Showing 57001 words to 60000 words out of 77635 words
d'aura"dato ya amsa ya wuce cikin d'akinsu"bbu jumawa yadawo da zannuwa biyu"inna ta amsa ta koma ciki"acikin zani guda tasaka babyn"sannan ta ajiye zanin guda"ta lek'o takoma kiran yah Abdul"ya iso wajenta ya amshi babyn datake mik'a masa"kayi hak'uri Abdul yarinyar ina zaton batada rai"amma kana iya kiran doctor yazo yadubata"gabansa na fad'uwa yakalli yarinyar"sak yaga kamanninsane da ita" afili yace"ikon Allah mai yanda yaso"bara na kwashe ruwan zafin can inna sun tafasa sai naje na kira doctor yazo yaduba"yafad'a yana mik'a mata babyn"ta amsa ta koma ciki da ita"ta shimfid'a tabarma ta azata asama"bilkisu dai na zaune tayi ta gumi tana tuna dama haka ake haihuwa....
ruwan zafin ya kwashe a babban roban wanka yafita dg cikin gidan da sauri"inna kuma ta kwashe komai taje ta zubar tasaka aka d'ebo bedi"tazo ta wanke kayan da billy ta haihu dasu"sannan taje ta d'auki kujera takai bayi"da kanta ta taimaka mata suka fito suka nufi bayin"da kanta inna mai k'osai tayi ma bilkisu wanka na asali"sai gashi tun a bayin tafara jin dad'in jikinta"time d'in da suka fito anata kiran sallar la'asar"inna ta wanke bayin taje ta goge d'akin ta kunna tsintsiyar k'amshi"babyn ta d'auka ta mayar wajen bilkisu dake shirya jikinta"gata nan bilkisu nizan wuce gida Allah yabaki lfy" kidinga yawan kama ruwa da ruwan d'umi"kuma idan za'a miki wanka ki dinga shiga ruwan zafi kamar yadda na miki"sai abu na gaba ki dinga cin abinci"to in sha Allah inna nagode sosai"ga wannan bbu yawa"tafad'a tana mik'o mata dubu 3"wlh bazan karb'a ba bilkisu"dan Allah nayi miki ke kamar jikatace"ada nayi anguwar zoma amma nabari tuni"godiya bilkisu ta mata sukayi sallama"riga da siket na atamfa tasaka tashafa powder da jan baki da turare"saiga billy tayi shar da ita kamar ba ita bace ta haihu"zama tayi kan bed ta lumshe idanuwanta"yunwa da bacci na addabarta"dan dama tun tana girki takejin ciwon daurewa kawai tayi harta Ida..... sallamar yah Abdul da musa da wani taji atsakar gidan" shigowa yayi d'akin da leda bak'a a hannunsa" suka had'a ido dashi ya ajiye ledar"yana fad'in ah ah my billy me jego kece kika sha kyau haka?"murmushi tayi tace"kai kuma Angon jego ko?"ni Allah wannan kwalliyar taki tajan mgn ce kikamun ko?"batace komaiba tana dai murmushi yazo ya d'auki babyn"yadubeta yace" doctor zai dubata ne"okay ta fad'a shi kuma yafita"anan tsakar gidan doctor d'in yadubata yagano batada rai dan tun aciki ta rasu"jiki asanyaye yah Abdul ya amsheta yamasa godiya yatafi"musa na bashi baki da nuna masa akwai abinda ubangiji ke nufi da amsar ran yarinyar"fatansu Allah yasa mai cetoce"d'akin yah Abdul yakoma" billy na zaune tana latsa y'ar wayarta nokia"bilkisu saidai muyi hak'uri tunma aciki Allah ya amshi kayansa"Allah ya jikanta yasa mai cetoce"ya amsa da Ameen"karka damu yah Abdul Allah zai bamu wata ko?"hakane billy nah"zamuje yanzun mudawo arufeta"aledar nan akwai magani da yadda zakisha"kici abinci sosai kinji?"saiki kwanta kiyi bacci"to kaifa bazaki ci abincinba?"tafad'a kamar zatayi kuka ta lura yadamu da