Showing 54001 words to 57000 words out of 114964 words
kawar da ni, ya dauko documents din data dauko a dakinsa, ya bisu da kallo kafin ya kuma yin wata murmushi yace, kuna tunanin kunyi girman da zaku kawar dani ne, kinyi kuskure Latifa now that I know exactly what he's up to, bazan barshi yayi succeeding mission dinsa ba, I'll teach him a great lesson, she'dan nun da suka fisa she'dana ma sun ganni sun barni balle shi 'karamin 'kwaro. Snn ke kuma idan kikayi gigin tona asiri na zan kashe Momyn ki snn na kashe Aliyu, na kuma ci gaba da hole rayuwata dake. Dan haka I warned you to shut your mouth.
"Banda kuka babu abunda Latifa take yi, she just couldn't believe what is happening...
"Can dare ta soma mutsumutsun farkawa, tana bude ido da salati ta ganta a wani waje daban, momma dake kwance kan wata kujera ta taso da sauri tana mata sannu, da mamki Hanifa ke bin momma da kallo dan taso gano fuskar matar, ta yun'kura zata tashi taji hannunta da 'kafarta sun mata tsami, ga bandage manne a jikinta tas hannu ta ta'ba goshinta taji bandage.... muryan momma ne ya katse mata tuno abubuwan da suka faru, wani sabon kuka ta sake, nan momma ta shiga rarrashinta tana fadin ko na kira Dr ne. Girgiza kai Hanifa ta soma ta share hawayen da suka zubo mata. "Momma ya akayi nazo nan, murmushi momma tayi tace mummyn Amal ashe zaki gane ni. Nan momma ta bata labarin ka'de ta da Sameer yayi har kawota asibiti.
"Hanifa ta share kwalln ta tace, nasan wani ya kade ni da mota daga nan ban sake sani yanda kaina yake ba sai yanzu, Allah na gode maka da kasa na fa'da hannun bayinka na gari, Allah na gode maka daka ku'buto dani daga hannun azzaluman bayinka.
"Da mamki momma ke kallonta kafin tace, wai me ya faru dake ne, me ya fiti dake waje a daren nan har aka buge ki.
"Wllhi momma wasu azzalumai ne ke bina shiayasa, amma yanzu Alhamdullah tunda nazo hanun na gari. "Murmushi momma tayi ta rike dayan hanunta maras drip tace "'kwarai kuwa kinzo yanda no one will harm you inshaAllah. Murmushi Hanifa tayi momma tace ko na kira likita ne, "a'a momma ai dare ma yaja kuma banji komai sai tsamin jiki, momma tace Alhamdulillah Allah 'kara maki lafiya. Ameen momma. Nan Hanifa ta shiga tambayan momma Amal, momma ta bata labarin rigimar da Amal take masu akan sai an samo mata mummynta da draman da sukayi yau da momma.... Hanifa tayi murmushi tace Amal knn, sarkin magana. Momma tace ai kaman ba Sameer bane ya aifeta, shi bayada hayaniya sai iya tsara zance abunki da lawyer. Sukayi dariya su duka biyun, hira kadan suka ta'ba kafin suka koma barci.
*Washe gari*
7:15am
"Barrister Sameer ya bude wa Amal front seat ta shige, tana faman zuba masa surutu, daddy ni bana son momma tana mun masifa, ni mummy na nake so ka samo mun, murmushi yayi mai bayyana ha'kwara ya shafi kan Amal yace, yanzu zamuje kiga mummyn naki, idan munje ki gaisheta bata da lafia, and don't talk too much okay. Tsalle tayi daga zaune tace yeey finally daddy ka samota, ta daga tafin hanunta tace I promise I won't misbehave daddy. Murmushi yayi yace " ehen that's my girl.... da haka har suka isa asibitin. Yana gama parking ya dauko basket din abinci da asabe ta hadawa su momma, ya riko Amal dake sanye cikin uniform dinta da daya hannun suka nufi cikin asibitin,.......
