Showing 1 words to 3000 words out of 77635 words

Chapter 1 - WATA UWA

Unknown   

10 Nov 2024

3610

๏ปฟ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒน๐Ÿคฑ๐ŸปWATA UWAH ๐Ÿคฑ๐Ÿป๐ŸŒน

๐Ÿ™†๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ(RAYUWAR ABDUL) ๐Ÿ™†๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ




Story & written by
mommyn fareesa


*Godiya* Alhmdllh ala kulli halin tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabammu annabi muhammad S A W da ahlayensa da sahabbansa"yah Allah yadda na fara wannan book lafiya yah Allah kasa na gamashi lafiya yasa ya amfanemu baki d'aya.

*Tsokaci* sunan wannan book d'in ga wacce ta tab'a karantashi abaya ba'a gamashiba har ana cewa ana jiran book 2 "to bbu zancen book 2 labarin zai sauya salo ne amma duk d'aya ne inkuma baki tab'a karantawa to garzaya ki Fara yanzun"bana son abini da zancen wai wata uwa akeso cmpt ko kuma wata tambaya nayi bayani ta yadda kowa zai fahimta"idan kin tab'a karanta shi bbu cigaba kibi wannan zakiga komai....

*Gargad'i* wannan littafi k'irk'irarran labarine ban yishi dan wata ba ko wani" idan yayi cin karo da irin rayuwarki arashine......