rasa babyn tasu"idan muka dawo zanci karki damu"nidai bazanciba"damun b'ata dake"yafad'a yana k'ak'aro murmushi"ta sakko dg samqn bed d'in ta amshi babyn ta ajiye asaman bed d'in"yayima yarinyar photo"bilkisu na tsaye gefensa ta aza kanta agefen jikinsa"my billy muje ku gaisa da abokina yamiki barka"nidai kunya nakeji"tafad'a tana b'oye fuskarta ajikinsa tana kukan shagwab'a"murmushi yayi yace"andena kunyar haihuwar fari yanzun my billy"muje ku gaisa"dato ta amsa ya kama hannunta suka fito tsakar gidan"gaisawa sukayi da musa yamata barka da gaisuwa sannan suka fita"bilkisu ta zubo abinci mai d'an yawa"shinkafa da makaroni da miyar naman kasuwa"ta duba ledar daya ajiye mata"maltina ce da magunguna sai ledar kaza gashashshiya"rabi ta d'iba ta d'aure rabin ta aza kan mirror......k'at tayiwa cikinta tasha magani"ko maltinar bata shaba tabarta sai zuwa anjima"tabarma ta shimfid'a mai girma sbd mutane in sunzo"ita kuma ta koma samqn bed d'in ta zauna tana matse k'afafuwanta"ahaka Anty kareema da inna hassana suka shigo(yayar ummi da k'anwarta)"ko minti 5 basuyi ba yah Abdul yashigo suka gaisa yad'auki babyn sbd aje a rufeta.....dandanan sai jama'a suka yita shigowa na kusa"dan har hafsat tazo"kasancewar bilkisu tayi wanka takumaci abinci"bbu wani girki da aka mata.....
Da dare✍️
wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki ta what's app n d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika fitarmun Allah ya isa ban yafeba
.......Da dare bayan gidan yarage jama'a yah Abdul yashigo sbd yasaba any time yana tare da bilkisu indai yana gida"yau duk sai yaji wani iri dabasu zauna atare ba"ga damuwar rasa babyn su"dama yana gama isha'i yaje ya amso wasu kud'i yasiyo ma goggo kaza gashashshiya yakai mata"yayi mamakin yadda tayi masa godiya"ta kuma sanar masa mahaifiyar bilkisu tazo dubata taka mata alkhairi"hakan ba k'aramin dad'i yamasa ba"gidan abud'e yake hakan yasa yayi sallama daya shigo"bilkisu ce sai wata mata data shigo a mak'ota"amsa sallamar sa billy tayi ta taso ta fito tsakar gidan"yah Abdul kadawo?"nadawo my billy"shine bakaci abinci ba kayita zama da yunwa ko?"ta fad'a tana ta kallonsa"sbd yayi wanka yacanza kayan zuwa k'ananu"ba k'aramin kyau yamata ba"yana k'ok'arin mgn matar dake cikin d'akin ta fito ta musu sallama ta tafi"billy kuma ta juya zata koma ciki yayi saurin rik'ota yana murmushi yace"miye na fushi billy nah?dama ana fushi da ango ne? gabanta yafad'i tayi saurin d'ago kanta tace"waye Angon?"dariya ya k'yalk'yale da ita yana haska furkarta da flash light d'in wayarsa yace"nine Angon jego ke kuma amaryar jego ko?"jikinsa tafad'a ta saki kukan shagwab'a"yana shafa bayanta yace"sorry sweetie nah kin iya kishi ko?"ni banida budurwa"gani da kamarki bilkisu miye zan gani awajen wata?"ku maza kun iya dad'in baki"nidai kazo muje kaci abinci"tafad'a tana jan hannunsa"idan bak'i sukazo fa?"bbu wanda zaizo sai inna mai duma"(k'anwar mahaifiyar ummi)itama nasan sai takai 9pm"miye zatazo yi?"anan zata kwana da safe zata dafa ruwa tamun wanka shinefa"my billy nidai dan Allah karkije wankan gidan nan"banaso