Showing 57001 words to 60000 words out of 87071 words

Chapter 20 - Budurwar Kauye Hausa Novel

07 Oct 2024

13128

ta rage masa baibiba shine Abba

Kuma gaskiya yanajinjina taya zai kalleshi bayan abinda ya aikata abaya

S
ai dai kuma yaduba yaga baya da wani option gara yaje yasami Abba wataqil yadace acan tunda yasan Abba mutumin kirkine...

✍🏻Faty Mmn Faty



🌾🌾🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾



Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€

Written by Faty Mmn Faty

September, 2017


5⃣4⃣
Shikadansa ya gama shawarinsa baikuma fada ma kowaba
Gari na wayewa sassafe asuban fari ya dauki hanyar dambam

Cikin ikon Allah qarfe tara ya shiga garin dambam
Gidan Abba ya nufa saidai zuciyarsa tana ta bugawa dan baisan yadda Abba zai karbi maganar ba shinko zai sauraresa ko zaimasa irin abinda daddy yamasa

Da haka harya qaraso qofar gidan yana isowa Abbah yana qoqarin fita

Parkin yayi cikin dauri ya fito dan harya shiga mota

Saida yazo har jikin motar sannan Abba ya ganesa dan yasha jumfer har qasa ga hula hakan yasa Abba baikawo shibane

Da faraarsa ya bude motar yana qoqarin fitowa cikin sauri papa ya tsugunna yana cewa sannu Abba

Aa tashi tashi zaka bata jikinka ai tashi muje cikin gida mana

Tare suka shiga side din Abba dan mama bata gari sunje biki jos

Harqasa ya duqa ya gaisheshi

Shima da faraa ya amsa yace amma dai agarin ka kwana ko

Cikin ladabi yace aa yanzu isowana

Ah lalle kayi sammako yasu daddy dasu hajiya

Dik lfynsu qalau ya amsa

Masha Allahu yayi kyau

Shiru ya danyi kafin yace dama wajenka nazo Abba

Abba ya gyara zama yace toh lfy daikam inasauraronka


Qasa da murya yayi yafara magana cikin nadama yace Abba tabbas nimai laifine awajenku kuma nasan nayi kuskure amma kuyafemun badan halina ba kuyi haquri...

Katseshi Abba yayi da cewa ya isa haka Alamin kaifa danane kum ni bakamun komaiba sabida haka komai ya wuce kuma naji dadin yadda naganka cikin kamala ubangiji Allah ya yafemu gaba daya

Cikin jin dadi yayita godia Abba yace bakomai ya wuce

Sannan yasake qasa da murya yace dama Abba nazo roqon alfarmace awajenka

Abba yace namefa Aminullah

Yace dama Abba fauziyyah ce nakeso tadawo dakinta shikuma daddy yaqi amincewa nan ya zayyane masa yadda sukayi da daddy
Abba dan Allah badan halina ba kutausayamun yanafadin haka yayi shiru dan jinsa yake kamar zaiyi kuka


Abba ya nisa ya dubesa cikin kulawa kafin yafara magana
Yace da darko sai ince Alhamdulillahi daka fahimci kuskurenka kuma naji dadin yadda kaxo kasameni kaitsaye tun abubuwa basu kwabe

Kuma gida bai qoshiba aibazaa bawa dawo ba
Amma alhji bai kyautamunba yana sane da kanason maida matarka ya hana sannan ya shigoda wata magana

Kuma shi wadda yake neman nata aibaasan halinsa ba

Tunda Allah yasa kazo kasanarmun halinda ake ciki to tazo gidan sauqi insha Allahu gobe zanzo bauchin muyi magana da Alhajin

Wani dadine marar misaltuwa yaji yana ratsashi ta ko ina

Sake risinawa yayi yana godia sosai

Abba yace dakaida fauziyyah dik daya kuke awajena sabida haka ka koma abinka kasa aranka fauziyyah matarka ce insha Allahu

Godia sosai haryasa kalmar dazaiyi amfani da ita tsabar murna

Haka yayima Abba sallama ya kamo hanya zuciyarsa wasai
Rabonsa dayaji farin ciki irinna yau harya manta ranan

Gabda laasar ya iso gida wanka yayi ya fito yaci abincinsa hankali kwance

Momcy dai tayi mamakin canzawarsa amma dai tayi shiru batace komaiba

Yana nan zaune afalo tafito ta wucesa tinda yaga fitanta awannan lokacin yasan wannan man dinne yazo ko ajikinsa saida yagadama sannan ya tashi ya dauko car key nasa da wayoyinsa yayi waje