dedicate to all my fans๐Ÿฅฐ๐Ÿ’“

BISSIMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM

free ๐Ÿ…ฟ๏ธ 1&2

*sokoto state* Anguwar gobirawa...........
misalin k'arfe 5:48 pm"yarinya ce budurwa y'ar kimanin 22 yrs tsaye abakin wani k'ofar gida mai dakali"tana sanye da riga da siket na atamfa red sun kamata sosai"ta yafa siririn mayafi asamqn kanta"wanda kallo d'aya zaka yiwa yarinyar ka tabbatar batada wani kamun kai balle wata cikakkiyar tarbiyya"doguwace fara"batada jiki "sannan kallo d'aya idan kamata zaka iya kiranta kyakykyawa"amma idan ka nutsu kana kallonta bazaka sakata sahun jerin kyawawa ba"amma batada muni"ga k'ira mai d'aukar hankalin duk wani namiji lafiyayye tanada ita"hasken man bleeching ne yak'ara sakq ake mata kallon kyakykyawar gske....wani saurayi na tsaye a gefenta"wanda shekarunsa bazasu wuce 33 yrs ba"kansa ak'asa yana kallon k'asa kamar mai yin nazari ko fahimtar wani abu acikin k'asar" hakan yasa banga fuskarsa ba"cikin karairaiya da lankwashe murya budurwar mai suna *jidda* ke fad'in gsky my *Abdul* yazama wajibi nayi ankon bikin maryam "sbd nice babbar k'awa"biki saura 3 weeks ban siyi anko ba sai yaushe zan siya kenan?"in kuma bazaka iya siyamun ba bbu damuwa sai nasan yadda zanyi wani yasiyamun"maza nawa na wulak'anta sbd kai???"tafad'a tana yatsina amma tak'i yarda ta kallesa sbd tasan idan ta kalli cikin manyan idanuwansa masu kwarjini bazata iya gaya masa haka ba"d'ago kansa yayi yana zuba mata manyan idanuwansa masu girma farare tas.....kallon sa nayi nace masha ALLAH! ubangiji yyi baiwar kyawu,kwarjini ,kamala hade da haiba"domin in badan yanayin hutu ba,da baya samu sai kace ba d'an nigeria bane lol... wankan tarwad'a ne shiba fariba ,ba kuma bak'i ba "yanada manyan idanuwa farare masu sakawa maraji tsoronsa" dan in yatsare mutum da ido dole yaga kwarjininsa" ga hanci har baka,uwa uba sajen daya k'awata doguwar fuskarsa dashi"wanda ke Jan mata da yawa cewa suna sonsa ,yanada kirar in garmar mazaje dan k'akkarfane ,jikinsa duk gashi amurde yake....idan kuwa yana mgn cikin sweet voice nasa baza kaso yadena ba"yah Abdul yahad'u๐Ÿ’ฏ"duk macen data ganshi muddin batada masoyi zatayi sha'awar mallakarsa amatsayin mijin aurenta"cikin nutsatstsiyar muryarsa mai dad'in amo da sauti yake fad'in I'm so sorry jiddah nah! 15K ne yanzun nan aka banisu na d'inki"5k kuma zan biya kud'in kayan d'inkin dana siya"yafad'a yana kallon fuskar jiddan yana jiran jin me zatace?sbd shidai bai cika doguwar mgn ba"jidda na k'okarin mgn wata budurwa tazo agefensu zata wuce ta shiga cikin gidan"tana sanye da yunifoam pink colour na islamiya ajikinta" da face mask a fuskarta"Ahankali ta musu sallama tana fad'in ina wuni?"yah Abdul ya amsa da lafiya qlau *bilkisu* jidda ta tab'e baki bata tankaba"bayan wucewar bilkisu ta wani shagwab'e fuska tana fad'in nidai 10k nake buk'ata"sbd 8k kud'in atamfar"sai 2k na head"kallonta kawai yakeyi sbd mamaki"yarasa meyasa jidda batada tausayi?"musammun idan taso abu"okay bara natafi tunda bakada time nawa"bece komaiba ya zaro kud'in dg aljihun wondon jeans nasa dark blue yazare 5k yamik'a mata sauran"bbu godiya ko amsa da hannu biyu"kawai tasaka hannu guda ta amshe kud'in"yariga yasaba da halayenta tun tsawon fara soyayyar shi da ita" kimanin 2 yrs hake take masa"zan wuce gida magrib ta gabato! yafad'a cikin cool voice nasa"jidda ta d'ago kanta ta kallesa tanajin kamar ta rungumesa"kukan shagwab'a tasaka tana fad'in nidai my Abdul da sauran time fa......jingina jikinsa da bango yayi da sauri sakamon abinda shagwab'ar jidda ta hadda masa"shiyasa bai cika son zuwa zance guntaba"sbd tana masa abubuwan dake tayar masa da hankali"cikin dakiya da b'oye yanayinsa ya sauya fuskarsa wajen fad'in jidda yaushe zan turo iyayena agidan ku?"b'ata rai tayi suka had'a ido"saurin janye idanuwanta tayi tana fad'in tayaya zamuyi aure bakada aikin yi balle gidan kanka?"da mamaki yad'ago kansa ya kalleta"yad'auki wasu few seconds kafin yace" d'inkin dana keyi ba aiki bane??gida kuma ki bari Ayi auren mana kigani " gsky sana'ar d'inki ban daukeshi aiki ba"kanada degree naka ka bari kasamu aikinyi mana"kinga jidda! idan aurenah ne bakya sonyi ki fito kimun