Showing 33001 words to 36000 words out of 87071 words

Chapter 12 - Budurwar Kauye Hausa Novel

07 Oct 2024

13114

kaya acikin sannan ta duba kitchen din falonta,wayam ba komai,sakowa downstairs tayi ta shiga kitchen da store ,rai bace ta fito suka nufi asibiti

Office din daddy ta shiga nan ta labarta masa komai cikin takaici tace Alamin yaci amanar yarinyannan ,bakomai banda shinkafa da mai da maggi kuma INA zaton tun garan bikinsu nema


Daddy yayi shiru yace balaifi ya kyauta muje wajenta kada ta farka ba kowa

Dakinda aka kaita suka shiga,basufi minti goma ba tafarka ,tana bude idanunta sai kuma ta fashe da kuka


Momcy tamatso kusa da ita tana shafa kanta,cikin lallashi tace kiyi shiru daughter gani nan kusa dake ba abinda zai sameki

Asabe mai aikin momcy ce tashigo,da basket na abinci da flask ahannunta, ajiyewa tayi tana tambayar ya mai jikin

Momcy tace dasauqi ,kikoma gida saimun dawo kawai inaga nan zamu kwana

Tace toh Allah ya sauwaqa sannan ta tafi

Tea mai kauri momcy ta hada sannan tace daughter muje kiyi brush kiyi wanka saiki sha ko

Ba musu ta tashi,saida ta kaita har toilet sannan ta a fito ta barta

Tana fitowa ta bata kaya taje tacanza, bayan tacanza kayan tafito zama tayi a bakin gado tayi shiru

Daddy ya ce ya jikin,ahankali tace dasauqi

Miqo mata tea momcy tayi amma maimako takarba sai tafashe da kuka


Rarrashin duniya sunyi amma taqiyin shiru, cikin lallami daddy yace mekikeso daugther nah fadamun amma kibar kuka kinji

Cikin kuka tace nikam wajen Abba da Mama zanje

Daddy yace toh kiyi shiru zan kira maki Abba awaya amma fa sai kinyi shiru kuma kinsha tea kinci abinci kin yarda

Cikin sauri tace na yadda

Daddy yashafa kanta yace good girl

Momcy ta matso tafara bata tea aiko nan da nan tashanye tass dan yamata dad'i, rabon data sha mai dad'i haka ai harta manta

Plate momcy ta dauka ta zuba mata fried rice wadda tasha kayan lambu da papper chicken

Nan tahauci hannu baka hannu kwarya,daddy juyawa kawai yayi dan takaici ace kamar fauziyyah dan tasamu abinci takeci kamar almajira

Momcy ma haka shiru kawai tayi amma baqin ciki ne fal ranta

Tass tacinye ta kora juice mai sanyi, haba sai wani natsuwa yaxo mata,har wani lumshe idanu tayi tanajin wani natsuwa ajikinta


Daddy ne ya kira Abba awaya bayan sungaisa yace masa ga fauziyya zasuyi magana, Abba yace lfy dai ko

Daddy yace lfy ba lfy ba itance bata da lfy amma dasauqima shine take rigima wai sai dai akawota gida shine nakira taji muryarka ko hankalinta zai kwanta

Ok toh bani ita, tana karban wayar tace ina yini Abba

Lfy lau mama na ya jikin dai,

Tace dasauqi,yace to kuma sai rigima kice sai kinzo gida


Cikin shagwaba tace ai inason ganinku ne

Abba yace toh ai basai kinzoba gobe insha Allahu zamuzo mudubaki

Cikin jin dadi tace dagaske Abba

Yace insha Allah ga mama kugaisa

Nanma cikin murna suka gaisa da mama , mama tace harda khairy zamuxo dan tazomun hutu

Cikin doki tace Allah ya kawoku lfy

Mama tace amin sannan sukayi sallama

Daddy yayi murmushi yace rigima ta qare ko

Sunkuyar da kanta tayi sai taji kunya kuma

Daddy yace momcy inaga muwuce gida kawai tunda tasami sauqi

Momcy tace to bakomai nan tafara hada kayayyakin su

Daddy ne ya dubi fauziyyah cikin kulawa yace daugther na zaki bimu ko zaki koma gida

Dasauri tace aa zanbiku

Nan yadada tabbstarwa lalle abunda papa yayiwa yarinyan nan bakadanba ne tunda har take gudun gidansa


Driver ya kira yazo ya saka musu kayansu a mota sannan suka wuce gida


Ranan fauziyyah tayi kwanan natsuwa dan kafinta ta kwanta sai da momcy tasa aka dafa mata farfesun zabuwa wadda yaji kayan qamshi nn taci tayi nak dama fauziyyah badai son dadi ba๐Ÿ˜œ


