Showing 69001 words to 72000 words out of 87071 words

Chapter 24 - Budurwar Kauye Hausa Novel

07 Oct 2024

13118

yakeyi yana tuna yanayin daya samu kansa aciki

Lalle Allah yayima Fauziyyah baiwa iri da ban da ban

Da tunaninta bacci yayi gaba dashi harda mafarki barkatai

*****
Yana fita tasamu ta miqe da kyar ta shiga cikin bedroom nata

Wanka tayi itam cos taga baqon abu atattare da ita sai anan tadanji qarfin jikinta

Falo tadawo ta zauna bude abinda ya kawo mata

Shawarma ce anade da duminta sai aroma dake tashi

Dayan kuma takeaway na gasmeat ne

Haka taci ta qoshi ta kora ruwa mai sanyi sai bacci nan tashige daki abinta ta kwanta

Sai dai sam bacci ya gagareta sai tunani papa daya addabeta lalle ya alamin ya iya luv abinda tafada aranta kenan

Tundaga ranan tasauya salonta bata taba yadda papa yayi koda qaramin wasa da ita

Daya kusantota zata fara kuka tana cewa idan yana qaunar Allah yarabu da ita tunda ba dole

Shikuma bai kaunar yabata mata rai haka zai kyaleta

Gashi kullum cikin tayar masa da hankali take wajen daukar wanka da kaya masu jan hankali

Kullum burinsa ya kyautata mata aikin gidama kusan 50-50 sukeyi kafin ta tashi zai rigata tashi yayi shara mopping ya kunna burner ko ina ya bule da qamshi

Amma abanza Fauziyyah batada niyyar sauqowama dan yanzu maganama bata cika hadasu ba yayi iyaka yinsa harya haqura ya kyaleta saidai baifasa kyautata mata da fada mata kalamai masu dadi na soyayyah ba


*2months later*

Yanzu kimanin watansu biyu da aure kenan

Kullum papa baida abinda ya fice ganin ya kyautatamata ya sanyata farinciki

Ko office ya fita harya dawo hankalinsa yana gunta

Ya sayo mata wannan wancan dik dan ya birgeta yakeyin hakan

Damuwarsa daya yadda yake fama da shaawarta amma ita batada niyyar saurara masa haka yake danne zuciyarsa

Afannin fauziyyah kuwa tun tanajin wani baqon Alamari gameda papa

Tunbatasan mene neba harta fahimci zuciyarta takamu da sonsa

Ahankali ta fahimci lalle zuciya tana son maisonta kuma mai kyautata mata

Wani irinso takejin tana masa wadda bata taba yima wani mahaluqi ba

Takuma gane ashe yasirma son yarinta tamasa

Saida kuma ta gagara daina quntata masa dikda komai zata masa bai nunawa at last ta realizing cewa lalle papa yanasonta sona haqiqa na gaskiya

Amma ta gagara nuna masa hakan koyaushe saita ringa nuna masa baigabanta sam kuma ta gagara daina hakan dan yanzun dakanta idan tamasa abu saiya dameta taji dama bata aikata hakanba

Amma abubuwa da dama taragemasa tunda idan tamasu abinci komabai kusa data leqa dakinsa dikda iyakarta bakin qofa tace yazo suci abinci sabanin da sai dai insanda yafito dan kansa

Yau dawuri ya taso office itakuma batajeba kasancewar Friday ne

Da yamma lis yasmeta zaune afalo

Barka da hutawa baby yafada fiskansa dauke da qayataccen murmushi

Uhum kawai tafada batareda da ta dago ba daga danna wayarta datake

Barinje gidan aunty naja dagacan zanwuce masjid sai after isha zandawo

Ok kawai tafada shikuma ya wuce dan inda sabo yasaba da halin ko inkula datake nuna masa

Yana wucewa tabi bayansa da kallo harya fice sannan ta zame ta kwanta tana roqon Allah yasa ta sassauta zuciyarta ta kyautatawa mijinta

Yana fita gidan Aunty Naja ya nufa afalo yasameta suna kallo itada da yara kasancewar friday babu islamiyyah