amaidani marayan k'arfi da yaji"yafad'a suna shiga cikin d'akin"ya zauna kan carpet"ita kuma tafara k'ok'arin zuba masa abinci tana fad'in nima sbd kai banaso naje"amma wlh naji ana zancen"nidai zan sanarwa Abba bazakije ba"ruwan zafi da kaina zan dinga dafa miki"harma wankan basaina miki ba?"dariya tayi tace"ni kaina ban iyaba sai an koyamun balle kai"tafad'a tana ajiye masa abincin agabansa"ta zauna agefensa"kizo muci mana"na k'oshi ni"my billy tashi ki had'a tea mai kauri kisha da magungunanki kinji?"dato ta amsa tanufi kitchen"acan ta had'o tea d'in sbd akwai ruwan zafi a flask"bayan ta gama had'awa yazo ta zauna agefensa samqn pillow"shi yanacin abinci ita tana shan tea"bayan sun gama da kansa yabata magungunanta"yajata suka zauna kan bed d'in"tayi zamanta samqn cinyarsa"yanata kallonta yace"jiya kamar yanzun kina nan da ciki"kunnansa ta murd'e sukayi dariya atare"Ahankali yace"dama kin sanarwa ummi goggo bata lafiya?"eh bayan kafita d'azun d'in na kirata ai"Allah sarki ai taje ta dubata harda d'awainiya takai"wlh naji dad'i sosai"Allah yasaka da alkhairi"tana murmushi ta amsa da Ameen"bilkisu dake da family naki banida bakin muku godiya"kun mun halacci ba kad'an ba arayuwata"tabbas ka auro y'ar asali wacce ta fito tsatso mai kyau shine daidai"karkace sai y'ar masu kud'i ko kace zakabi kyau na fuska ko jiki kasota"gara kasota dan Allah" wlh bilkisu na hankalta da rayuwa"zancen danake miki yanzun wai k'anwar nura ta sami wani sim card tasaka awayarsa"shinefa bema saniba saida yaga anata kiran wayar"yad'aga yaga sim2 ne ake kiran"tambayarsa akayi waye shi kuma yana ina?"tsaki yayi yakashe wayar"wlh bincike yayi bincike har gida police sukazo suka tafi dashi cikin tozarci"wai ashe sim d'in na y'ar minister ne kuma ansaceta"anata nemanta ba'a gantaba"ayadda na fahimta wad'anda suka sace yarinyar suka yarda sim card d'in ta"shine tsautsayi yasaka k'anwar nuran ta tsinta"yanzun haka yana station an masa duka na fitar hankali......sai gashi da bakinsa yake fad'in alhakinane yaka mashi nayafe masa"dama kekunan shine yahad'a kai da wasu aka sace aka dawo aka kamani aka saka na biya kud'i"ni kuma wlh nace bazan yafeba billy"yaje shida Allah"ajiyar zuciya bilkisu ta saki tana fad'in ai dama shiyasa akace ka guji hakk'i"komai k'ank'artarsa kuwa"Allah yasa yagane gsky idan yafito ya gyara"ni kaina ban yarda ka yafe masa ba wlh"yana k'ok'arin mgn sukaji sallamar inna "hakan yasa bilkisu tabar jikinsa da sauri ta fito tsakar gidan ta tarbeta"shima fitowa yayi yagaisheta ya wuce wancan d'akin"bilkisu tabishi d'akin"tafara masa shimfid'a yana zaune yanata kallonta yace"billy nasan yau bazanyi bacciba za'a raba mana makwanci ko?"wlh nima haka"saidai muyi hak'uri nad'an lokacine ai"hakane tozo kiji wata mgn"bbu musu ta matso jikinsa yayi hanzarin had'e bakinsu..... romancing d'inta yakeyi sosai"saidai kawai sukaji muryar inna na kiran bilkisu"saurin cikata yayi tana gyara rigarta"murya can k'asa yace"my billy cikin dare kidawo pls nasamu na rage zafi kin san banida hak'uri"kanta kawai ta gyad'a masa ta fice dg d'akin da sauri.....