Motarsa ya shiga saida yazo dafda su sannan ya sauqe glass ya nunasa da hannu yace hey kada kabari nadawo nasameka tareda matata kuma zaifi maka sauqi idan katafi kada kasake dawowa

Duban papa yayi da kyau yace matar ka kuma ta ina tazama matarka

Yace bani da tym inada wajen zuwa amma katambayeta ita zata amsa maka ai yana fadin haka ya daga glass din motarsa ya wuce abinsa

Fauziyyah kuwa abu biyu su suka dameta nafarko yadda ta boyema Brr cewar papa shine mijinta na farko sannan yadda papa yake iqirarin wai ita matarsa ce

Brr. Ya kalleta da kyau yace wane ne wannan awajenki

Ahankali tace yaya nane

Yace kada kimaidani bitacan mana inason kifadamun gaskiya miye alaqarki dashi dan najima da fahimtar akwai abinda kika boyemum game dashi

Nan idanunta sukayi raurau tace wlh ba abinda nake boye maka kawai dai banason tuna abinda yafaru abayane

Yace naji amma kada kifadamum shine mijin da kuka rabu

Murya na rawa tace shi shine

Wani baqin kishine ya taso masa cikin fada yace i see shiyasa ashe yakemum abinda ya gadama kekuma kikaqi sanar dani ashe dama tsakaninmu akwai yar boye

Tace bahaka bane

Yace toh ya ne inba haka ba kawai bakida abinda zaki fadamun

Haka taita bashi haquri dan ta lura ransa ya baci shima haka ya tafi yana tunani kalakala

Washegari Abba yazo inda suka zauna da daddy akan maganar su papa

Amma fir daddy yace baisan zancenba idan har papa aure yakeso ya nemo awani waje

Abba yace toh shikuma baiga dalilin da zaa hana papa fauziyyah ba

Nan dai suka ringa muhawara har Abba yayi nasaran shawo kan daddy amma da sharadin sai fauziyyah ta amince

Abba yace batun wannan yaron sai adakar su amma aini har raina ya baci ace taya zaka hana alamin fauziyyah

Daddy yace bawai hanashi nayiba kawai abinda ya aikatawa kansane

Abba yace aiyawuce Allah ya kiyaye nagaba

Abba yace toh shizai tafi amma yanason magana da fauziyyah

Bayan tazo Abba ya dubeta yace mama na ya aiki

Lfy lau Abba ya mama sai gobe zadu dawo tacemun ko

Yace eh sai gobe insha Allahu ai anyi biki kam kuma sunyi ziyra

Tace hakanekan

Abba yace mamana ya maganar yaronda yake zuwa wajennaki kinsanar masa ya turo dinne

Shiru tayi tana tunanin dama akan jiyane zata sanar masa saikuma yatafi cikin bacin rai hakan yasa bata fada masa ba

Abba yace baki amsamunba

Ahankali tace aa banfada masa ba tukunna

Abba yace Alhamdulillah dabaki fada masaba amma kisaurareni kiji abinda zanfada maki

Dafarko nahadaki aure da dan uwanki baason rankiba wadda zan iyacewa dole namaki

Toh yanzun lokaci yayi daya kamata ace kina da aure tunda dik abinda ake nema na rayuwar duniya kinsamu daidai gwargwado

Toh wannan karon bazance ga miji na zaba mikiba amma amatsayina na mahaifinki zanbaki shawara idan har ta miki

Batun maganar Alamin ason raina shine ki amince ki koma dakinki

Cikim sauri ta dago kanta tana kallon Abba

Abba yace bafa nace lallai bane aa shawarace kiduba kiga yanda iyayensa suka daukeki tamkar su suka haifeki

Sannan dik yadda suke tayaki kin Alamin kisani bayadda suka iyane tunda kema kin nuna bakyaso amma suna son dansu kuma sunason farin cikinsa

Kuma nima har zuciyata inasonki da alamin sabida haka kije kiyi tunani da kyau akan maganata

Kuma tunda mutum ya maka laifi ya kuna nemi gafara aisaika yafemasa

Fauziyyah dai nan take tafara hawaye

Abba yace aa nifa banace tilas bane inhar kinfison wancan din shikenan amma ni shawara nake baki kuma kije kiyi tunani mai zurfi

Tsabar kuka gagara magana tayi har Abba ya miqe yace zaitafi shikam

Dakyar ta iya cemasa Allah ya kiyaye hanya

Ranan kasa runtsawa tayi lalle maganar Abba gaskiyane kodan su daddy yakamata ta amince da ya Alamin saidai kuma bata sonsa

