Showing 48001 words to 51000 words out of 87071 words
dai kaida zakayi 1 week me zai dameka kuma Dr sai yamma shida yadawo
Yace ai har tunani nke next idan zanzo wacce qarya zamu masa tunda munce nazo gyara carry over ne
Dariya tayi tace wannan mai sauqine tunda shi baho ne inba hakaba sai kace ba mutumin daya shiga ajin ABCD ba
Komai aka fada masa sai ya yadda
Shima dariya yayi yace nidai muje toh pls mana
Riqe hannunta yayi suka shige bedroom nata
Nan suka fara mashaarsu da suka saba
Tsabar sunyi nisa basa cikin hankalinsu ko jin shigowar mota basuyiba
Papa kuwa ko parking mai kyau baiyiba haka ya fito ya nufi cikin gida
Ahargitse ya shigo falo dakinsa ya nufa
Yazo daidai dakin juhaina harzai wuce sao yaji kamar nishi
Saurarawa yayi da kyau sai yaji tabbas ba kunnensabane nishintane
Cikin sauri ya bude dakin dan atunaninsa ko batada lfy ne
Yana shiga yayi turus wani jirine yaji ya debeshi yayi saurin riqe qofar sabida abinda idanunsa ya gane masa
Juhaina da munnir kwance haihuwar uwarsu suna aikata zinah
Abinda bai taba tunaninba juhaina zataci amanarsa kuma ma da dan uwanta
Su juhaina kuwa jin anbude qofa yasa cikin sauri suka juyo ganin papa atsaye yana musu wani kallo cike da baqin ciki har idanunsa sukoma jajaye kamar gaunta bushashshe
Dasauri munnir ya tashi akanta itakuma cikin razana ta tashi zaune tanajan mayafi tana kare jikinta
Ahankali yasamu nutsuwarsa ta dawo maida qofar yayi ya rufe da key sannan ya nufo su gadangadan
tsabar tsoro ba juhaina ba hatta munnir jikinsa rawa yake
Yana zuwa ya shaqo wuyan juhaina yace cikin kakkausan murya kifadamun wane ne munnir kuma meye atsakaninku
Aifa cikin tsoro da firgita tace dan Allah kayi....
Wani gigitaccen mari daya zabga mata saida taga wuta shiya katseta
Cikin tsawa yace wane ne munnir zaki fadamun da bakinki kosaina kasheki shegiya tsinanniyah macucuciya Allah ya isa tsakanina da keh wlh kinci amanata
Ganin yadda kamanninsa suka sauya fiskarsa tayi jajur tsabar bacin rai
Murya na rawa tafada masa tsakaninta da munnir tace amma kayafemun wlh bazan sake ba
Bata gama rufe bakintaba ya saka hannunsa ya makata da gini nan tafadi a asume
Munnir kuwa tsabar tsoro ganin yadda yayima juhaina saida ya saki fitsari ajikinsa
Aikuwa da papa ya damqoshi yafara dukansa yana cewa munafiki kana zaune agidana kana zaluntata ashe ina tare da kwarto bansaniba
Mari duka harbi haka yake masa saida kansa bakinsa hancinsa ko ina jini yake amma zuciya ta hana papa ya kyaleshi
Hannunsa yasa yakamo gabansa da iyah qsrfinsa ya jawota ya murde wadda saida ya saki kashin azaba
Hannunsa ya kama ya buga da jikin drower ji kake kass kass ya karyashi
Axaba iya azaba saida yakasa motsi sannan ya kyaleshi ya nufi toilet ya debo ruwa a bucket
Zuwa kan juhaina yayi wacce ke kwance asume ya sheqa mata
Nan ta firgita ta farka aiko itama nan yahau jibgarta da waya yana harbinta
Saida jikinta ya faffashe fiskarta ta kumbura tayi sumtum tsabar duka
Tsabar azaba har saida ta kasa kuka cikin baqin ciki ya jawota har waje tana nade acikin zanin gado amma saida kamanninta ya canza dan ba dukan wasa ya mata ba
Sannan yace tsinanniyah kada nafito nasameki kificemun agida na sakeki saki uku muna fuka
Itadai batada bakin kuka ma bare bashi haquri
Mai gadi ya kira yace suzo suna biye dashi har dakin juhaina yace su fitar masa da munnir agida su kaishi can waje
Haka suka jawoshi kamar har sun kai qofa paoa yace ganan haqorinsa biyu kuhada dashi kufitamun dasu
Suna fita ya nufi dakinsa yafada agado ya fashe da kuka....