Yana sallama oga ya taso da gudu ya rungumesa yana oyoyo uncle

Papa ya dgashi sama yana cewa oyoyo my boy

Zama yayi ya daura oga akan cinyansa suna gaisawa da aunty

Bayana sun gaisa tacema su sopy oya kuwuce dakinku kuje kuyi kallon acan

Ta dubi oga daya dane cinya tace harkaima dakake wani lafewa tashi kabisu

Papa yace da anbarmin abokuna ai

Tace rabu dashi damunka zaiyi da qiriniya

Bayan sun wucene ta dubi papa tace ya Fauziyyah dai yanzunkam komai normal ko

Dan sosa qeyarsa yayi yana cewa umm ai rikicecciyace ammadai yanzun tarage fitina

Tace banganeba wai haryanzun bakasamo kantaba

Cikin muryar tausayi yace ai aunty rikicinta sai a hankali

Da mamaki ta dubesa tace kada kacemun kaikuma zuba mata idanu kayi kake kallonta

Yace to yazan mata ninafison saita fara sona ta aminta dani

Tace so na biyu ko na nawa ai dik wanda yaje gidanku yazauna daku na awa daya zai fahimci fauziyyaha tana sonka kawai pretending takeyi kaikuma idanunka sun rufe ka kasa fahimtar haka

Yace to nidai kawai ina lallabatane muzauna lfy tinda banida option


Tace kana da option kuma cikin ruwan sanyi zaka samu kanta

Nan tafada masa yadda zaibi
Nidai banji maitaceba dan yadda tayi maganar ahankali

Sai kawai naga yanata dariya dan mganar dariya tabashi


Yace kai aunty bakida dama
Itanma dariya tayi tace kaidai kawai kayi yadda nafada maka


Saida aka kira sallan magriba yatafi

Baikoma gidaba sai bayan da yayi sallan isha tukun


Lokcin daya shigo bata falo yaji dadin haka sai ya wuce dakinsa

Toilet ya shiga yayi wanka da ruwa mai zafin gaske dik da shiba maabocin muamala da ruwa mai zafi bane sosai amma haka ya daure nan jikinsa ya dau dumi

Cikin sauri yasaka kaya ya shige bargo ya rufu

Baifi 5mins ba da kwanciya ta leqo falonsa taga bayanan saita leqo dakinsa taga koya dawo yafito suci abinci


Ahankali ta tura qofar ganin wutan dakin akunne yasa tafahimci ya dawo

Shiga tayi ta tsaya abakin qofa ganinsa akwance akuma qudundune cikin bargo yasa tayi tunanin lfy

Cikin sanyin murya tace kafito muci abinci

Murya na rawa kamar mai zazzabin daya masa mummunan kamu yace kije kici kawai bazan iya ciba

Harya juya saita kasa tafiya dan yadda tai voice nasa tasan ba lfy ba to amma mai yasamesa lokaci guda baicin dazun ya fita lfy lfy ta tambayi kanta

Juyowa tayi ta tako har bakin bed inda yake kwance sai rawar sanyi yake kamar gaske

Nanmada ta tsorata dayanayin data gansa

Hankali tashe tace ya Alamin mene yasa meka

Jin yadda tai maganar adame yasan tarkonsa ya kama bushiya

Sake shaqe murya yayi yace baby am sick banajin dadi fever ke damina

Fever tafada tana zare idanu

Daga kansa yayi irin bai iya amsawannan

Nam take taji wani tausayinsa ya dirar mata dan bata taba ganinsa cikin wannan yanayi hakaba

Sannu Allah ya sauwaqa amma lfy kafita ko dama kanajinsa ajikinka

Tai magnar tana miqa hannunta jikin wuyansa ta taba

Nan taji zafi zau.....