👸🏻Queen Samy😍💄💋.......
[5/21, 5:35 PM] 🌹 Muhammad🌺kabeer🌹: 🌹🌹🌹 *Mijin Haneefah*🌹🌹🌹
50
"Hanifa tana jingine jikin pillow, momma na zaune saman kujera suna dan ta'ba labari su Sameer suka yi nckn, momma ce ta bada izinin shigowa bayan Hanifa ta rufe gashinta da sirirn veil din dake ma'kale wuyanta.
"Amal ce ta shigo da gudu ta haye jikin Hanifa, nan fa momma ta shiga mata sababi, " yawwa kinzo zaki soma ko, toh saura ki 'karasa ta, murmushi Hanifa keyi ta shiga biyewa Amal da surutunta, gaba daya bata lura da Barrister ba sai jiyo muryansa tayi suna gaisawa da momma. Bata dago ta kallesa ba saida yace "yaya jikin naki, ya fadi yana dubanta. "Kallo daya ta masa ta sunkuyar da kanta kana tace jiki da sau'ki Alhamdulillah. Masaha Allah, Dr din bai iso ba ko, ya fadi yana duban momma. "Bai iso ba sai 8 momma ta fadi. Kallon Hanifa yayi yaga tanata faman tadi da Amal. Gyaran murya ya danyi kafin yace "babu yanda ke maki ciwo ko, girgiza kai tayi snn tace babu. "Ok ni zannkai Amal sch momma daga nan zan wuce office yanda kukayi da likita sai na sani. Momma tace toh Allah bada sa'a, ta jawo dan hijabin Amal tace "wato ba kya gaisheni ba sabida kinga mummynki koh, turo baki Amal tayi ta kar matsawa jikin Hanifa, saida Barrister ya riko hanunta da lallashi kafin ta yarda suka fice daga asibitin . Momma tayi serving Hanifa tasta cin abincin dole, Sosai Amal ta shiga ran Hanifa....
"Har rana ta fito beyi shirin fita office ba, yana zaune so miserable, Aisar ya dubasa a office dinsa bai gansa ba, ya kira wayansa yafi abunda yafi baya dagawa 'karshe ya kasheta gaba 'daya. Excuse Aisar ya dauka ya nufo gidan Haidar.
"Zaune ya samesa a parlor ko wanka beyi ba, Haidar yana ganinsa ya mike cikin kunan rai yake fadin " what are you doing here you coward,
"You need to calm down Haidar, let's talk about it.
"Get out of here, ka fita Aisar, I think I've made this clear to you, bana son ganinka, I hate you like hell, just leave pls.
"Fine naji zan fita but you need to get ready for the office.
"Ubana bazanje ba, Dmmn it, is none of your business idan na rubuta retire yanzu, kai barin fada maka your good intentions are not needed, I think it will be much more better if you leave.
"Haidar am not leaving here until you explain everything, everything to me.
"Galala Haidar ke kallonsa kafin yace" Why do I have to do that, meyasa zan bata lokacina wajen maka bayani inspired of everything thwt had happened. It's pointless, you know what Aisar, ka tafi pls let me be alone, you are just making things worse.
"A dole Aisar ya tafi ba don yaso ba, yayi reporting a office cewa Captain Abubakar is sick.
"Haidar yana tashi stations ya sake bi daya bayan daya yana tambayan ko an tsinci Hanifa amma shiru, yana son sanarw a kafafen watsa labarai yana tsoron ya iso wa su Abba, iyaka gidajen radio da television na jihar lagos kawai ya kai sanarwan da hoton Haneefah, haka ya kare day dinsa a binciken Hanifa amma shiru kome kama da ita bai samu wanda yace ya gani ba. Idan kaga Haidar sai ka tausaya masa d'an kwana 'daya da yayi babu Hanifa.