โ๐ปFaty Mmn Faty
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐พ๐พ๐พ๐พ
๐พ๐พ๐พ
Budurwar Qauye๐คท๐ผโโ๐คท๐ผโโ๐คท๐ผโโ
Written by Faty Mmn Faty
August, 2017
*Gaisuwa mai tarin yawa musamman zuwaga Members na Mmn Faty Novel Group, Ina matuqar jin dadin yadda kuke bada gudumawarku da nuna jindadin ku akan littafin BUDURWAR QAUYE nagode sosai Allah ya bar qauna ๐๐*
4โฃ7โฃ
Kuka yake mai cike da nadama, hawaye wani nabin wani haka suke zuba akan face nasa
Zuciyarsa cunkushe da zallar dana sani akan abinda ya aikata abaya
Tabbas yau ya tabbar alhakin iyayensa ne dana fauziyyah ke bibiyarsa
Kuma ya qara daukan darasi akan bijirema iyaye ba abune mai kyauba tunda gashi yaga saka makon abinda bai taba tunani ba
Wani irin nauyi yaji qirjinsa yamasa
Kuka yake sosai har abin tausayi domin dik abinda mutun ya aika matuqar yagane kuskurensa har yayi nadama nagaske ba tuban baqin muzuru ba dole ya baka tausayi
Sambatu kawai yakeyi yana cewa daddy, momcy, fauziyyah kuyafemun ashe gata kukamun na auramun yarinya yar mutunci kuma mai mutunci
Amma son zuciya yasa na bijire muku yau gashi abinda yasameni wayyo kaicona kaicon halina dama duk masu hali irin nawa...
Maganarce tasarqe qirjinsa ya cushe numafashi yafara masa wahalar fita
Dakyar ya dauki wayarsa yafara kiran layin TJ
TJ yana office saiya ga kiran abokinsa
Hello man shine abinda ya fada yana daukar wayar
Cikin wata raunanniyar murya datake nuna mai ita yana cikin wani hali
Yace pls kazo gida kasameni ina cikin wani hali
TJ baisan sanda ya miqe tsayeba cikin razana jin yadda muryar abokinsa take a hargitse
Meyasameka??? Shine abinda ya maimaita harsau uku
Ahankali papa yace TJ banida lfy juhaina zata kasheni kazo pls kataimakeni
Afirgice TJ yace ganinan zuwa ganinan zuwa am on my way yana fadin haka ya suri key din motarsa ya fito cikin sauri yacema scretery nasa idan bandawoba zuwa 2 ka kulle office kawai
Baijira amsar shiba ya fice cikin sauri da tashin hankali dan baisan yadda zai sameshiba
Cikin gudun balai har ya iso gidan papa wani mahaukacin horn yake dannawa
Maigadima saida ya tsorata dajin irin horn dake masa
Aiko baibata lokaciba ya bude
TJ yana shigowa ko cikkakken parking baiyiba ya hnyar cikin gida daidai qofar falo yayi turus ya tsaya ganin juhaina lullube da zanin gado tana rizgar kuka dan sai alokacin tasamu kuka yaxo mata gashi ya kulle qofa bare ko kaya tasama jikinta baran tasannayi
Juhaina ina Alamin yake kekuma meya sameki naganki haka
Gagara magana tayi sai da hannu ta nuna masa qofar falo
Tura qofar yayi ya jita gam akulle bubbugawa yafara da iyaka qarfinsa dan abin yaqara bashi tsoro
Papa yanajin bugun qofa gakuma wayar TJ tashigo masa yasa ya taso ya fito falo ya bude qofar
Yanaganin TJ kawai saiya fada jikinsa yaqara saka kuka mai tsuma zuciya