*Gaisuwa mai tarin yawa agareki Auntyn Papa Mmn Faty ta๐Ÿ‘๐Ÿป*




โœ๐ŸปFaty Mmn Faty




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

September, 2017



6โƒฃ4โƒฃ
Wani sabon tausayinsane ya dirar mata lokaci guda

Banda shaking ba abinda jikinsa keyi, kansa kawai ya iya gyada mata

Haka kawai taji bazata iya tafiya ta barshi awannan yanayinba

Zama tayi akan bedside drawer tadaura hannunta akan goshinsa

Murya ahankali tace toh kanemi magani kasha kaji tafada tana kallonsa

Murya ashaqe yace nasha bayan nashigo

Cikin tausayi tace toh Allah ya sauwaqa

Ganin yadda gabadaya yanayinta ya sauya ta shiga damuwa sai kawai yadan razana kamar wani abin tsoro yagani

Cikin sauri ta riqosa ta qanqamesa tana cewa subhanalillahi ya Alamin menene?

Sake razana yayi ya qanqameta shima aifa nan tafara kuka hawaye wani nabin wani tana cewa meya sameka kamin magana mana sai kuka take dik tafirgita da yanayinsa

Yadda hankalinta ya tashi sosai saiyaji tausayinta ya kamasa

Ahankali yake cemata relax baby ba abinda zaisameni haka fever na yake so ki kwantar da hankali kinji

Da muryar kuka tace aa kam kodai nakira momcy awayane akaika hospital

Aa baby kada kitayar masu da hankali nafarajin sauqi ma da yardar Allah zansami sauqi

Ganin yafara samun natsuwa ya kuma rungumeta ya lafe ajikinta yana sauqe numfashi yasa tadan tsagaita da kukan amma batabar hawayeba

Sunkai 10mins ahaka kafin ahankali yace baby zafi nakeji sosai

Zafi kakeji ya Alamin tafada tana goge masa zufan goshinsa

Gyada kansa yayi yace sosaima

Yaye masa blanket din tayi ganin dik jikinsa ya jike da zufa irin alamun sauqan zazzabi

Tace Alhamdulillah aizafin nasauqan zazzabin ne sannu ya Alamin Allah ya sauwaqa

Lumshe idanunsa yayi yace Amin baby nagode da kulawarki gareni

Murmushi mai sanyi tamasa tace bakomai kona qaramaka qarfin AC dinne

Yace qaramun baby , toh tafada tadauki remote din taqara masa qarfin AC din

Nan da nan sanyi mai dadi ya karade dakin

Cikin kulawa tace ko zakayi wankane kadan sami qarfin jikinka

Kwantarda kansa yayi akan laps nata yace as u wish baby amma banjin qarfin jikinane yanzun

Ayyah sorry kasan jiki da jini barin hada maka ruwan wankan ko

Amma banson warm water baby

Tace i know but tinda da fever ajikinka kada yakuma dawomaka dashi

Cikin shagwaba kamar qaramin yaro yace pls baby Allah banson ruwan zafi

Tace is ok shikenan barinzo nan tazame kansa ahankali ta daura akan pillow ta fice toilet

Yaune shigarta na farko toilet dinsa nan takuma tabbatar lalle ya Alamin mutum ne mai tsabtar gaske komai tsaf saikace baa amfani dashi

Bathtub ta cika masa da ruwa tasaka masa turaren wankansa sannan ta fito da towel ahannunta

Tsayawa tayi akusa dashi tace ya Alamin shiru bai amsaba sake kiransa tayi akaro nabiyu

Uum yafada yana bude lumsassun idanunsa

Jikinne ta tambayesa
No kawai banjin karfin jikinane yafada

Let me help u tafada tana miqo masa hannunta kan ya riqe

Aiko bai bata lokaciba ya riqe tattausan hannunta ya tashi ahankaki tana riqe da towel din tarakasa har toilet

Miqa masa towel din tayi sannan ta fice cikin sauri

Murmushi yayi ganin haqansa ya kusa cimma ruwa ya kuma gaskata maganar Aunty Naja dan tabbas yanda tanuna damuwarta qarara akansa hakan ya nuna tana sonsane

Baiwani jimaba ya fito daure da towel a waist nasa
Sunkuyar da kanta tayi tana wasa da yatsun hannunta