"Tun yamma likita ya sallameta, kai tsaye gidan su Barr Sameer suka nufa wato gidan momma, bayannta huta ne momma tace ai ya kamata a maidaki gida kila suna can suna kan nemanki.... take annurin fuskan Hanifa ya dauke. "Barr ne ya shigo bayan ya gama jin cikiyan Haneefah a radion motarsa gaba daya kammaninta da kayan jikinta an zayyano. Waje ya nema ya zauna kafin yace, momma ai gwara mu maidata gida dan naji cikiyanta a gidan radio.
"Zaro ido Hanifa tayi tace "daddyn Amal dan Allah karku maidani wllhi kasheni zasuyi..... Sameer da momma da mamaki suke kallon juna. "Momma tace su waye zasu kashe kin wai dama ba an nan garin kuke da zama ba. "Kwalla ya ciko idon Hanifa tam rasa me zata fara fa'da masu take dabara ta fado mata ta soma fadin.
"Dama nida yayana muka zo nan shi yana aiki a nan lagos ni kuma ina karatu, toh a gidansa nake zama, kullum sai ya rinka kawo abokansa maza da mata suna hole rayuwarsu, ni kuma gaskiya abun na damu na, a haka har abokan nasa suka soma daura ido akaina, koda na fada masa banza dani yayi yace mun wai nan bariki ne na saki rayuwata nayi yanda kowa keyi, ni kuma harga Allah bazan iya sa'bawa mahallici na ba, kuka ya kufce mata sanda take fadin, koda ka ka'de ni a titi ina gudu, tsere wa abokan nasa masu shirin mun fyade nayi...... kuka yaci karfinta, gaba daya jikin momma da Sameer yayi sanyi, salati kawai momma keyi suna jinjina lamarin, Hanifa taci gaba da fadin dan Allah ku barni a nan har na gama warkewa kadin ku maidani garinmu wajen iyayena.....
"Zuciyan Sameer kaman ta fashe jin wasu suna shirin yin fyade wa abar kaunar shi, ji yake inama ya gansu yanzu da ya kashesu one by one.... cikin 'kunan rai yace, "wnn ba abunyin shiru bane, they need ro be punished, dole a gurfanar dasu a gaban hukuma..... da sauri Hanifa ta dago kai tana dubansa gani tayi ransa yayi mugun baci kafin tace" a'a daddyn Amal, ni na barsu da fitowan rana da faduwarta Allah zai mun sakayya, na gode wa Allah da basu ci nasara akai na ba, karatu kuma na hakura da yinshi a nan zan koma gabn iyaye na. Na godewa Allah da ya ha'da ni da mutane kaman ku.
"Momma ta sau'ke ajiyan zuciya, Sameer kam fuzar da iska yayi daga bakinsa snn ya fice a parlor dan gaba daya ransa a jagule yake.....
"Yau kwanan sa uku be ko le'ka Office ba, I zuwa yanzu kam abun yayi affecting dinsa sosai, kana ganinsa kaga abun tausayi, masu gadinsu ma abun duk ya damesu, mutum kaman Haidar wanda baya wasa da batun aiki, wanda duk abunda yasa a gaba toh sai kaga nasara cikin ikon Allah, amma yanzu kam ko ganinsa basa yi. Ga aiki ya taru masa a office saukinsa daya Aisar yayi reporting bashida lafiya da abun ya shafi aikinsa, ko kadan Haidar bai damu ya rasa komai a yanzu ba tunda ya rasa Hanifa, bakle wani banza so called job.
"Ran kwana na hudu da 'batan Hanifa kasa hakura yayi dole angulu ta koma gidanta na tsamiya, giyansa ya samu yayi tatul dashi nan ya jisa a sararin samaniya. Kaman wanda aka zabura ya suri car keys dinsa duk da layi da yakeyi be hanasa driving ba.