Momcy ce ta shigo dakin daddy cikin shirin bacci nan tasameshi yayi shiru

Zama tayi agefensa ta dafashi tace daddy lfy kuwa kayi shiru tunanin me kake

Saida ya sauqe numfashi sannan yace tunanin wanne irin hukunci zanma Alamin nake tunda baida mutunci har yana neman kashe yar mutane saboda son zuciya

Momcy tace nima tunanin danake kenan amma kabarni dashi fauziyyah kuma baxata koma ba harsai ya gane kurensa

Daddy yace hakan zaayi amma ahankali kitambayeta medame ya ke mata

Momcy tace badamuwa bari ta warware


Washegari su Abba sukaxo murna awajen fauziyya ba magana

Tare sukazo da khairy

Nan suka shiga dakinta inda momcy da su mama suna falon daddy


*****
Papa kuwa ganin sunqi sauraronsa gashi baifito da wayaba da yakira TJ yazo ya maidashi gida

Drivern daddy yasa ya maidashi gida

Washegari bayan yayi wanka yafara tunanin yaje ne ko kar yaje


Sai yace gara yaje kada yasake laifi amma bari ya kira TJ yazo suje

TJ ya kira awaya yace yaxo rakashi wani wajemana

Tj yace badamuwa in d next 30mins yana zuwa

Bada jimawaba sai gashi agidan papa yayi parking motarsa suka shigata ta papa suka fice

Suna tafe ahanya amma papa hankalinsa yana can tunanin ko momcy data saurareshi


Tj ne ya katse masa tunani yana cewa man kadakkoni rakiya bakafadamun inda zamujeba sannan kayi shiru baka ko magana lfy kam

Baibashi amsa ba saima yaga sun dau hanyar asibitin daddy


TJ yace man kamun bayani mana kuma gashi mundau hanyar asibiti


Papa yace kaidai bari wlh waccar yarinyan ce batada lfy kawai shikenan su momcy suka fara fushi dani suna nuna kamar nina saka mata rashin lfyr

TJ yace wai wace badai fauziyyah ba


Papa yace ita mana ni wlh yarinyannan tazamamun liability


TJ yace i know u very well friend anya kuwa ba wani abu kamata ba

Cikin fushi yace toh mezan mata nikuma

Tj yace Allah yasa dagaskene kake kuma indai da hannunka nima ba ruwana

Daidai da shigowarsu cikin asibiti nan ya hango wata nurse kiranta yayi ya tambayeta tace ai tunjiya suka tafi gida


Shiru yayi TJ yace ai saimuje gidan to

Nan suka wuce gida, Falon daddy suka fara shiga nan suka samu su Abba

Cikin girmamawa papa yagaida Abba da mama

Sannan ya gaida daddy da momcy haka dai suka amsa ba yabo ba fallasa sabida gabansu Abba nema yasa suka amsa

Wucewa cikin gida sukayi ganin ba kowa a falo yasa suka nufi dakin da yasan zai samu fauziyyah......



โœ๐ŸปFaty Mmn Faty
[3:53PM, 8/19/2017] โ€ช+234 803 341 6395โ€ฌ: ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017


3โƒฃ4โƒฃ
Bako sallama haka ya hankada qofar dakin ya shige ciki

TJ ne dake bayansa yayi sallama

Khairy dake zaune afalo tana danna wayarta tadago tana amsa sallamar

TJ ko yana ganin khairy yagane ta da faraa yace manyan bakine haka

Itama da faraarta tace sannu da zuwa dan taganesa

Amutunce ta gaidasu, TJ yace ya maijiki

Dasauqi ta amsa ,yace Allah ya qara sauqi tace amin

Ina fauziyyah Tj ya tambaya

Tace tana bacci amma barin tasota

Cikin sauri papa yace aa kibarta kawai sai anan yayi magana tun shigowarsa

Samun waje TJ yayi ya zauna dan shifa ya kyasa baran yau saiyaga taqara masa girma da kyau

Amma kuma bansan sunan malamarba yafada yana kallon khairy

Murmushi tayi cikin kunya tace khairy

Yace waw nice name khairy ya maimaita

Papa da haushi ya kasheshi yace oya man muje idan ta tashi madawo yafadi hakan dan sutafi

TJ yace ok muje amma malama khairy kozan sami no wayarki dan muringa gaisawa

Shiru tadanyi , qasa da murya yayi yace ko zaamun rowa ne

Tace aa sannan ta bashi

Godia nake sosai yafada sannan ya fice lokacin papa har yakai qofa


Suna fita papa yace kaidai Allah ya shiryaka mai zakayi da no wayar wannan yarinyar


