Showing 45001 words to 48000 words out of 87071 words

Chapter 16 - Budurwar Kauye Hausa Novel

07 Oct 2024

13112

taho bh

Daddy yayi murna sosai

Sannan yace meye shawarin aunty

Aunty tace yanzu dama sun sayi jamb form sun kuma sayi form na gwagwalada university

Daddu yayi shiru yace jiya sunyi magana da mr khan wani friend nasa dake india

Kuma yamasa magana akan asamawa fauziyyah gurbin karatu a jami'ar new delhi

Kuma ya tabbatar masa wannan badamuwa zai trying best nasa yace atura masa takardunta

Sosai sunji dadin shawaran da daddy ya yanke

Kwanansu daya ta wuce dambam abinta dan bata kaunar abinda zai hada ta da papa

Cikin watanni uku komai ya kankama na tafiyar fauziyya dan tasamu admission kuma agidan mr khan zata zauna dan abokin daddy ne sosai

Ranan talata su daddy suka kaita airport dake lagos dan tacan zasu tashi

Qarfe uku na rana jirgin su fauziyyah ya bar nigeria ya nufi india...[truncated by WhatsApp]





[7:12PM, 8/26/2017] β€ͺ+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾


Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017



*I dedicated this page to Zainab Abdulmumini(Mmn Samha) n My Swt Sis Fauzy, Allahu ya barni daku Mmn Faty 😍😘*


4⃣5⃣
Dawuri ya dawo gida cos yana da sugery da yamma a asibitin daddy

Akwai wani mutum da zaamasa aiki a spinal cord nasa

Yana shigowa tin daga parking space ya gane juhaina bata nan sabida he did not see her car

Key nasa ya bude qofa ya shiga ciki dan inda sabo ya saba da hakan

Dik randa ya kuskure ya bar key nasa kuwa to zai zauna a gate jiranta

Sabida rana daddaya ne zai dawo yasameta agida

Room nasa ya shiga ya kwanta nan bacci ya kwasheshi sai pass 3 ya tashi

Cikin dauri ya shirya ya fito sabida 4:30pm zai shiga aikin

Fitowa yayi ya kulle dakinsa dan ya kuskura ya bari abude sai tamasa barna

Amma ga mamakinsa bata dawoba ficewarsa yayi kawai abinsa

Bashi ya fitoba sai wajen 7 sallah yayi sannan ya nufi gida amma sai daya tsaya a resturant yaci abincinsa sannan ya wuce gida

Dagangan yaqi saya mata yace taci yawon taqoshi yau bazai saya ba

Har lokacin daya koma gida nanma bata dawoba

Tabe bakinsa yayi yaje yayi wankansa yayi sallah sannan ya fito ya kunna press tv yana kallon wani program da sukeyi

Har wajen 9 sannan yaji shigowarta

Gyalenta a hannu ta shigo falo

Ganinsa azaune sai tayi kamar bata ganshiba zata wuce
Keh daga ina kike da wannan daran yafada yana kallonta

Ko cikanka bata ce dashiba zata wuce ta gefensa

Cikin sauri ya riqo hannunta yace bada ke nake maganaba nace daga ina kike

Hannunta zata fisge yayi saurin sake riqeta sosai sannan ya miqe tsaye

Yace juhaina wai me kika maidanine dan iskanci ina maki magana sai kiqikulani toh inkinga kinbar wajennan sai kinfada mun daga gidan ubanwa kike at this time

Wani walaqantaccen kallo ta wurga masa sannan tace daga gidan uban mai tambayar nake

Nan take yaji xuciya ta debeshi watoma harshi zata zaga

Aiko nan take ya daga hannu ya wanka mata mari mai kyau

Yana sauqe hannunsa itama ta daga hannunta ta zabga masa mari tana huci tace kai har ka isa kadakeni to ko ubana bai dukana baran kai banza a banza ta fisge hannunta ta wucectabarshi

Shikuwa mamaki ne da baqinci suka hanashi cewa komai ko ya tanka mata

Wani zafi ne kawai yakeji yana taso masa daga kasan zuciyarsa kamarshi ace matarsa har tadaga hannu ta mareshi

Tsabar bakin ciki nan take idanunsa suka caza launi suka qanqance

Dakinsa ya nufa ya bude fridge ya dakko wine nasa ko takan cup baibi ba

Ya dannan bakin kwalbar amma maimakon tamasa dadin sha sai yaji wani daci sabida yadda zucitarsa ke tafasa

Nan take sai tunanin fauziyyah ya fado masa

Yaune rana tafarko daya fara tunota tinda ya saketa

Tunanin yadda yake nada mata duka yakeyi amma koda wasa bata taba tunanin fada masa magana mai muniba baran tarama