Wata zuciyar tace shima Brr. Aiba wani sonsa kikeba

Tunani kawai take taya zata koma zaman aure da ya Alamin tayi kuka har idanunta ya kumbura

Kwana biyu da zuwan Abba abubuwa sun dameta gashi Brr koya kirata awaya bata dauka dan batasan mezata cemasa ba

Shikuma yadauka bata huce bane tun abinda ya faru

Kwanan Abba hudu da zuwa tayanke shawaran amincewa da Alamin amma badan tana sonsa ba saidan farin cikin Abba dan tafahimci yanasonta da Alamin ya boyene sabida kawaici

Haka su daddy ma tasan kawaici kawai suke mata

Ranan tayi kukan rabuwa da Brr hartaji ba dadi

Waya ta kira Abba ta sanar masa ta amince ta zabi ya Alamin

Abba ya ringa samata albarka da mata adduoi sannan yace toh tasanar ma daddynsu shiba ruwansa kada daddy yace shiya tursasata


Suna zaune afalo da daddare tasamu momcy tace tafasa auren Brr. Ita ya alamin zata aura

Momcy tace aa fauziyyah kada kitauyema kanki haqqifa

Tace aa ta amince har zuciyarta

Tashi momcy tayi taje tasamu daddy da maganar

Yace ta kira masa fauziyyah tana fita papa ya shigo bada jimawba suka dawo tare

Bayan ta gaida daddy daddy yace yanzu mom dinku tazomun da wata magana inasonjinta daga bakin

Qasa tayi da kanta sannan tace haa daddy me tayyarki shaadi ya Alamin(hakane daddy na amince da auren ya Alamin)

Wani lamarine mai sanyi papa yaji yana shigarsa tindaga qafarsa kamar anjiqashi da ruwan qanqara

Idanu kawai ya zubawa fauziyyah yanajin wani sabon sonta har cikin ransa....


✍🏻Faty Mmn Faty



🌾🌾🌾🌾🌾?🌾


🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾



Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€

Written by Faty Mmn Faty

September, 2017


*Wannan shafin nakune kudanku masoya Budurwar Qauye, Mmn Faty tana godia kuma tana qaunarku adik inda kuke,wadanda banisamun damar mayar masu da reply na messages nasu suyi haquri banmanta dasu ba abinne dayawa amma nagode sosai Allahu ya bar qauna 😍😘*


5⃣5⃣
Wani farin cikine ya ziyarci daddy jin abinda fauziyyah tafada da bakinta

Murmushi yayi mai cike da annushuwa yace zonan yar gidan daddy matso kusa dani

Babu musu ta tashi tamatso kusa da qafafunsa ta zauna ta sunkuyar da kanta

Cikin murya mai taushi daddy yace daugther na kifadamun gaskiya dakanki kika amince zaki auri Alamin ko kuma Abbane ya tursasaki

Girgiza kanta tayi cikin natsuwa tace aa bashibane ba baima da masaniya akan hakan

Alhamdulillah Allahu ya hada kanku ya kuma kauda fitina
ALLAH ya maki albarka ya baki yara masu biyayya kamar yadda kika mana

Momcy tace amin ya Allah dan itama wani farin ciki takeji marar misaltuwa tana kuma jin son fauziyyah har ranta

Daddy yace tashi kije abinki Allah ya maki albarka

Asanyaye tace amin sannan ta miqe ta fice dakinta tana shiga tafada kan gado ta bude sabon shafin kuka

Daddy kuwa tana fita ya maida hankalinsa kan papa wadda shikuma yabada full attention nasa akan hanyar waje inda ta fice ya bita da kallo ya kuma gagara dauke idanunsa

Daddy yace toh nadawo kanka yafada yana kallonsa

Jin muryar daddy yasa ya juyo yana kallon daddy

Kasaurareni da kyau kaji abinda zanfada maka

Nafarko kagodewa Allah da mahaifin fauziyyah mutumin kirkine sannan itakuma yarinyace mai biyayya

Toh kagama bin kafa har kasamu burinka ya cika

Amma kasani bazan lamunci kwatankwacin abinda ya faru abaya ba

Matuqar kanason zama inuwa daya da ita saika sake halayenka tass

Cikin ladabi papa yace insha Allahu zankiyaye daddy

Daddy yace Allah yasa sannan tunda burinka ya cika saika tattara kakoma gidanka gobe dan bazaka zauna karinga takura mata ba

Ko ajikinsa yace shikenan daddy Allah ya kaimu

Daga haka ya musu saida safe ya fice zuciyarsa fari qal qal

Yana fitowa ya nufi dakin fauziyyah cikin saa kuwa qofar abude take

Falon shiru sai qaran AC gami da wani sansanyan qamshi wucewa yayi har cikin bedroom nata