*****************
ki manin kwana 3 kenan da haihuwar bilkisu"tayi shar da ita sbd kulawar datake samu awajen yah Abdul da innah"kuma iya bakin gwargwado komai yanayi iya k'arfinsa"goggo nacan dangi anata zuwa ganinta"kabeeru kuwa tunda akayi haka be koma zuwa gidan ba"abin yabama goggo mamaki yakuma yi mata ciwo"kullum yah Abdul zaizo da safe yagaisheta da jiki"sannan yadawo da rana da abinda Allah ya hore masa yakawo gidan dan dama sunada kayan abinci....ayau tun wajen 3pm meenah ta tafi skul dan lactures d'in yau na marece gareta"yah Abdul yazo ya zauna da ita"saida aka kira sallar la'asar yace"zaije yayi sallah masjeed yadawo"koda yafito wata farar motace yagani fake a k'ofar gidan"be damuba yayi gaba"yana barin wajen laurat ta fito dg gaban motar itada wata budurwa"laurat na sanye da abaya black ta dad'e da eye glass bak'i"tana rik'e da hand bag nata suka nufi cikin gidan goggo"bbu ko sallama suka shigo"k'arar takalminsu yasaka goggo dake zaune a tsakar gidan ta d'ago kanta"gabanta taji yafad'i ta tsuke fuska tana binsu da wani irin mugun kallo"laurat tasaki murmushi tana zare eye glass nata"ta zuge hand bag nata ta zaro dorina tana murmushi ta kalli goggo ido cikin ido tace"ke tsohuwar banza! yau zanyi maganinki na kirana da kikayi da y'ar iska"ta yadda banzan d'anki zaiyi zuciya yasakeni"dama k'addara tasaka na auresa amma tunda na gano fasik'i ne manemin matan banza na tsanesa"inda ayanzun inason kabeer wlh da saina rabaki dashi"kuma dama ba sonki yakeyiba kece kika damu dashi"ta fad'a tana nufo goggo da dorinar a ahannunta"goggo ta zaro ido tana nuna kanta tace"nikike zagi kuma kike k'ok'arin duka? k'awar laurat na dariya tace"yanzun zaki gani ki dena tambaya ma"goggo na k'ok'arin mgn laurat ta fara tsula mata bulalar iya k'arfin ta"tasaki ihun azaba"ita kuma tana cigaba da dukanta tako ina"gashi goggo bbu damar ta tashi k'afa adore"tana ihu da komai laurat duk tafashe mata baya"kafin taja tsaki tana huci tace"dg nan dama gidanmu nayi kisanar masa ya aikamun da takardar sakina"tana fad'in hakan suka fita da sauri sbd gudun kar asamesu"fuskar goggo jage jage da hawaye tana jin radad'i ajikinta tana wani irin numfashi sbd tsananin b'acin rai.....tana ahaka yah Abdul yashigo da sallama"turus yayi arikice yace"goggo lafiya kike kuka?"Abdul matar kabeeru ce tazo yanzun ta zageni ta kuma dokeni da bulala"ta fita yanzun nan itada k'awarta"what??? yafad'a da k'arfi yana zaro manyan idanuwansa yana isowa gaban goggo yana duba jikinta"idanuwansa jajir ya d'auki wayar goggon yana huci yafara k'ok'arin kiran kabeer"hands free yasaka wayar"gab da zata tsinke kabeer yad'aga yana fad'in wai lafiya aka isheni da kira?"kai wawa lusari! dani kake mgn bada goggo ba"y'ar iskar matarka tazo har gida ta daki mahaifiyarmu ita matsiyaciya"wlh nayi arba da ita koni ko ita muddin baka d'auki matakiba"yoni wane mataki zan d'auka zaka kirani kanamun wasu surutai da ihu?"ita goggon damuwa tayi dakai dakake tada jijiyoyin wuya akanta?"tabbas kacika dak'iki dakake wannan zancen" iyaye basai sun soka kake kare mutuncin suba"okay to ni bazan kareba"bbu matakin dazan d'auka sbd bansan yadda akayiba"kana nufin bazaka rabu da itaba balle ka hukuntata?"eh inason matata bazan rabu da itaba....yana fad'in hakan yakashe wayar"goggo na kuka da hawaye zuciyarta