Ya walaqanqanta ta son ransa amma yarinyar nan haka zata haqura sai dai tayi kukanta tayi shiru bata taba fada ma waniba

Anya kuwa yamata adalci kuwa nan yaji xuciyarsa tasake quntata

Kotana ina yanzu ko wani hali ta shiga lokacin daya saketa bada haqqinta ba

Nan take zuciyarsa tafara bugawa da sauri sauri

Nan yafara tuno irin yanayinta kyan fuskarta yanayin jikinta

Tuno rananda yafara ganin qirjinta yayi nan take yaji wani kewanta marar misaltuwa yana shigansa

Zuciyarsa take raya masa inama har yanzun itace matarsa ba juhainaba daya rungumeta tsakani da Allah da bai cutar da ita ba

Nan ya tuno qamshin girkinta idan tana dafa abinci amma zuciyarsa ta cuceshi ta hanshi aminta da ita

Cikin qunan rai yake zargin kansa da mai yasa tunda baiga wannan abubuwanba sai yanxu da bai masan inda takeba

Nan wata zuciyar tace wataqilanma tayi aure abinta

Damm yaji zuciysrsa ta buga wani zafi yasakejin yana mamayeshi har yana zufa dikda sanyin AC dake bugawa

Haka ya ajiye kwalbar giyar dan bazai iyama shaba

Yadda yaga rana haka yaga dare sabida tunani daya addabeshi ya kuma tabbatar ma kansa zuciya takaishi tabaro tunda gashi yau yarasa tudun dafawa


Tundaga wannan ranan tsanan juhaina ya dasu a azuciyarsa amma haka yake zaune da ita ya kuma kasa saketa

Hakadai suke zama marar dadi

Sai abinda yafi daminsa wato yadda tunanin fauziyyah ya addabi rayuwarsa ba dare ba rana

Wani matsanancin son kasancewa tare da ita yakeji

At last ya tabbatar ma kansa sonta yakeyi

Rasa mafita yayi yaje yasami TJ ya fada masa abinda ke faruwa

TJ yaso yayi masa dariya amma ganin halin dayake ciki sai ya danne

Yace toh wai bakada labarinta ne

Papa yace banma san inda takeba ko agidan momcy ban sake ganintaba

TJ ya nisa yace toh yanzu shawarn da zan baka kadage da addu a idan rabon kace tadawo gareka

Nikuma zan tambayi khairy tunda yar uwartace dole nasan tana da labarinta inma aure tayi inma ko me nene zamuji

Godia yayi ma TJ sosai dan har yadan sami natsuwa

Amma da TJ ya tambayi khairy hanya hanya tamasa kawai taqi fada masa gaskiaya

Shima haka dai yayima walawala ya qi sanar masa khairy taqi fada masa dan kada yaji haushinta

Haka rayuwa tayi ta tafiya inda papa yake cikin wani hali yakumayi dana sanin abinda ya aikata abaya kuma har gobe fatansa Allah ya nuna masa fauxiyyah ya roqi gafararta dan yanxu yagane cewar alhakinta ya ke bibiyarsa

Ba abinda ke qara daga masa hankali kamar yarda kullum sonta yake qaruwa acikin zuciyarsa

Watarana ankawo wata yarinya asibitinsu tasamu matsala a guiwarta daga faduwa

Aifa tun dayaji sunanta fauziyyah shikenan haka yaringa hidima da ita har aka sallamesu sabida yarda yake qaunar mai sunan

Kuma yasama ransa dik ranada yasan inda fauziyyah take kuma bata da aure tabbas koza ayi yaqi sai an maida masa da matarsa idan kuma basu sake haduwaba yasan sontane zaiyi ajalinsa


*****
Fauziyyah ta sauqa lfy, inda tasamu tarba na mutunchi awajen mr khan da matarsa da yaransa yan mata guda biyu

Kwanan ta biyu da zuwa tafara xuwa makaranta tanajin dadin karatunta sosai gashi Amisha tana taimaka sosai akan abinda bata ganeba

Cikin ikon Allah karatunta yana tafiya yadda akeso

Da haka har tacinye shekarar farko

*Bayan shekara biyu*
Fauziyyah ce zaune tana hada kayanta cikin farin cikin sabida gobe zata koma gida nigeria cikin nasarar uban giji ta kammala karatunta da saka mako mai kyau

Yanzu tazama cikakkiyar *PAMACIEST*

Cikin shekaru ukun datayi sau biyu kawai taje nigeria

Washegari jirgin qarfe 9 nasafe ta biyo sai gida

Acan nigeria kuwa su daddy ne da momcy da su aunty mabarukha harda aunty niima sukazo taronta dan akwai liyafar da daddy ya shirya mata a nan abuja