Basarwa yayi kamar baisana da itaba ya wuce yadan shafa cream kadan ya fesa spray ajikinsa

Wasu kayan shan iska ya saka kafin ya dawo kusa da ita ya kwanta gamida lumshe idanunsa

Ya Alamin muje kadanci wani abin mana kada ka kwanta da yunwa

No bani shaawan komai baby just black tea nake buqata

Marairaice murya tayi tace aa pls don't say that mana kobayawa kadanci inyaso saina hada maka black tea n inbakason fitane nakawo maka nan inyaso

Dan yamutsa fiska yayi yace shikenan muje toh amma saidai kidan riqemun hannuna cos am feeling dizzy

Allah barin kawo maka nan idan bazaka iya zuwaba

Aa muje kawai yafada yana yunqurin tashi zaune

Tana riqe da hannunsa suka fito har dinning room

Nan tayi serving nasa kafin itama tadan zuba kadan dan batajin cin abincin itama

Kawai dan yadancine yasa itama tadan zuba

Bayan sun kammala wadda dukkanninsu kowa yadan chakulane ya bari

Bayan yasha tea din tace zaka koma dakine

Aa muje falo dai nadan kwanta acan

Ok tafada kafin suka koma falo shiya kwanta itakuma tana zaune agefensa sai faman sannu take masa

Can taji yayi shiru irin bacci yadan daukesa while idanunsa biyu likimo kawai yayi

Xubama kyakykyawar fiskansa idanu tayi tana jin wani sabon sonsa da tausayinsa suna ratsata

Sunjima ahaka hartafara jin bacci shikuma dagangan yaqi ya tashi yafison tagaji danknta

Ganin bacci na neman kwasheta awajen yasa tasa hannunta tadan bubbuga hannunsa

Ya Alamin katshi ka koma daki kada jikinka yayi ciwo

Bude idanunsa yayi ahankali cikin murya kamar mai bacci yace umum kibarni kawai anan zankwana

Anan kuma?ta tambayesa

Umm anan zan kwanta bani shaawan kwana a room nawa har garamun nan

Shiru tadanyi harga Allah ita bacci takeji kuma bazata iya tafiya tabarsa afalo shikadai ba ga ba lfy ce dashi ba

Cikin sigan lallami tace haba ya Alamin taya zaka kwana anan baicin dik yawan dakunan gidan nan

Idan can baimakaba saika canza wani dakin bawai ka kwanta anan ba

Sai dai muje room naki ya fada kansa tsaye

Shiru danyi tana nazarin maganarsa

No kada kisama kanki tunani kije ki kwanta abinki sai da safe yana fadin haka ya juya mata baya

Shiru ta danyi nadan lokaci kafin murya asanyaye tace katashi to muje

Aa barin takureki bafa kije kawai abinki

Umum baka takurenba muje ka kwanta acan din badamuwa

Yunqurawa yayi ya miqe zaune tare da miqo mata hannunsa

Riqesa tayi ya miqe ta kashe komai suka wuce

Har bakin gado takaisa saida ya kwanta sannan ta juya nan ta tsinkayi muryarsa yana cewa inazaki

Batare da tajuyo ba tace zancanza kaya nane ta wuce ta dauki kayan baccinta ta shige toilet

Acan ta canza kayanta sannan ta fito blanket ta dauka ta nufi kan sofa ta kwanta

Dik abinda take yana kallonta

Mene haka kuma zakije can kikwanta

Eh kai ka kwanta akan bed ni nanma ya isheni tafada tana lulluban jikinta

Tashi zaune yayi yace aa kam keda dakinki barinzo intakurekiba, kidawo nan sai ni na koma falo inyaso inkuma ba hakaba kizo kikwanta abinki, inbakuma guduna kikeba

Tace ya Alamin na roqeka ka kwanta abinka ni hakanm yamun

Ganin ya miqe dagaske zaifita yasa tace shikenan zandawo ka kwanta toh

Tasowa tayi tawuce can qarshen gado ta kwanta sannan shima yazo ya kwanta abaki baki