"Latifa da ta kasa hakura da dokan da dad dinta na ganin Haidar yau ta saci 'kafa ta fito ta nufo Maritime ko zata gansa. Tana tafe kaman daga sama ta hangi motansa motansa yana fita daga layinsu, ai kuwa nan ta shiga bin bayansa, Haidar be zarce ko ina ba sai Office dinsu, yana gama parking kuwa, sojoji suka shiga sara masa tun kan ya fito. Latifa tana hango yayi parking tayi parking motarta a gefe ta nufo sa, kaman ace ya daga kai sama ai kuwa ya hangota.
"A sittin Haidar yayi kanta ya ma'kure wuyanta yana fa'din " this is all your fault... cikin muryan maye, yaci gaba da fadin, sai na kashe ki wllhi sai na kashe ki you bitch.... nan fah attention din mutane ya dawo kansu. Babu yanda basuyi ba su kwace Latifa abu ya gagara Haidar ya sha'ke wuyanta tana kakarin numfashi. Nan fah cikin sauri aka nufi ofishin Admiral dad dinta aka sanar dashi, Aisar na daga floor dinsa yaji hayaniya, a sittin ya fito ganin Haidar ya ma'kure Latifa kaman zai kaita lahira......
"Let go of my daughter, Admiral yake fadi kan ya karaso wajen, Aisar ne yayi saurin fincikan Haidar yana fadin " What's all this Haidar, don't make a sin here, kallon daya masa ne ya gane a buge yake, da mamaki Aisar yace "are you drunk? Ko kallo be ishe Haidar ba shidai kawai a barsa ya kashe Latifa.
"Admiral yace kunajinsa ko duk abunda ya sami 'yata shine, tunda gashi yun'kurin kasheta yake. " Haidar na tangadi ya 'karaso gabansa yana nunasa da yatsa yake fadin " You Worthless basted am not done with you yet, you won't get away with what you did,...... ganin Haidar ya nufi Admiral na masa magana haka yasa sojoji suka nufo Haidar, harara ya galla masu don yafi su matsayi kafin yace " don't you dear come near me. Aisar ne ya fuzar da iska ya shiga jan Haidar yana turasa cikin mota, Haidar yana fincika yaci gaba da nuna Latifa dake kuka tana sosa wuyanta yanda ya sha'keta snn yace " Am gonna kill you, you bitch, Mark my word.
"Da kyar Aisar ya jefasa cikin mota ya nufi gida dashi.
" Babban abun kunya Haidar yayi wa Naval Chief Of Staff guda, gaban kowa gaban Recruits dinsu, rai 'bace ya fizgo hanun Latifa ya nufi office dinsa da ita. Suna shiga ya shiga mata sababi, " So are you happy now, burinki ya cika tsinannen yaron nan ya watsa mun 'kasa a gaban yarana, barin fa'da maki babu ke babu fita daga yau, Latifa dai banda kuka babu abunda take, bata san me tayi wa Haidar da har yaje wnn fushi ba.
"Urgent meeting Admiral. Ya kira, nan da nan manyan navys suka hallara, yana zaune a center ya mike ya so a magana. Regarding abunda Captain Abubakar yayi earlier ya canci a koresa daga aikin navy gaba daya, if possible a hukuntasa ma tukkuna. Da yawan manyan navys sunki singing kan a kore Aliyu. Ran Admiral. sosai ya baci ya shiga nuna masu irin ta'asa da furucin da Haidar yayi akan diyarsa. Dukda haka da yawa basu yarda ba sai 'kalilan, wanda haka dole yasa aka kawar da batun ba don Admiral yaso ba, amma ya dau alwashin sai ya kawar da Haidar a doron 'kasa......
"Aisar yana gama parking ya fito da Haidar daga cikin mota da kyar ya nufi cikin gida dashi, hararansa kawai Haidar keyi can yace " wai kai maye ne, thought I told you to stay away from me, na tsaneka you idiooot.... yana gama fadin haka ya zube bisa carpet bacci yayi gaba dshi.