bayani mana"yakikeso nayi da raina?"8 month kenan ina miki mgn kina mun yawo da hankali" so kike na cutu da abinda ke damuna na feeling ko kuwa yaran layi kikeso nakamako me?"yafad'a cikin kakkausar muryarsa"yawani d'aure fuska"saidai hakan ba k'aramin kyau yak'ara masaba"ganin yana k'ok'arin yin fushi yasaka jidda yin k'asa da murya tana fad'in miye amfanina my Abdul?"ko bamuyi komai ba ai ko romance zan barka kayi dani kafin zuwa time d'in auren.....bakida hankali ne jidda?"yakatseta da mamaki"yana cigaba da cewa"me kike nufi?"to bari kiji bazan tab'a aikata zina ko kusantarta ba"ban kuma tab'a zaton haka dg garekiba"inada k'anwa da yayu mata da y'ay'an dangi"idan kayi zina da k'anwar wani ko yayar wani ko y'ar wani"kaima za'a yi da taka! idan naso aikata zina jidda da tuni na fara aikata ta"amma bbu abinda na tsana aduniya irinta"yana fad'in hakan yaja doguwar tsuka yyi gaba yana bar mata k'amshin turarensa......jidda taja tsaki tana tab'e baki had'e da d'age kafad'a irin ko ajikinta" tana fad'in kafin safe zamu shirya ne"kaga namiji har namiji saidai kashi! bakada kud'i"wanda sune jin dad'in rayuwa"ta fad'a tana k'ok'arin shiga cikin gidan su taji muryar *babawo* yana fad'in jiddancy babbar yarinya! juyowa tayi sbd kanta yafasu"tana murmushi tace"mutumin 2days?"kedai bari naje lagos ne"jiya nadawo"ina Asee baby?"tana gidansu fa"lafiya kake nemanta?"lafiya qlau" wani party zamuje da ita anjima" naje gidansu bata nan"kedai nasan ba zuwa zakiyi ba"tana k'ok'arin mgn Abba ya iso zai wuce ciki"babawo yamasa wata y'ar iskar gaisuwa"ya amsa ya wuce ciki"jidda ta dubesa tana fad'in sai anjima mayi waya ko?"dadai kina what's app ko face book ko exter gram"dasai muyi fira ta chats"amma kina fama da baby nokia aida matsala....sosai abin yayiwa jidda zafi"tana ganin ai laifin Abdul ne dabai siya mata babbar waya ba"kuma shi yanada wayar babba ai, k'in mgn tayi ta wuce ciki"Abba na tsakar gidan yana alwalar sallar magrib jidda ta shigo gidan bbu ko sallama"K! Abba yadakatar da ita"tana wani cin magani ta tsaya"dg yau nakoma ganin kina taramun maza a k'ofar gida ranki zai b'aci"kisa nar mun wanda kika fidda yaturo iyayensa Ayi mgn....ah ah gsky abin baikai hakaba! wace irin mgn ce haka mlm?"wannan ai rashin adalcine"ka bari ta zab'a ta durje sannan ta fitar"tunda Allah yabata farin jini ai dole ta kula maza ko?"ga wasu nan bbu farin jinin muna gani bbu mashin shini"cewar magajiya tana yin tsaye abakin k'ofar d'akinta data lek'o"jidda ta tab'e baki ta wuce ciki"tana gunguni"Abba ya ajiye buta yana dagowa yakalli magajiya"yasan yanzun yadawo gidan" kuma girkin tane amma ta masa banza bbu sannu da zuwa" sbd be dawo da leda ba ahannunsa"saidai sahura ce gudar matarsa ta masa sannu da zuwa ta zuba mishi ruwan alwalah"amma gashi dg yayi zance Akan jidda ta fito bbu shiri tana mgn harda yada habaici wa matarsa" fuskarsa ad'aure yadubeta tanata wani cika tana batsewa ita ga mai y'a"Abba ya girgiza kansa yace"magajiya kenan!! ina jiye miki YAU DA GOBE ta juyo kanki"shin ke wace irin UWACE ke? kaga mlm dan Allah ka barni"kaidai bakaine ka haifi jidda ba"ko baki kamata bazai bitaba"dan Allah ka tursasa y'ar ka bilkisu ita ta fitarsa mijin "in kuma gajiya kayi da zama dani bbu matsala"ran Abba ab'ace yaja tsaki yafita dg cikin gidan bai tankataba"magajiya na mita tabi jidda d'aki"batare data damu dasu fito suyi alwalar sallar magrib ba........jidda na zaune tana duba kud'in da Abdul yabata"washe baki magajiya tayi tana cewa"wannan kud'in fa y'ar lelena? tab'e baki jiddan tayi yace"kud'in ankon maryam ne dubu 10 da Abdul yabani yanzun"tsaki magajiya taja tana fad'in na rasa ubanme kika gani ajikin matsiyacin yaron nan dakika manne masa?"sai kace tsiya kansa ta k'are dazai baki dubu 10"ni yanzun bazaki bani komai ba aciki?"gsky da sake yaron nan be dace dakeba jidda"burina ki auri mai kud'i yadda zan huta mak'iyanmu suji haushi"wlh nima inada wannan burin ummah"amma Abdul daban yake acikin maza ummah" duk cikin mazan dake cewa suna sona ban tab'a had'uwa mai kyau da kamala irin saba"kyawun banza bbu zufar aljihu"ki rabu da d'an wahala kawai"shiru kawai jidda tayi dan da wuya ta iya rabuwa da Abdul......