Amma yana tunanin hanyar da zaibi ya jawota jikinsa

Itakuma tana kwanciya bada jimawaba bacci ya dauketa

Kamar amafarki taji nishin mutum kuma bana lfy ba cikin firgita ta tashi zaune ta waiwaya ind yake kwance

Nan taganshi qudundune acikin blanket sai rawan sanyi yake yana nishi samasama

Batasan sanda ta isa gabansaba tana kiran sunansa ya Alamin jikinne ganin ya gagara amsa mata kawai saita fashe da kuka tana cewa saida nace inkira momcy ka hana yanzun gashi dare yafara yazanyi

Murya ashaqe yace sanyi nakeji pls kitaimakamun sanyi

Tace inqara maka bargonne, murya narawa yace koma mene kimun kitaremun sanyin nan

Qara masa bargon tayi amma still baidaina shaking ba

Hankalinta inyayi dubu ya tashi sai hawaye datakeyi wani nabin wani

Cikin kuka tace katashi mutafo asibiti kaji

Girgiza mata kai yayi yace yace aa sanyi kawai nakeji banjin zazzabin

Tace ai shine alamun zazzabin nanan kenan nidai mutafi asbiti adubaka


Yace aa abu daya zakimun nasamu sauqin sanyinnan shine dumin jikinki pls ki kwanta ajikina

Ba musu ta yaye bargon zata kwanta yace saikin cire rigarki sannan nasamu dumin jikinki

Tsabar yadda take adame ganin halin dayake ciki batai musuba ta cire doguwar rigar baccin dake jikinta ta kwanta ajikinsa

Lumshe idanu yayi yana jin sauqan niima har cikin bargonsa
Gyara kwanciyarsa yayi ya matseta sosai akan qirjinsa lokaci guda yaji wani kasala ya dirar masa har idanunsa na rufuwa

Itama wani yanayi ta tsinci kanta aciki amma ganin yadda yake cikin halin rashin lfy saita haqura ta kwanta sosai

Ahankali hankali yadaina rawan sanyin ya kuma daidaita natsuwarsa dan bacci sosai yafaraji

Itama bada jimawaba baccin yasake dauketa

Ranan shima kwanan farin ciki yayi koba komai yanzun yana ganin nesa tazo kusa

Sassanyar iskan sanyin asubane daya karade sararin samaniya wanda ya sanadin sanyaya duniyar baki daya shiya qara sanyaya dakin daya hadu da sanyin AC

Hakan yasa taji sanyi yamata yawa har yayi sanadiyar farkawarta

Sannu ahankali ta bude idanunta nan taganta kwance tayi daidai ajikin papa

Yinquri tayi cikin sauri zata matsa sai taga ya motsa aifa nan tasake lafewa ajikinsa dan batason yafarka yagan ta awannan yanayin

Daga ita sai dan guntun wando ajikinta.....



โœ๐ŸปFaty Mmn Faty





๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Fat Mmn Faty

September, 2017



6โƒฃ5โƒฃ
Batasan cewar ya rigata farkawaba kawai baison jikinsu ya rabune yasa yayi kamar bacci yake

Cikin dabara ahankali ta zame jikinta daga nasa ta jawo rigarta ta saka

Lallabawa tayi ta sauqa ta nufi toilet Alawala tayi tadawo tafara sallolinta kamar yadda tasaba

Shikuma tun data tashi yaqura mata idanu yana kallonta harta shige toilet

Lumshe idanunsa yayi yana yaba surar da Allah yai mata, wani murmushi yasaki daya tuno yanayin qirjinta

Ganin har zai makara sallan asuba yasa shima ya miqe Ahankali ya fice dakinsa

Wanka yayi sannan ya daura alawala ya fito yayi sallansa adaki

Sai wajen 6 sannan ya dawo room nata lokacin ta idar da adduointa tana ninke sallayan

Bakin bed ya qarasa ya zauna saidata maida komai wajen zamansa sannan ta dawo ta zauna aqasa jikin qafafunsa