Cikin rudani TJ yace waime ke faruwane man kamin bayani mana kozanji sauqin abinda nakeji
Sake qanqame TJ yayi yana cewa na cuci kaina na biyema san zuciyata na cutar da matata ta gaskiya na baqanta ran mahaifana yaugashi naga abinda bazan taba mantawaba
TJ ma kawai saiyafara hawaye nafarko tausayin papa dikda baisan meya faruba amma yadda yaganshi a hargitse yana kuka da idanunsa tabbas babban abune
Sannan murnan abokinsa ya gane gaskiya
Share hawayen fiskansa yayi yafara lallashin papa da kalamai masu dadi har papa yayi shiru
Sannan yafara bawa TJ labarin abinda ya faru yana furta abinda yagani sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo masa
Cikin tashin hankali TJ yakejin abin kamarca mafarki
Nan ya fara tausan papa da banbaki akan ya kwantar da hankalinsa komai zai wuce
Papa yace hankalina bazai kwantaba har sai ka kaini asibiti anmin test na HIV tukunna
TJ yace insha Allahu babu abinda zaisameka ka kwantar da hankalinka
Taya hankalina zai kwanta matuqar ina dauke da wani mugun ciwo wlh jujaina ta cuceni ta shiga tsakanina da fauziyyah dan bayadda fauziyyah zata dawo gareni ina halin jinya
Tj yace ya isa haka muje asibitin inhar hankalinka zai kwanta dan yaga har numfashinsa yana samasama
Amma kabar juhaina ta suturta jikinta kafin ta tafi
Da kyar ya yarda yace amma kada yadawo ya sameta
Nan suka fito TJ ya kalleta yace kitashi kije kisuturta jikinki amma yace kada yadawo yasameki gidansa yanafadin haka ya wuce abinsa dan dama papa ya riga da ya wuce
Sai bayan sunfito TJ yace wanne hospital zamujene
Ka kaini asibitin daddy shine kawai abinda ya iya fada
Suna isa asibiti lab suka wuce
Maaikatan wajen suna gaisheshi baiko amsaba yace subashi abin gwajin HIV kawai
Damamaki kowa ke kallonsa cikin tsawa ya maimaita masu nan take suka miqo masa
Alluraya dauka ya caka wa hannunsa nan take sai jini yazuba yafara zaman zullumi
Bada jimaba saka mako ya nuna negetalive
TJ dake tsaye agefe yace Alhamdulillah bana fada makaba gashi ai d answer is negetive dafatan hankalinka ya kwanta
Shiru kawai yayi ya miqe dan baijin zai iya magana
Tashin da zaiyi ya yanki jiki ya fadi sumamme
Cikin razana TJ ya sumkuya yana kiransa amma ina baimasan yana yiba
Cikin sauri aka kawo abin daukar marar lfy aka turashi sai emergency
Nan suka bashi taimakon gaggawa har Allah yasa numfashinsa ya daidaita sannan aka maidashi dakin hutu amma dai bai farka ba tukun
In hankalin TJ yayi dubu to atashe suke
Sai a lokacin ya tuna yadauki wayar papa dake aljihunsa ya fara kiran momcy
Bugu uku ta dauka tana cewa hello son
Cikin natsuwa TJ yace ba Alamin bane Tijjani ne
Momcy tace ayya ya khairy da mubeen (dansune wadda bai wuce shekara biyuba)
Lfy qalau umm dama Alamin dinne bashida lfy yanzu haka muna asibiti
Salati momcy ta fara tace mai yasamu papa kuna wanne asibiti
Asibitin daddy muke naje wajensama bayanan