Ak'afa yaya Abdul ya iso gidan su dake *Alkanchi*" tafe yake cikin yanayi biyu na damuwa"b'acin ran da jidda ta hadda masa da yanayinsa daya sauya"sai kuma far gaban me zaije yatarar agida?"tafiya yakeyi cikin nutsuwa yana tunani"wasu da yawa na masa kallon yanada girman kai sbd kyawunsa"bayan abin ba haka bane....anutse yashigo gidan nasu"asoro yatsaya yabud'e k'ofar d'akinsa ya ajiye wayarsa da zobbansa na azurfa"yafito ya wuce cikin gidan"gabansa har bugawa yakeyi sbd besan me kuma yanzun *goggo* zata fad'a akan saba?" matsakaicin gidane namai rufin asiri sosai"dan bazamu kirashi gidan talakawa ba"sallamarsa yayi Ahankali yana k'arewa tsakar gidan kallo"d'aki biyune jere cikin baranda"sai kitchen da toilet"tsakar gidan share k'al agoge"hakama tayis d'in dake jikin bango dake a baranda shima k'al yake"gidan bbu laifi yanada girma sosai" *meenah* ta lek'o dg cikin kitchen tana amsa sallamar yayan nata tana murmushi tace"yaya Abdul"duk yau bangankaba?"d'an murmushin daya fito masa da tsantsar kyawunsa yasaki kafin yace"ina shago shiyasa autar mu"dariya tayi tace"ka kyauta yaya"bara na zuba maka ruwan alwalah"tafad'a tana fitowa dg cikin kitchen d'in"yah Abdul ya zauna gab da maguji yana zare takalmin k'afarsa sawu ciki yana nad'e hannun rigarsa irin colour d'in jeans d'in jikinsa"yyinda meenah ke k'ok'arin zuba masa ruwan alwalah a buta"tana k'are masa kallo aranta tana fatan Allah yabata masoyi mai kyau"dan tasan yayanta k'arshe ne wajen kyawun"......motsin me nakeji wai?"cewar wata dattijuwa da zatayi kimanin 52 yrs data fito dg cikin bed room d'inta" tana dg tsaye tana hangensu"ta wani d'aure fuska"tana jifar yah Abdul da wani irin mugun kallon dayasaka yayi k'asa da kansa"ke mai damun ruwana ba zaiyi mun alwala agida ba"uban me yake tsinanamun agidan??"kullum aikinsa shine kiran fatara da tsiya"wani yasiyamun ruwan" shi yazo ya amfana dasu "to bazai yuyuba"yo ina amfanin haihuwar d'a marar galihu irinka?? bakada wani amfani aguna wlh" tafad'a bakinta har kumfa yakeyi"cikin wani yanayi meenah tace"........โœ๏ธ