TJ yace abinda kake da taka yarinyar dan ubanka

Papa yace lalle nayarda kanka aduhu yake kuma bakasan me duniya take cikiba

TJ cikin rashin fahimta yace toh wayar mun dakai mana

Baikuma cewa komaiba sai da suka shiga mota ya dago tab dinsa yace kallo nan

Karba yayi adakile yace wannan mai idon yan chines dinfa?wace ce ita harda samun matsayin hawa wallpaper

Papa yace buu, dan iska marar mutunci aifa nasan kai dan adawane shiyasa ban shafa maka ba amma tunda kafito fili da rashin mutuncinka to matar da zan aura ce kuma kada ka gwada gigin aibatata

TJ da ya daskare yanajin papa yace man me kake fada aure akan wani dalili

Yes aure ko haram ne ko kamanta ni mijin mace hudu ne

TJ yace nasani but inasonjin dalilinka na neman aure

Cikin rashin damuwa yace sabida nasamu test dita kuma ta dace da kalar matar da nakeso

Jinjina kai yayi yace ah lalle Alamin yakamata ka farka idan bacci kake

Amma mezakayi da wannan yarinyar wlh gara ka natsu ka rungumi matarka yafimaka,ni har ina maka murna nadauka komai ya wuce kundaidaita kanku sai ka tsiro da wani zance kuma haba

Papa yace to ubana barin qarqare maka sabida banason dogon magana

Kasan Allah wannan auren babu fashi idan bazakasa albarka ba just chup(kawai kayi shiru)

TJ yafahimci wanda yayi nisa baijin kira sai yace hakane toh Allah ya sanya albarka yasa ayi damu

Papa yace ahaa yanzun naji magana tunda kabi hanya next week tare zamuje

TJ yace a ina take da zama?

Yace sunanta Juhaina kuma a kd take da zama

Nan suka wuce gidasu TJ suna tattunawa ahanya


Cikin sati biyu TJ yagama shigarda kansa awajen khairy kuma yasamu karbuwa awajenta

Dan yafada mata bada wasa yakeba zai turo iyayensa

Amma taqi amincewa sabida karatunta

Yace indai maganar karatune ya amince taci gaba agidansa

Cikin qanqane lokaci ya samu soyayyar ta dan TJ badai iya zanceba kuma yagaji da gararamba da mata sabida haka yaga gara ya rufawama kansa asiri yayi aure gashi agidama sun dameshi har mmansa tana cewa zata samo masa mata inhar bazai natsu ya fidda mata ba

Hakan yasa dayaga khairy ta masa baxaiyi wasa ba gara kawai ya lallaba ya aureta


*****
Wasawa watan fauziyyah 1 agidan momcy harta maida kibanta ta murmure sabida kula na musamman datake samu daga wajen momcy da daddy

Kuma har yau ba labarin komarta gidan papa,sabida haryanzu papa bai samun fuska awajensu daddy danko gaisuwarsa basa amsawa

Idanma zuwa gidan yayi haka zai qaraci zamansa ya tafi bamai cemasa cikanka

Tin abin baidamunsa har yafara daminsa,ga gidan yamasa shiru idan yadawo office sai dai ya wuce wani wajen dan ya debe masa kewa

Yauma kamar kullum ya taso office gida ya dawo amma sam sai yaji bai shaawar zama acikin gidan danko bakomai wannanar villager tana debe masa kewa ko masifan da walaqancin daya ke mata ma amma yau ba wanda zaima

Cikin sauri yayi wanka ya shirya ya nufi gidan momcy dan ya basu haquri cos ya gaji da shareshi da suke akan abinda baima san dalili ba

Cikin saa kuwa yasamesu dik afalon momcy suna ta hira harda fauziyyah

Tana ganinsa ta miqe zata bar wajen ,daddy yace da ita ina zuwa daugther na

Tace zan shiga dakine

Daddy yace aa muna hiranmu ba inda zakije dawo kiyi xamanki

Cikin sanyin jiki ta dawo ta zauna

Shima qarasowa yayi ya zauna kusa da momcy yace ina yini momcy

Yitayi kamar batajisaba,ganin bazata amsa ba yasa ya juya wajen daddy shima haka bai amsaba

Nanfa yaji zuciyarsa tana masa zafi

Cikin damuwa yace wai mena makune kukemun irin wannan punishment din, baku kulani baku amsa koda gaisuwata akan abinda bansan dalili ba

Momcyne ta harziqo tace au bakamasan mekayiba lalle dasauranka toh kaje rananda kasan laifinka sai ka dawo

Cikin fushi daddy yace lalle Alamin dasauranka yanzu dik abinda ka aikta bkasani ba wlh ka kiyayi duniya kabita ahankali


Ka cuci yarinya ka zalunceta dik kace bakasan laifinka ba toh kashiga taitayinka kuma wlh kaguji sakayyah ranan da zata....