Momcy tace eh yau bai fita ba amma muna zuwa yanzu
Daddy ne ya dubeta yana cewa wai meya sami Alamin din
Cikin damuwa momcy tace nima bansaniba kam
Toh dauko mayafinki muje
Suna zuwa suka shige inda aka kwantar dashi
TJ suka sami yayi shiru yana zaune
Bayan yamasu sannu da zuwa daddy yace wai meke faruwane kam
Nan TJ yafada masu abinda yafaru yace shine dai sanadin sumansa
Sannan TJ yace dan Allah daddy kuyafe masa wlh yayi nadama kuma yanzu damuwarsa qaruwa zatayi matuqar baku yafe masa ba
Daddy yace hakane Allah ya yafemu gaba daya ya kuma kiyaye na gaba
Dik suka amsa da amin
Suna nan zaune ahankali ya fara motsi
Kadankadan idanunsa suka washe yafara ganin komai tass
Aiko yana ganin su momcy sai yafara hawaye zaiyi magana
Daddy ya kamo hannunsa yace kada kace komai Alamin munyafe maka duniya da lahira saifatan wannan yazama darasi agareka
Momcy ta matso kusa dashi tana shafa kansa tace ya wuce papa ka kwantar da hankalinka sannan matakin daka dauka akanta yayi daidai Allah yasaka maka sukuma Allah ya shiryesu
Cikin jin dadi ya yunqura zaune yace nagode daddy na gode momcy nagode sosai
Momcy tace sai mutafi gida tunda yasami sauqi
Daddy yace muje amaidaka gida sai muwuce
Girgiza kansa yayi yace bazan iya zama acikin wannan gidanba ni gida zan koma
Momcy tace toh shikenan kutaho a motar tijjani inyaso sai kuje kadauko kayanka
Ahankali ya miqe TJ na riqe da hannunsa har mota
Momcyma gida suka wuce Sukuma suna zuwa gida basu tarar da juhaina ba
Nan TJ ya hada masa kayansa suka fito sai anan yayi magana yabawa maigai key yace idan tazo kwasan kayanta ya bude idan tagama ya kulle ya ajiye key din awajensa
Suna tafiya a mota ba mai magana acikinsu
Papa ya kwanta ajikin kujera ya tallafe fiskarsa da hannunsa yayi nisa cikin tunani
TJ yace haba man karage tunanin nan mana haka yanzu ai saidai ka godema Allah tunda kagane gaskiya sannan Allah ya toni asirin munafukai
Cikin damuwa yake kallon TJ yace man damuwata fauziyyah tafi qarfina ta wuce tinanina fauziyyah ta nuna batama sanniba yazanyi wlh idan ban auri fauziyyah ba mutuwa zanyi sabida ina sonta sonda bantaba jin inayima wata ya maceba aduniya ashe juhaina ma ba sonta nakeba fauziyyah nakeso na yaudari kaina nan idanunsa suka sake kadawa sukayi jajur
Cikin mamaki TJ yacecfauziyyah kuma a ina ka ganta
Nan yafada masa iya abinda yasani da haduwarsu
Tirqashi shine abinda TJ yafada dan yasan tabbas zaayi haka rananda papa ya komwa fauziyyah da sunan so
Papa cikin damuwa yace komai ya jagulemun man,kyiu wati hai bahaa??? Kyiu kyiu (mai yasa wannan canjin yanayin maiyasa maiyasa) ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka
TJ yace komai zaidaidaita kaci gaba da addu a kakuma kwantar da hankalinka
Maganar fauziyyah zamu zauna muga yadda zamu bullowa abin
Da haka har suka qaraso gida...