Da sallama ya shiga kwance ya hangota tayi rubda ciki akan bed kuma bata amsashiba

Wani kasalane yaji ya sauqo masa ta dalilin abubuwa uku

Nafarko sanyi da qamshin daya doki hancinsa na biyu tsaftan dake tattare da dakin kamar kada ya fita haka yakeji
Na uku yanayin kwanciyar da tayi saiyaji kamar ya qarsa ya kwanta ajikinta dan saiyaji dik hankalinsa ya tashi

Gashi dama wata yaloluwar doguwar rigace ajikinta dazataje wajen daddyne ta daura hijab akai tana shigowa kuwa ta cire
Dik tabi jikinta ta manne sannan ta bayyana illahirin suran jikinta

Wani yawu ya hadiya yana godema Allah daya sanya fauziyyah zata zama mallakinsa

Itakuma tanajin motsin bude qofa da sautin muryarsa taji wani baqin ciki yasake kamata

Banza tayi dashi kamar batasan da shigowarsa ba

Ahankali ya tako har bakin gadon leqa fuskanta yayi nan yagane idanunta biyu kuma kuka mq takeyi dan ganan hawaye shabeshabe akan fiskanta

Nan take yaji ya damu gashi baisan dalilin kukan nata ba

Cikin murya mai tattare da natsuwa da kulawa ya kira sunanta My Fauzy

Wani dam taji zuciyarta ta buga sakamakon tuno mata da yasir da yayi dan shine kadai ke kiranta da wannan

Anatse yasake kiranta My Fauzy sunotoo(kinajina)

Nanma banza tayi dashi kamar da dutse yake magana

Zama yayi agefenta ya riqo hannunta dake gefensa ya sake qasa da murya cikin sanyi yace My Fauzy pls jababdo(ki amsamun)

Bata kulasaba sai yunqurin kwatan hannunta daya riqe takeyi

Saqe riqe hannunta yayi gagam ganin baya da niyyar sakinta saita rabu dashi kawai

Tambayarkifa nake why ar u crying n baki amsaniba yafada atausashe
Ganin batada niyyar yimasa magana yasa ya cigaba da fadin

Koma meke daminki pls kiyi haquri kibar kuka banson kanki yayi ciwo ko idanunki yayi ja

Nazo namaki godia ne akan amincewa da kiyayi zaki aureni
Inkuma qara baki haquri akan abinda namaki abaya

My fauzy inaroqonki kibani dama na nuna maki irin sonda nake maki
Nayi nadamar abinda na aikatamaki abaya
U don't know how much i regret everything that i have done to u

I luv u my fauzy i luv u with all my hrt

Magana yake yana murza dan yatsun hannunta masu laushi da taushi kamar na jarirai

Maimakon taji sanyi aranta sai tasakejin wani zafi aranta nan tasake fashewa da wani sabon kuka mai sauti ahankali

Nam yayita lallami da maganganu masu dadi amma abanza harya fahimci maganarsane batasonji akan dole ya miqe ya fita yanajin kukanta har cikin zuciyarsa

Adaren ya kira TJ ya shafa masa halin da ake ciki

TJ yayi murna sosai ya kuma sake bashi shawara mai kyau akan kada gaba ya kuma gangancin kwatanta abinda ya faru abaya

*******
Washegari daddy ya tafi dambam nan suka zartar da maganar biki sai nan da watanni biyar masu zuwa
Kafinnan angama ginin sabon gidan da zaa kai fauziyyah

Yan uwa kowa yayi murna da samun labarin komawar fauziyyah musamman saida aunty mabarukha tazo bh takuma dauki nauyin gyaran amarya idan lokaci yayi

Haka maman fauziyyah da farko taqi yadda saida Abba yamata nasiha sannan ta amince takuma sanya Albarka

Da aka sanarda papa lokacin auren sai cewa yayi shifa lokacin yamasa tsayi gaskiya

Momcy harta qulu tace tosaika rage tunda ka isa da hakan

Cikin sati daya magana tagama kankama har daddy yabada contract na ginin gidan sabon gidan papa amma wanna karon a kusa dasu nan *Gida Dubu*

Wani filin daddy dake kusa da gidan Aunty naja dambam sukayi shawaran gina masa

Momcy tace gara kusa da auntynsa tunda koba komai yafi shiri da ita kuma zatana leqasu akaiakai taga inda yayi ba daidaiba tasashi ahanya

Dan abinda ya faru abayama harda rashin wani babba akusa wanda yake leqasu

Daddy ya amince da shawarin momcy

Daddy ganin har sati guda papa baida niyar komawa gidansa yasa ya kirasa yace ayau dinnan yayi parking inba so yake ya saba masa ba

Babu musu ya hada kayansa ya loda a mota sai abinda baa rasaba ya bari saidaga baya zaizo ya dauka nan ya


nufi gidansa dake sokoto road wadda rabonsa da gidan tun rabuwarsa da j
uhaina....


