi??"ah ah sweet heart miyayi zafi?"ka barshi kawai pls"shikenan yaci darajarki wlh"tana k'ok'arin mgn Abba ya iso zai wuce ciki"da sauri jidda tace"Abba sannu da zuwa"kallonta kawai yayi sbd rabon data gaishesa ko masa sannu da zuwa yama manta"baba ina wuni?"muryar Alh duniya ta katse masa tunani"yakallesa da mamaki yana amsa gaisuwar tashi"dan yafahimci bama yaro bane" koya girmesa ba bada wani abu ba amma yake kiransa da baba"dama Abba zakuyi wata mgn dashine"wace mgn kuma?"keda ayau saura kwana 14 ad'aura auren ki.....inaso dai abani dama muyi mgn baba"to babu damuwa"shiga ciki ke"jidda batace komaiba ta wuce cikin gidan"Abba da Alh duniya suka zauna kan dakali"bbu wani b'oye b'oye Alh duniya yayiwa Abba bayanin manufarsa"dg k'arshe yasanar masa idan ya amince zai bashi millon 2"wani murmushi Abba yasaki kafin yace"subahanallahi! niba makwad'aici bane"na rik'e talaucina "banida matsalar rashin ci dasha"Alhmdllh ina godiya ga ubangiji nah"bazan zamo mai mgn biyu ba"na riga nayi mgn da iyayen yaro"bazan zamo mai k'aramar mgn ba"kuma nema cikin nema ai haramun ne......dakata baba! na riga na gama yanke hukunci saina auri jidda"karka manta bakai bane mahaifinta"ko bujurewa umarninka tayi bbu abinda zai faru da ita"sbd haka saina aureta"Abba na murmushi yace"to shikenan Allah yabama mai rabo sa'a"yana fad'in hakan yatashi tsaye ya wuce ciki"Alh duniya yakira jidda ta waya yasanar mata yadda sukayi"dg k'arshe yasanar mata gobe zai turo mata kud'i ta siyawa mamanta gida su koma"acan sai Ayi hidimar bikinsu"ta amsa hankalinta kwance"Abba kuwa becewa magajiya komai ba"amma abin yasoki zuciyarsa sosai"ko abincin dare kasa ci yayi yanata tunane tunane"yyinda jidda da uwarta hankalinsu kwance.....
Afannin yah Abdul kuwa ajigace ya iso gida"da k'yar yarufe gidan yanufi b'angarensu da aka gama gyarawa"ko kayan jikinsa be cireba ya kwanta kan tabarma"kansa na ciwo"zuciyarsa na zafi"gaba d'aya jikinsa zuface keta ketowa ta ko ina"yadda yaga rana haka yaga dare"dg k'arshe ya d'auro alwalah wajen 3am yafara jero nafilfili"bayan yagama yayita istigifari da hailala da salatin Annabi"kafin yanemi zab'in alkhairi"sannan yarok'i Allah yafidda masa da soyayyar jidda aransa"sbd har yanzun yanajin soyayyar ta aransa"zuciyarsa tak'i yarda wai jiddansace zata aikata masa haka"da wannan tunanin bacci b'arawo yasacesa......be farkaba sai wajen 8:15 am"da hanzari yatashi yanufi toilet yayo alwalah yazo yayi sallah"sannan yayi wanka"shirya yayi cikin k'ananun kaya"yyi y'ar rama"ba k'aramin kyau yayiba"idanuwansa har yanzun jajir suke"fitowa tsakar gidan yayi yahad'u da meenah zata shiga kitchen"tayi saurin dubarsa tana fad'in yaya katashi?"yanzun nake cewa "najika shiru duk yau da safe banji motsinkaba"banajin dad'i ne meenah"wayyo Allah sannu ! ya jikin?"da sauk'i yafad'a yana nufar parlourn goggo"zuciyarsa akare sbd tunawa da yayi da sukayi fad'a kwanaki da kabeer ta masa baki"kodai bakin ne yafara binsa??kai lafiya zaka shigomun sangam sangam bbu ko sallama?"muryar goggo tadawo dashi tunaninsa"Ahankali yace"nayi baki jiba"ina kwana? lafiya qlau"dg haka ta maida hankalinta wajen tv"shi kuma yatashi dg dukiyar da yayi zai fita meenah ta shigo" anan tace"yaya kajira kayi kari mana"dama anan yake kari yanzun?"ai zuciya yayi yadena cin komai na gidan nan"idan yanada zuciyar yanema ai saiya ci mai dad'i"cewar goggo tana tab'e baki"yah Abdul bece komaiba yarab'a meenah yafita"meenah tazauna kan kujera tana ajiye flast d'in hannunta tana fad'in"dan Allah goggo ina rok'onki alfarmar ki sassautawa yaya ko yasami sukuni"wlh da alama yau yana cikin damuwa"yoni kuwa ubanme na masa?"munafukar yarinya zaki watsamun tsaba kaji subini"to