*****
Fauziyyah kuwa tana wucewa awajen tamanta da shafinsa dan sam baya gabanta sannan tunaninsa tsabar tsanan data masa batayi
Qarfe uku ta iso gida sai dai bakowa su momcy basa nan
Wanka tayi ta daura alwala
Sai datayi sallan laasar sannan tayi kwalliya ta shirya cikin wata doguwar riga yar kanti lokacin da zata dawo nigeria tasayeta
Coppee da milk tasha ado mai kyau
Bata saka dankwaliba sai gashinta data kama da milk ribbon ta fesa turare tafito
Tana zuwa falo taga momcy tadawo tace sannu da dawowa momcy
Momcy tace yawwa kindawo baki samemuba munje asibiti ne papa bayada lfy amma ansallamesa ma
Allah ya sauwaqa shine abinda ta furta albarkacin momcy
Momcy tace naga motarki shine na leqa dakinki kina wanka
Tace eh wlh sai danayi sallah tukun nafito
Momcy tace kinci abinci kuwa
Yanzu zanci ta amsa
Kai daugther bakyason cin abinci ko mai yasa toh kije kici
Toh ta amsa sannan ta wuce dinning taci abinci
Falo ta dawo ta zauna kenan su papa suka shigo
Aiko yana kyalla idonsa akan fauziyyah yaji wani sanyi aransa dan baqaramin kyau tamasa ba
TJ ma haka yake kallonta da mamaki ya kuma jinjina abin lalle akwai aiki agaban abokinsa dan yada ko kanta bata dagoba bare tasan da shigowarsu saima wayarta dataketa latsawa
Momcy tace sannu tijjani Allah yabar zumunci papa kushiga mana katsaya anan
Wajema yasamu yazauna yana cewa aa zansha iska kadan anan
Fauziyyah kuwa kamar ta bar wajen amma sai taga kada ya rainata kawai ta matse abinta
Acikinsu ba maimagana dan shi papa kallonta ma yasashi farin ciki sai yaji tsoro kada yamata magana tama bar wajen shiyasa yaja bakinsa ya tsuke
TJ kuwa shakkar mata magana yake kada shima tace bata ganeshiba
Wayarta ce tafara ringing dubawa tayi taja tsaki axuciyarta ganin no Brr.Nabil ne
Yau batasan iya adadin kiran daya mataba kuma bata dauka ba shikuma bai haqura ba
Harta katse bata daukaba sake kira yayi sai taji shaawar ta dauka kodan tasamu hanyar barin wajen
Momcy kuwa miqewa tayi tace barin turo muku da abinci
Fauziyyah cikin daddar muryarta tadau wayar da sallama jin muryarta mai sanyi yasa papa lumshe idanu.....
โ๐ปFaty Mmn Faty
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐พ๐พ๐พ๐พ
๐พ๐พ๐พ
Budurwar Qauye๐คท๐ผโโ๐คท๐ผโโ๐คท๐ผโโ
Written by Faty Mmn Faty
August, 2017
*Wai maiyasa mutane bakwa uzuri ma mutum ne? Idan kukaji shiru kunsan aidai da dalili kuma dai bazanyi typing ban turoshiba idan kuwa har hakane saikuyima mutum kyakykyawan zato masu cewa wai dan andamu nake masu yanga toh ai mai sauqine tinda ku kuka dami kanku ba nina saku ba, sabida haka saiku daina karantawa tunda ba wanda nasaka saiya karanta dole*
4โฃ8โฃ
Murmushi yayi sannan ya amsa sallaman
Cikin natsuwa tace ina yini
Fara arsa ya fadada yace lfy dan wani dadine ya lillibesa jin yadda ta amsa da faraa sannan yau har gaisuwa ya samu
Cikin murya mai sanyi yace gimbiyar mata asassautamun mana aidai ko haka na wahala
Juya idanuwa tayi cikin murya mai jan hankali tace namefa
Murmushi yayi sannan yace tinsafe nake kira baki dau wayata ba pls ko shiruma nikiyi amma dai kidauka sai hankalina ya kwanta
Hakan daya fada shiyasa ta wani qayattacen murmushi wadda ya qawata face nata tace ayyah aifa ba dagangan bane ba bani kusane kuma yanzun bagashi nadauka ba