karki bari wannan book d'in yawuceki akwai abubuwa da yawa aciki yi k'ok'ari ki biya ta wannan hanyar ๐Ÿ‘‡


wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day

zaku biya kud'in ku ta wannan acc number๐Ÿ‘‰2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne

banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraโŒ

Y'an nijar kutuntub'i wannan n๐Ÿ‘‰ +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
special people 2000f

dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyabaโ€ฆ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒน๐Ÿคฑ๐ŸปWATA UWAH ๐Ÿคฑ๐Ÿป๐ŸŒน

๐Ÿ™†๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ(RAYUWAR ABDUL) ๐Ÿ™†๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
mommyn fareesa


wannan shafin nakine halak malak kiyi yadda kikeso dashi zqinab hamisu wada๐Ÿ’“๐Ÿฅฐ

free ๐Ÿ…ฟ๏ธ 3&4

.......cikin wani yanayi meenah tace"haba goggo! alwalah d'in ma hanashi zakiyi yayi dan Allah? meyasa bakya yiwa yaya Abdul adalci?" fad'amun yadda zanyi dan ubanki"cewar goggo afusace tana tunkaro meenah dake tsaye"yah Abdul yamik'e tsaye zuciyarsa na wani irin zafi ya k'ak'aro murmushin yak'e yana fad'in meenah jeki Ida aikinki"goggo kiyi hak'uri zanje masjeed nayi alwalah d'in acan"yafad'a cike da ladabi"goggo taja tsaki had'e da cewa"ina ruwana ma da Inda zakayi?"ke kuma kutsugagga ki fita dg idona na rufe"zaki tafi ki bani waje ki idamun girkina ko kuwa?"hawaye na tausayin yah Abdul suka wankema meenah fuska"tana girgiza kanta tace"goggo Inda badan inada tabbas kece mahaifiyar muba danace ba kece kika haifi yaya Abdul ba.... ji kikeyi tass! goggo ta d'auke meenah da mari mai rai da lafiya tana mara dakk'uwa"yah Abdul ya girgiza kansa bece komaiba ya juya yafita"goggo ta dinga masifa da bala'i"meenah batace komaiba ta zuba ruwan tayi alwalah d'in tana kuka"kafin ta koma kitchen d'in ta duba girkin sannan ta wuce parlourn.....
bayan sallar magrib yaya Abdul yashigo cikin parlourn goggo"tana zaune kan kujera tana kallon tv kamar tasan me suke fad'a"sau 3 yanayin sallama Amma ta masa banza"k'asa kan carpet yazauna ya sunku yadda kansa ak'asa Ahankali yace"goggo sannu da gida!"kaga dan Allah bana son takura"akanme zakazo kamun zaune?"yah Abdul na k'ok'arin mgn meenah tashigo parlourn da plate d'in abinci a hannunta na shinkafa da miya da nama" ta ajiye gaban yah Abdul"wlh meenah idan bakiyi hankali daniba saina miki baki"dan ubanki dani dashi wa kikafi so?"haba goggo menayi kuma?"oh bakisan me kikayi ba kenan?meenah na k'ok'arin mgn sukaji sallamar yara suna fad'in ance gashi"washe baki goggo tayi tana mik'ewa tsaye" kamar zatayi tuntub'e ta fita tana fad'in da alama d'an albarkane yabayyanah"meenah ta girgiza kanta tana bin yah Abdul da yayi tagumi"da kallon tausayi yad'ago kansa suka had'a ido"d'aure fuska yayi yace"dg yanzun komai goggo zatamun ko zata fad'a akaina bance kisa mata baki ba"ki d'auki abincin ki mayar banaci"yafad'a murya adake"dukda yana jin yunwar amma bazai iya ciba"meenah na k'ok'arin mgn goggo ta shigo d'akin da kaya nik'i nik'i a hannunta tana fad'in wayyo Allah haihuwar mai arzik'i tayi arayuwa"dana haifi talaka gara na haifi mai arzik'i"yo miye ribar haihuwar fatararre Allah natuba?"ke meenah maza kwasomun sauran kayan can dake acikin baranda"meenah batayi mgn ba ta fita"yah Abdul yayi k'asa da kansa yana mamakin sbd bedashi kawai mahaifiyarsa ta tsanesa?"Assalamu Alaikum! cewar kabeer yana shigowa cikin parlourn"da kallo nabi d'an lelen na goggo wanda bbu alamar tarbiyya atare dashi"yana sanye da k'ananun kaya"jeans d'in yayi k'asa har boxer nashi ana gani"yabar uwar suma cike da kai"ya zauna gefen goggo yana fad'in my mom na sameku lafiya?"lafiya qlau kabeer ya habujan ?"sannufa da hanya d'an albarka"yauwa mom(haka yake kiranta sbd yafi k'arfin yace"goggo)kallonsa ya maida kan yaya Abdul yace"yaya sannu gida nasameku lafiya?"lafiya qlau kabeeru"ah ah dakata ! bana son rashin tsoron Allah akanme zaka b'atama d'ana suna??yazo baka masa mgn ba"sbd kana masa hassadar yafika"saidai shine yafara maka mgn"idan baza kace kabeer ba ka bari"basar kawai mom"cewar kabeer yana d'aga wa goggo hannu"hakan yayi daidai da shigowar meenah parlourn"yah Abdul beyi mgn ba sbd beson raini amma yaji haushin kalaman kabeer""itadai ta masa cin fuskar data keso zai hak'ura tunda mahaifiyar sa ce" amma bazai d'auki raini agun na k'asa dashi ba"ya mik'e tsaye yafita"goggo ta tab'e baki "meenah na dg tsaye tace"yaya kabeer sannu da hanya"yauwa sis"tayi d'an murmushi tana jawo plate d'in abincin da yah Abdul be tab'a ba zata ajiye agabansa"goggo tayi saurin dakatar da ita gun cewa"kinga ki canzo masa wani"tunda shi wannan zalamammen beciba"kabeer yyi saurin cewa" mom ta barsa gsky dan bazan iya cin girkin taba dan is local"ba girmana baneba ,wannan villager girl d'in tayi girki naci "abarshi naje restorent naci kawai"hmm yaya kabeer kenan! rayuwa batada tabbas"ada kafin kayi kud'in ince irin wannan abincin kakeci koma wanda bai kaisaba ko?"wata uwar tsawa goggo ta dako mata"bbu shiri tabar parlourn tana mamakin halin mahaifiyar tasu....goggo kuwa firan yaushe gamo sukayi tayi da kabeer kafin ana kiran isha'i yasanar mata zai tafi masaukinsa yahuta da safe zai dawo"dan baya kwana agidan Idan yazo sai hotel duk time d'in daya zo.....
bayan fitarsa ,meena dake zaune atsakar gidan ta share hawayen ta"ta shigo parlourn ta zauna ta dubi goggo daketa duba uban kayan shopping da kabeer yamata tace" wlh koda kasheni za'a yi bazan dena fad'in gsky ba "domin ana nuna banbanci sosai agidan nan k'arara"sannan na yarda da ake cewa" duk wanda yake da kud'i agdnsu to shine Alh komin k'arantarsa "gashi nagani anan gidan"kwata kwata yah Abdul ne babba agdn nan amma sbd bashida kud'i an maidasa k'arami! komai sai yah kabir shine na kirki me kyan hali mu duk b.....cikin tsawa goggo tace" wlh ko kimun shiru ko namiki shegen duka "ai dukiyar kabeer ta miki rana dan ubanki"tunda da ita kike ci dasha da hidimar karatunki"fita ki bani guri shashar banza kawai....