na zafi tace"kaicona dana d'auki son duniya na zab'i d'an bai kamataba na aza akansa"Allah ya isa tsakanina dakai da ita"Abdul ka barshi dg shi har ita"nasan tabbas kace zaka d'auki mataki komai zai iya faruwa sbd ubanta yanada kud'i"na shiga ukku ni fatima"na zab'i y'ar banza marar tarbiyya"wacce bata dace data zama surukataba"ga yadda ta kwashe dani"Allah sarki bilkisu! yarinyar arzik'i"wacce bata iya had'a ido dani"balle harta iya gayan bak'ar magana koda mi zan mata....bata k'are zancen ba ta b'ingire tana maida numfashi ta danne saitin zuciyarta"yah Abdul yanufota arikice yana kiran sunanta"wani irin tari goggo keyi tana dafe kirji"dagota yayi ya jinginata ajikin pillow yaje ya d'akko ruwa yazo yana bata"yana fad'in kiyi hak'uri ki dena tuna wannan abin da yafaru"shi kuma Allah ya shiryesa"karkiyi masa baki goggo"ita duniya haka take zatayi aiki akansa"shiru kawai tayi tana kukan zuci"gaba d'aya rayuwar ta mata k'unci"ga nauyi da nadamar abinda tayiwa yah Abdul aranta"sai yanzun tagane Allah yamata kyautar d'a nagari amma bata ganeba sai yanzun"suna ahaka baffa Aminu da baffa mukhatar suka shigo cikin tsakar gidan"yah Abdul yamusu sannu da zuwa"ya shimfid'a musu tabarma"yakamusu ruwa"bayan sun gama gaisawa suka sha"kallo d'aya baffa Aminu yama goggo yasan tanada damuwa"bayan sun mata yajiki tana kuka tasanar musu abinda ke faruwa"baffa ya girgiza kansa yace"Allah ya kyauta ayanzun me kika fahimta a wannan al'amarin?"ita dama duniya haka take"idan kanunawa d'a so to tabbas zakayi nadama had'e da dana sani"wanda bakyaso kika nuna kamar ba kece mahaifiyar saba shine yasan darajarki da mutuncinki"dashi da matarsa"dan da bakinsa gaya nan zaune" idan muna waya yake sanarmun kyawawan halayen ta"kuma ni dama tunda mukaje neman aurenta nasan yadace da y'ar gidan mutunci"sbd dattako na iyayenta"amma ke sarkin kwad'ayi bakimaso munje awajen neman auren kabeer ba sbd kar ace danginsa talakawa ne"to wlh ki gyara kuskurenki fatima....Abdul yakuma hak'uri?"yafad'a yana maida kallonsa ga yah Abdul"kansa ak'asa yace"Alhmdllh baffa"madalallah! dama munzo garin da safe sbd muna kawo shanu anan"saina tuna ka kirani kasanarmun bata lafiya kuma mai d'akin naka ta sauka"shine nace mu biyo"kazo muje ga tunkiya can a mota na baka ayankama mai jego"dukda dai bbu rai kyautatawa ce ayanka mata d'in" taci naman ta maida ruwan jikinta"baki washe yah Abdul yakama godiya yana fad'in"wlh ni kaina nayi tunanin hakan baffa"to ita da kanta tacemun yah Abdul nidai tunda bbu rai karkayi yankan komai kana ta kanka"Allah sarki mace ta gari kenan"to a yanka mata dan Allah"Allah yayi muku albarka bak'i d'aya"mu zamu wuce"goggo ta musu godiya suka fita atare da yah Abdul"bbu jumawa yadawo da tunkiyar"kuma bbu laifi babbace dan idan siyota zaiyi zatayi 50k"goggo tace"kagode sosai saika d'aureta acan nanda kwana 4 sai ayanka mata"yayi mamaki sosai danshi bada niyar ya ajiyeta anan yakawotaba"yazo dai da ita yanuna mata"ya yadda tabbas abinda yafaru yasaka goggo sauyawa"beyi musuba yad'aureta da igiya"yafita k'ofar gidan yatura sadeeq yasiwo kayan abincin dabbobi "ya ajiye mata agabanta"yazo yazauna"yana anan har meenah ta dawo gab da sallar magrib"sallama yayiwa goggo yatafi"yana mamakin wai tana fad'in yagaishe da bilkisu"bayan fitarsa goggo na kuka tasanarwa meenah