Cikin murmushi yace hakane nagode da kika bani lokacinki amma da zaa taimakamun abani dama nazo gida mugaisa
Shiru tadanyi dan harga Allah bata san takuri amma kuma yau sai takejin nauyinsa sosai
Maganarsa ce ta katse mata tunani yana cewa ya kikayi shiru pls fauziyyah kibani dama na bayyana maki irin sonda nake maki wlh tunda nake arayuwana bantaba jin son wata mace aduniya kamar yadda nake sonkiba kuma ni inkika amince mun insha Allah zan zamar maki alheri arayuwa amma kibani dama domin kitabbatar da maganata
Jikintane taji ya mutu murus kuma ya tuno mata da wasu kalaman da papa ya taba fada mata abaya
Cikin sanyin murya tace bakomai ur always wellcome
Wani dadine ya lillibeshi yace thanks a lot my life insha Allah gobe da yamma zanzo
Cikin murya mai kamada shagwaba tace gobe kuma gaskiya is to early
Cikin rarrashi yace haba my life ai da zafi2 akan bugi qarfe amin haquri dai nazo goben kinji my life
Murmushi mai dan sauti tace ok Allah ya kaimu
Papa dayakai har wuya dan takaici dan tini ya fahimci da wani take waya
Jiyake kamar ya shige cikin wayar yazugamasa rashin mutunci dan wani kishine ya tirniqeshi dan ya fahimci ya samu waje tinda taketa zuba murmushi
Cikin qunar rai ya miqe afusace yayi side nasa
Ganin yadda ya tashi afuce nan danan fiskarsa ta canja hakan yasa TJ ya tashi yabi bayansa
Adaki yasameshi sai safa da marwa dayakeyi acikin daki
TJ yana shiga yace yadai man lfy kuwa lokaci daya kacanza
Cikin damuwa yace badole nacanba kana kallo cin fuskan da fauziyyah tamun
TJ yace haba man kada wannan ya dameka kabi ahankli mana kadaina bata ranka
Cikin fushi yace wani irin kada na damu bayan fauziyyah ta nuna batasanniba then gashi tana hira da wani awaya harda yimasa murmushi haba haba
Ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka
TJ yace pls man cool down ur temper komai zaizo dasauqi da yardar Allah ammafa saikabi komai ahankali kuma daki2
Cikin sauri yace kamar me kenan pls tell me abokina wlh ruwan kaina ya qare i dont know what to do
TJ yace zauna kaji yadda zamu bullo wa lamarin
Zama yayi ya paying full attention nasa akan TJ
TJ yace dafarko abinda nakeso dakai kasauqe dik wani abinda kakeji dashi agefe sannan ka cire saurin fushi kadau hakuri kasa ma ranka
Wannan shine matakin farko dan dole sai kayi haquri
Sannan kasameta anatse kabata haquri akan abinda kamata kanemi yafiyarta dan inba hakaba bazaka taba samun fiska awajentaba matuqar tanajin haushinka tana kuma tuna abinda ya faru abaya
Amma idan har tayafe maka ta haqura to komai zaizo dasauqi
Papa yace wlh nima inada niyyar bata haquri saidai bansan ta ina zan fara ba tunda lokacin data gannima cewa tayi bata sanniba kuma wlh abin yacimun rai ya dameni kuma ya dagamun hankali
TJ yace tafada ne kawai sabida tanajin haushin abinda kamata shiyasa nace kafara bata haquri tukunna
Sannan katattara dik wani halin banza ka zubarshi agefe wannan shaye shayen banza da wofin ka haqura dashi dan ba macen arziqi da zataso mijinta da wannan halin
Papa yaja wani dogon numfashi yace hakane kamtunba yauba dama komai ya ficemun arai kuma dayardar Allah nabar shan komai tinda suma basa qaran mutum da komai
TJ yace good abokina