yah Abdul kuwa yana fita shagonsa na d'inki yanufa"gaba d'aya duniyar ta masa zafi"amma dukda haka ya fawwalawa Allah komai"shagon abud'e yake sbd wanda suke atare ashagon suna d'inki yafito"kasancewar akwai nefa shagon da haske"yana shigowa wayarsa nayin y'ar k'ara alamar shigowar message"musa abokinsa na zaune kan kujerar da yah Abdul ke zama"kallo d'aya yayiwa abokin nasa yasan yanada damuwa"d'an murmushi yah Abdul yasaki yana fad'in na hak'ura my jiddo nah"yafad'a yana koma karanta message d'in da jidda ta turo masa naban hak'uri da nuna kulawa"tab'e baki musa yayi sbd yaji abinda Abdul yafad'a"shifa harga Allah aransa" be son soyayyar Abdul da jidda sbd wasu miyagun halaye na jidda"saidai yanayin shurune dan yafahimci Abdul d'in na yiwa jidda wani irin zazzafan SO"wanda da wuya ya iya rabuwa da ita"
kallon tausayi musa yyi masa" dan kaf yasan halin da yah Abdul yake ciki da kuntatawar UWA! dan bayada wani amini sama dashi, sun yarda d junansu ,su kashe su rufe a tare.....
Ango Ango!! cewar yah Abdul yanajan sit ya zauna"musa na murmushi yace"bakada kirki abokina 3 days kenan rabona dakai"nadubaka ta online naga kajima baka hauba"hakane abokina"amma kana Ango miye ya fiddoka awaje?"gunka nazone ai"muje dg waje"okay yah Abdul yafad'a suna mik'ewa tsaye suka fita"nura dake d'inkinsa yatab'e baki"dan yatsani yaya Abdul dukda bai masa komai ba"hakanan yakejin zafinsa"bayan kuma yah Abdul d'in shine yanemi alfarma

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login