Kuyi manage da wannan


โœ๐ŸปFaty Mmn faty๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017



3โƒฃ5โƒฃ
Kamaka dan wlh dik wadda ya dau hakkin wani Allah bazai barshiba

Amma kai ko ajikinka sabida bakasan wannan ba

Momcy tace kuma duk abinda ka aikata kaje kanka kayiwa bamuba tunda ka nuna bamu isa dakai ba

Cikin tsukewar fuska yace wane irin baku isa dani ba kuma ,dan ransa ya soma baci agaban yarinya qarama zasu ajiyeshi suna masa shouting abanza

Daddy yace to inba ka nuna mana cewar bamu isa dakai ba taya zaka ajiye matarka cikin yunwa wanda abanza da wofi na shaye2nka kake kashe kudi fiye da misali

Au cewa tayi ina barinta da yunwa yayi maganar fiskarsa a murtuqe alamun bacin rai

Momcy tace qaniyanka nace qaniyanka dake bamu muka gani da idanunba ko wlh papa ka kiyayeni zanci mutuncinka akan maganar nan dama na zuba maka idanu ne inga gudun ruwanka

Cikin fushi shima yace dama akan wannan munafukan yarinyan tafada maku qarya d gaskiya yasa ko gaisuwata baku amsawa, dama nasan kunfi sonta akan ni shiyasa akan ta akemun abunda aka dama

Bayan antauyemun haqqina an hadani da ita na haqura ina zaune da ita hakan baiyiba sai kuma anxo anacewa nayi laifi

Daddy ne ya taso akansa yace kai har ka isa ka ajiyemu kana fadan magana san ranka

Sabida ka kafi karfin kayi laifi ka amsa laifinka ko toh kayi kadan to

ta inda yake shiga ba tanan yake fita nan ya wankeshi tass

Ganin dagaske ran daddy ya baci yasa ya sassauta murya sa

Yace toh yanzu me kukeso nayi muku

Momcy tace ka amsa laifinka kuma ka gyara gaba dan bazamu lamunci tozarciba, yanzu idan iyayen yarinyannan sukaji wani irin kallo zasu mana

Danma Fauziyyah yar albarka ce bata taba fada masu halinda take cikiba

Sake qasa da murya yayi yace toh naji nayi laifi kuma bazan sakeba kuyi haquri Allah ya huci zuciyarku

Daddy yace nadai fadamaka da gigin wasa kada ka kuma mafarkin maimaita abinda kayi

Yana fadin haka ya miqe ya wuce side nasa rai bace

Fauziyyah kuwa tunda suka fara magana take kuka

Momcy tace kiyi shiru daugther share hawayenki bamai cimaki mutunci mu kyalesa tashi kije kiyi alwala ankusa kiran sallah

Tana tashi momcy ta dubi papa tace son wannan yazama na qarshe kada ka kuma gangancin yin abinda ka aikata kaji nafada maka tunda aure ba hauka bane

Naji shine binda ya fada ya miqe yace nawuce gida

Allah ya kiyaye tace dashi kamun itama ta wuce dakinta ta kuma qudira azuciyarta fauziyyah bazata komaba har sai ranan da yazo da kansa yace ta koma


*1month later*
Papa nazaune a office yana duba xray da akayima wata yarinya a cinyanyanta,watanni uku kenan da yin accident dinta ta karye amma kashin yaqi hadewa shine aka turota wajen Dr Alamin


Wayarsa ce ta fara rurin neman agaji

Tsaki yayi kamar bazai dagaba dan yana aiki amma sai ya daure ya jawo wayar

Ganin sunan mai kiran yasa ya ajiye file din hannunsa ya picking call din

Hello yane toh shine abinda yafada

Daga dayan bangaren akace normal fa ya aiki

Yace aiki ba dadi wlh namagaji ga wani case da aka turomun mtss yaja wani guntun tsaki

TJ yace eyyer sowwie shaanin aikine niyau tun 1 na gudu cos bama da wani aiki shiyasa


Yanzun muka gama magana d popsy nace bara nafara maka albishir kafin muhadu

Cikin kulawa yace inajinka mutumin

Saida yayi wata dariya sannan yace next week fa su popsy zasujemun dambam tambayan aure