*Wai ina labarin juhaina kam[truncated by WhatsApp]


🌾🌾🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾



Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€

Written by Faty Mmn Faty

September, 2017


*This page goes to Aunty Faty G Dambam, Nagode da qaunar da kike nunama littafina, Insha Allah 2019 Bauchi sai Proffessor, Mmn Faty Luvs u 😍😘*
5⃣6⃣
Hankali kwance yake driving har ya qaraso

Amma yana isowa gate sai yaji ransa ya baci cos nan take kwakwalwarsa tafara recalling masa abinsa yafaru lokacin rayuwar da yayi da ex wife nasa juhaina

Horn yafara mai gadi ya bude masa gate dan yasan da zuwan ogan nasa cos ya kirasa awaya kan cewar agyara gidan before ya yazo

Qarasa shiga yayi har parking space yayi parking motarsa

Qarema gidan kallo yake saiyaga ya canza masa kodan ya jima rabonsa da gidanne oho

Koda kudin buqatar maigadi da sauransu saidai suyi waya yazo ya karba

Wani iska mai zafi ya furzar kafin ya bude qofar motan yana tattara wayoyinsa

Yana fitowa daidai da isowar maigadi kenan

Sannu da zuwa yallabai ya fada yana risinawa

Cikin kulawa yace yawwa ya gidan dai hope babu wata damuwa

Aa babu konai yallabai ankuma gyara ko ina kamar yadda ka umarta sai dai daki daya wadda yake akullene da baa gyara ba sabida acikin keys da suke wajena babu nasa aciki

Ok babu damuwa i think key din yana wajena barin qarasa ciki zan fito saika shigar mun da kayana idan kuma Abdu ya iso shikenan

Toh yallabai afito lfy

Wucewa yayi ciki inda yabar maigadi da mamakin canzawar ogan nasu

Tun bayauba ya lura da sauyin idan yaje wajensa but nayau dabanne lura da yadda ya bada time nasa sukayi magana ta fahimta

Falo ya bude ko ina tsaf sai qamshin room freshner da sanyin AC

Ba komai acikin falon sai carpet dake tsakiyar falon

Wucewa yayi falonsa nanma komai agyare yadda yake ba kuma abinda aka taba

Kallon dakin juhaina yayi kamar ya wuce amma sai ya qarasa ya bude nanma bakomai ciki da sauri ya jawo qofar ya rife hadida rintse idanu sabida tuno da abinda ya faru da yayi

Cikin sanyin jiki ya wuce dakinsa key yasa ya bude qofar

Qurakam baa magana ko ina yayi qura kallon dakin yake sosai fridge ya bude nanma da sauri ya kulle ganin kwalaben wine iri da ban daban

Ga wasu kwalabe a zube aqasa ga kuma kwalayen sigari da dai sauran kayan shaye shayensa

Lokaci guda yaji kyaman dakin ya kamasa fitowa yayi ya shiga kiran layin Abdu bada jimawaba ya daga hello oga sir am sorry pls na kusa isowa

Ok am ka tsaya ahanya kasamomin kwalaye manya mana ammafa empty

Ok badamuwa ya fada

Bada jimawaba ya qaraso da manyan kwalaye kamar yadda aka sashi

Karba yayi ya shiga loda tarkacen aciki saida ya kwashe su tas sannan ya manne su tass ya kira Abdu yace yayi waje dasu ya loda su a boot

Falo ya dawo ya zauna ya jira Abdu ya gyara masa dakin nan ko ina ya tsaftatu kamar bashiba

Kayansa suka shigo masa dasu daganan ya wuce toilet ya watsa ruwa hadi da alwala

Agurguje ya shirya ya nufi masallaci

Sai da yayi ishai sannan ya dawo

Yabawa Abdu kudi ya samo masu abinci

Bayan yayi dinner ya jawo system nasa ya kunna ya duba wasu abubuwa sai dai ya gagara samun natsuwa

Jingina yayi da jikin kujera ya lumshe idanunsa ya tuno fiskar luv of his lyf

Jiyake inama yana da no wayarta daya kira yaji muryarta ko zaisami sukuni

Gashi ya na zaune shiru shikadansa dik kadaici ya damesa

Wayarsa ya jawo ya kira TJ

Amma baidaukaba harta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login