abinda ke faruwa"salati meenah tayi"ranta ab'ace tana duba jikin goggon"hawaye masu zafi suka wanke mata fuska....cikin raunin murya tace"kiyi hak'uri da abinda zan fad'a miki goggo"wlh tallahi nina san harda hakk'in yah Abdul da Anty billy haka yafaru dake"miyafi bak'in ciki atakaka bakada halin ramawa?"yanzun in bacin dakika tsaida yaya Abdul"zaije yayi ko menene sbd kare mutuncinki"amma kinsan dg k'arshe ba abu me kyau zai biyo bayaba sbd ubanta nada kud'i"shiyasa kika hanashi"Anty bilkisu bbu irin takurawa da matsawa daba kiyi mata ba itada yah Abdul"bata miki mgn da ihu sai cikin ladabi"amma wannan y'ar iskar ko gaisheki bata yi balle tasan ke uwace awajen mijinta"gashi shima bai d'aukeki da daraja ba"yanuna bakida matsayi awajensa"wlh Inda yah Abdul ne ba fata nakeba"ko wane irin SO yakeyiwa mace ta miki haka yabarta har abada"amma ga yah kabeer yanuna bazai rabu da itaba"kin koresu yah Abdul agidan nan sbd shi"bayan yaso yaketa mutuncin matar yayansa"sai gashi gasky tayi halinta kince da bakinta take fad'in manemin mata ne"kuma ba k'arya tayiba"tun kafin ya aureta nasan yana neman mata hakama yah Abdul yasani"wlh goggo ki nemi gafarar yah Abdul da Anty billy tun lokaci bai k'ure mikiba"ki guji addu'ar wanda aka zalinta"hak'k'i komai k'ank'artarsa hakk'ine"bawai fad'a nake miki ba"ah ah kullum ina k'ok'arin ankarar dake kiyi abinda ke daidai kidena biyewa son zuciya"goggo na kuka jage jage da hawaye tace"tabbas meenah na sani"tun bayan barin su gidan nan naketa fama da miyagun mafalkai"wlh meenah zuciyata ciwo takeyi sbd wannan b'acin rai"na haifi d'a da cikina matarsa ta dakeni amma ko ajikinsa bashida alamar d'aukar mataki"mi yafi wannan ciwo?"fatana Allah yabani lafiya naje har gida na rok'i bilkisu gafarar abinda na musu"wlh nayi nadama meenah"ajiyar zuciya tasaki tace"Alhamdllh goggo Allah ya yafe mana gabaki d'aya"ta amsa da Ameen jikinta asanyaye"zuwa magrib zazzafan zazzab'i yakama goggo da ciwon kai sbd dukan datasha da kuma kuka"acikin daren yah Abdul yazo shida musa da meenah da wata yayarta suka kaita asibiti acikin wata motar abokinsu"wanda saida musa yakashe 8k dan yah Abdul beda kud'i"anan aka gano ta kamu da ciwon zuciya"adinga kiyaye b'acin ranta"meenah tasha kuka sbd
ganin wata banza tayi sanadin mahaifiyarta ta kamu da ciwon zuciya"sai awashe gari da safe aka mayar da goggo gida......
Ayau take 7days da haihuwar bilkisu....✍️
wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki ta what's app n d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika fitarmun Allah ya isa ban yafeba
.......ayau take 7days da haihuwar bilkisu"wanda ba wani bidia za'a yiba ayau d'in"hasalima bilkisun tace"batayin wani taro"amma dukda haka anyi abinci kala2 na suna tuwon masara da jallop rice"sannan tayi kwalliyarta cikin sabbin d'inkuna kala 2 data bayar acikin sauran kayan lefenta aka d'in ka mata"tayi kyau masha Allah"saidai tayi mamakin yankan da akayi mata"fatanta Allah yasa ba bashi bane yah Abdul d'in yaciwo"kasancewar tun bayan angama yankan baya gidan"yatafi d'akko mai gyara akoma duba k'afar goggo"ga ciwonta na zuciya yatashi"sbd idan ta tuna wai matar d'an data haifa tazo ta nakad'a mata shegen duka"sai taji kamar zuciyarta zatayi bindiga"sbd b'acin rai da damuwa"kuma gaba d'aya kabeer ya d'auke k'afarsa