"Aisar ya zauna ya zuba masa ido sosai tausayinsa ya kamasa, ya tuna Haidar ne ya masa wa'azi ya daina shan giya gashi shi ya koma ruwa, lallai Haidar yana tsananin son Hanifa, ya 'dau alwashin taimaka masa wajen nemanta. Ya mike ya gyarawa Haidar kwanciyansa kafin ya fice, yana fita stations ya kara dubawa koda case din tsintuwar Hanifa amma shiru. Ya jima yana zagaye har mutane yake tsarewa a titi yana nuna hotonta ko sun ganta amma babu wanda yace yaga mu kamanta. Haka har dare ta kusa yi Aisar na abu daya Sallah ne kawai yake dakatar dashi.
"Haidar yana farkawa yaga tulun kwalaben beers da yasha, kuka mai tsuma rai ya kufce masa, gaba daya ya zamo tamkar mace bai sanin sanda hawaye ke zuba idonsa, mutumin da tun tasowarsa da wuya kaga abunda zaisa kuka sai gashi yanzu kuka ta zama masa jiki, tattara kwalben yayi yayi jifa dasu ya rinka fasa su, ya dau alwashin gobe insha Allah zai yi confronting iyayensa, wata zuciya tace kilama Hanifa tana Kano, da wnn tunani ya dan samu nutsuwa har ya gabatar da ibadunsa....
👸🏻Queen Samy😍💄💋........
[5/21, 5:35 PM] 🌹 Muhammad🌺kabeer🌹: 🌹🌹🌹 *Mijin Haneefah*🌹🌹🌹
51
"Misalin karfe 8:12pm, Aisar ya shigo gidan, zaune ya sami Haidar saman darduma da alama sallah ya ida, zama Aisar yayi saman kujera yana kallon yanda abokin nasa ya koma tamkar wanda ya jima yana cuta a 'dan kwana kin nan. Can ya mi'ke ya nufi kitchen ya fito da plate fork, zama yayi ya bude takeaway da ya shigo da shi ya shiga zubawa a plate din, chips ne da egg with leaver sauce, Aisar ya ajiye gaban Haidar yace " I know you must be hungry, nasan you haven't eaten anything since morning. "Banza Haidar yayi dashi kaman bainsannda hallita a wajen ba, Aisar yayi gyaran murya yace " Haidar dan Allah kayi hakuri, wllhi ni bani da masaniya akan abunda Latifa tayi, wllhi ban shirya komai tare da ita ba, believe me friend bazan iya blackmailing dinka ba, kasan haka Aliyu.
"Har lokacin Haidar be ko kallesa ba balle ya tankasa, sunfi minti biyar a haka, can Aisar ya mike yana duba wristwatch dinsa, sauke ajiyan zuciya yayi kafin yace "na kai cigiya tashoshin mota da airport, insha Allah zamu dace, pls Haidar kaci abinci ko kadan ne, ni zan wuce gida.
"Sai snn Haidar ya dago ido yana dubansa, har Aisar ya isa kofa ya tsinkayo muryan Haidar yana fadin " am leaving tomorrow, thanks for your kindness, duk da nace maka bana bu'kata. Daga haka yayi shiru bai kuma cewa komai ba ya kauda kai gefe. "Murmushi Aisar yayi yace Allah ya kaika lafia Haidar snn Allah yasa mu dace, zan zo da safe kafin ka wuce.
"Ba sai kazo ba, na gode, ya basa ansa a takaice. Sallama Aisar ya kara masa kafin ya fice.
"Washi gari jirgin 'karfe 2:00pm Haidar yabi zuwa Kano.
"Misalin 'karfe biyar da rabi taxi ta ajiye shi a kofar gidan mahaifinsa, take yaji zuciyansa ta kuma karaya, idan kaga Haidar baka ce shi bane duk ya zama wani sukuku abin tausayi,