Papa yace waw what a great news nayi murna sosai abokina dole nazo gida idan nataso office amma kuma natausaya maka zubewar girmanka

TJ yace toh nagode sai dai kafin nawa ya zube nakane yafara zubewa tunda kaika fara

Papa yace hhh dakenan aini yanzu free nake tunda nasamu su momcy suka riqeta awajensu tunda tayi rashin lfy ni yanzu ai banada matsala

TJ yace kai wlh mutumina bakada kyau dama ashe bata dawo ba tun wancan lokacin toh wlh gara kaje kayi qaramar murya abaka matarka yafi maka

Papa yace wucenan wlh tayi ta zamanta acan har qarshen rayuwarta danni this week ms kd zanje nafada ma queen zanturo dan aure nake buqataryi nan da 3months masu zuwa kafin wannan stomach pain din yamun illah

TJ ya sheqe da dariya yace kaidai kajama kanka tunda da matarka kake daurama kanka ciwo

Kai haba god forbid nahada jiki da wannan villager kuma mai zansamu kawai saina shigo bayan magrib

TJ yace Allahu yahdika abonkina sai kashigo din

Nan sukayi sallama inda TJ yake jiyema abokinsa kokarin barin damarsa dayake shirin aikatawa

Ranan saturday papa ya shirya ya tafi kd wajen sarauniyarsa

Kamar kullum haka suka sha hirar soyayyarsu nan yake fada mata zai turo iyayensa so ya tagani

Murna wajen juhaina baa magana amma sai ta boye tace bakomai ta amince

Yace toh idan ya koma dik yanda yayi dasu daddy zai sanar mata sai tafadama dad dinta ya basu ranan zuwa


Washegari ya dawo bayan ya huta yamma lis yayi wankansa ya chaka ado cikin blue jins da red shirt sun masa kyau sosai

Qafarsa sanye da red bufalinos

Motarsa camry LE ya shiga kalar navy blue ya nufi gida


Falon daddy ya wuce nan ya samu momcy sunashan fruit ita da daddy suna hiransu abin shaawa

Zama yayi ya gaidasu sannan yasa hannu ya dauki grabes guda daya yasa abakinsa

Shiru yayi sai yayi kamar zaiyi magana saiya fasa

Momcy tana lura dashi sai tayi wani murmushi atunaninta yanason tambayar abashi fauziyyah ne kuma yakasa fada


Daddy ma ashe yana lura dashi dubansa yayi da kyau sannan yace yadai babana bakin kannan kamar akwai magana amma kayi shiru

Dan murmushi yayi yace umm daddy wajenka nazo


Daddy yace toh lfy dai ko

Sai da ya dan sosa kansa yace umm lfy lau daddy dama sai kuma yayi shiru

Uhum go on inajinka daddy yace dashi

Dama daddy akwai yarinyar da muka daidaita da ita ne shine nakeson ajemun tambayar aurenta

Cikin sauri momcy ta dubeshi dan maganar yazo mata abazata kuma bata taba tunaniba

Daddy ma haka yaji maganar watairi shiru yayi kawai yana kallonsa cos he is totatly speechless dan yarasa ma mai zaice masa nan take yaji wani irin baqin ciki ya lullubeshi

Dubansa kawai yake cikin takaichi kafin.....


โœ๐ŸปFaty Mmn Faty
[6:13AM, 8/19/2017] โ€ช+234 705 319 5189โ€ฌ: ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017


3โƒฃ6โƒฃ
Cikin takaici yace Alamin kana cikin hankalinka kuwa?

Kodai kwakwalwar ka ta tab'u ne?

Momcy tace wanne irin ya tab'u da hankalinsa sarai sai cin mutunci dayakeso ya mana

Daddy yace ok, toh kabud'e kunnenka da kyau kajini idan har nina haifeka ban aminceba ban kuma yarda ba da wannan magana

Idan kuma kaqi toh saidai kanemi wasu iyayen su shige maka gaba kuma bani ba kai that's all

Nan da nan fiskansa ta canza damuwa qarara ya bayyana bude baki yayi zaiyi magana cikin sauri daddy yace i don't want to hear anything from u kawai katashi katafi tunda ba arziqine ya kawoka ba sha3 wadda bai san meke masa ciwoba haryanzun

Rai bace ya mike ya fito motarsa ya fada ya nufi gida ranan kwana yayi cikin damuwa sabida haka ya kashe wayoyinsa baki 1 dan baisan mezaicema juhaina ba idan sukayi waya


*****
Papa yana fita momcy ta dubi daddy tace lalle papa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login