Murya Ahankali tace ina kwana ya Alamin

Da murmushi afiskansa yace lfy lau babyna

Ya jiki?tafada ahankali

Dasauqi sosai baby dafatan kintashi lfy daiko

Tace lfy Allah ya sauwaqa

Amin yafada yana kallon yadda ta sunkui da kanta irin batason su hada idanun nan

Baby ya kira sunanta da wani salo

Har cikin zuciyarta taji sautin muryarsa,naam ta amsa asansaye

Taso kiji wata magana

Babu musu ta dawo gefensa ta zauna

Zamewa yayi ya kwanta akan laps nata cikin sanyin murya yace baby nagode nagode da kulawar da kika bani Allah yabani ikon kyautata maki nima

Murmushi tayi dan taji dadin kalamansa tace bakomai ai haqqinane na kula da kai lokacin dakake buqatar hakan

Yace toh nagode

Dame zakayi break nadafa maka ta tambayesa

Shiru ya danyi yace nibanjin shaawan komai dan nayi loosing apatatide

Da muryar lallami tana dan shafa kansa tace haba dai daurewa zakayi badan dadiba kadanci wani abin
Aidai bai yiyuwa kazauna da yunwa daiko

Dan yatsina fiska yayi yace shikenan naji

Tace to mezakaci

Anything ya amsa yana lumshe idanunsa dan yanajin dadin yadda take sosa masa kansa


Shikenan barinje nadanyi aiki, aa baby kibari bayanzuba mana

Tace toh shikenan naji

Dahaka har bacci ya daukesa sannan tazameshi ahankali tafice danyin ayyukanta

Sai 10 taqare komai tadawo dan tayi wanka nan ta tarar baya dakinta

Wanka tayi fess tafito ta shirya cikin atampa dinkin doguwar riga wanda tamata matuqar kyau

Dinkin yazauna sosai ajikinta kamar kasaceta ka gudu haka tayi kyau

Fitowa tayi sai qamshin humra ke tashi ajikinta ta nufi dakin papa kan yafito ya karya

Tasaka hannu zata bude qofar falon shikuma ya rigada ya bude aiko saita afko ciki dan tabada qarfinta wajen jingina ajikin qofar

Nan tafada kan faffadan qirjinsa tana sauqe numfashi dan ta tsorata, zatonta aqasa data fadi

Shikuma tana sauqa kan qirjinsa ya shaqi wani niimtaccen kamshinda ya haifarmasa da kasala lokaci guda

Hannunsa ya daura akan bayanta yace am so sorry baby bansan kina wajenba

Kanta ta kwantar sosai ajikinsa kafin tace bakomai nasan bakasaniba ai ammafa na tsorata

Eyyer am sorry my dear kada kitsorata am here kinji

Kanta ta gyada kawai sabida yadda yake wani shafan kunnenta da hannunsa harya gangaro zuwa wuyanta

Cikin wata iriyar murya saitin kunnenta yace baby sarqannan tamiki kyau sosaifa yana shafan jikin wuyanta

Wani yarr taji harcikin jikinta yadda yake maganar yana wani shafanta kasa jurewa tayi cikin qarfin hali tace ur breakfast is ready

Ok thanks a lot mujeko yasake maqaleta ajikinsa

Ahaka suka sauqo sai wani shafata yake yana sunsunan jikinta kaman wani sabon maye itakuma dik jikinta yasake tawani lafe ajikinsa

Kujera ta jawo masa ya zauna sannan itama ta zauna agefensa

Faten irish potatoe tamasa mai dan ruwaruwa yasha alayyahu da hanta irin namarasa lfyn nan

Zuba masa tayi tace bismillah maqe kafada yayi yace umum

Tace why tana kallonsa

Yace saidai muci tare

Murmushi tayi tace toh muci, tare sukaci yana cewa ya qoshi tana lallaminsa ya daure yaci

Batasan cewar dadin abincin yakeji sosaiba kawai yana pretending ne irin patient dinnan lol

Bayan sungama ta tattara wajen suka

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login