Jirgin na sauqa na hangota cikin jerin fasinjoji amma zaka rantse da Allah baquwace tazo daga india kuma zata koma sabida yadda fatarta ta murje tayi wani haske na musamman kyanta yasake fitowa

Kallo daya zaka mata kafimci zallan wayewa atare da ita dan tana daga cikin jerin mata masu class

Ko yadda take saqqowa cikin natsuwa kawai ya isa ya tabbatar maka cewa lalle wannan mace ce mai jida kanta

Daddy kuwa murmushi kawai yakeyi

Cikin sauri aunty ta qarasa ta rungumeta tana mata oyoyo

Wani daddan murya naji ya daki dodon kunnena hausa takeyi amma kamar maiyin indianci sabida yadda harshenta ya juye

Cikin farin ciki ta gaisa da kowa sannan suka nufi gida

Da yamma aka gabatar da liyafa mai kyau acikin gida

Sunsha hira sosai da daddare daddy ya kirata yace washe gari zasu wuce bh tare amma ita zata wuce dambam gida dagacan zai tura driver ya maidata abuja sai service nata ya fito sai tadawo bh tayi acan

Haka koh akayi watanta daya a dambam ta koma Abuja

Watanta biyu a Abuja service dinta ya fito amma jos aka turata nan daddy yamata cukucuku amaida ta bh

Tsabar tanada daurin gindi ko camp bata shiga ba

Sai byan an musu posting aka duba nata anturata teaching hospital na bh

Ana saura sati daya ta dawo bh uncle salim qanin mijin aunty yazo da abokinsa Barrister Nabil Abdullahi gidan aunty mabarukha
Wajen aikinsu daya a bh yanzuma wani aikine ya kawo su abuja kuma babansa shine commissioner for works n houses na bh

Tunda ya kyalla idanu yaganta ya nacewa uncle salim shifa yaga wata balarabiya kuma tamasa

Har saida ya kira aunty awaya yafada mata abokinsa dasuka zo tare yaga fauziyyah yana so kuma ya fada masa ta taba aure yace ko dik yaran duniya ita ta haifa yaji ya gani

Aunty kuwa hakan yamata dadi nan take ta tura masa phone no fauziyyah

Tunda yasamu no shikenan waya ba dare ba rana text ne meyene amma sam fauziyyah bata kulashi dan ba namiji aranta sam

Ranan sunday ta taho bh dan monday zata fara fita aikinta na service

Isowan yamma tayi lis dan basu taso da wuri ba hakan yasa tayi bacci da wuri

****
Papa kuwa yau tun daya tashi yakejin zuciyarsa wani iri kuncine meye ne baima saniba gashi yana da aiki a office gashi akwai maganar da zasuyi da daddy kafin ya fita office

Dolee yasa da wuri ya shirya ya taho gida daga can ya wuce office

Fauziyyah kuma qarfe bakwai ta tashi tayi wanka ta shirya amma tayi ligh make up sai pink jambaki data goga a lips nata

Kayan su na coppers tasaka ajikinta nan naqare mata kallo da kyau

Rigat ta kamata sosai inda na fulaninta da suke a cike dam gasu atsaye suka cika mata gaban rigan hakama wandon hips nata da bayanta sunfito sosai dan ya kamata sosai

Gaskiya wadda yasan fauziyyah lokacin tana gidan papa yaganta yanzu bazi ganeta sabida yadda tacanza komai najikinta ya canza ga wani kyau na musamman data qara

Kallon kanta tayi tsaf a madubi sai taji kunya bazata iya fita waje ahakaba

farar qaramar hijab ta dauka iya guiwa amma bata saka ba sai ta riqo ahannunta

Nima sake kallonta nayi da kyau nan naga zallan kaman datake da *Arti matar Yash na cikin film din married again*

Cikin natsuwa ta dakko yar qaramar jakarta mai kamar purse ta rataya hannuntabriqe da hijab

Tana fitowa falo da momcy tafara haduwa bayan tagaisheta momcy tayi murmushi tace masha Allah kiyi maza kije wajen daddy sai kizo kiyi break ko

Cikin muryarta mai dadi tace ok sannan ta mufi bangaren daddy

Da sallama ta shiga cikin faraa ya amsa bayan ta gaidashi

Yadan mata nasiha sannan ya miqo mata key din motarta sabuwa dal daya saya mata yace motarki tana waje Allah ya kiaye hanya ki kula da tuki

Nan taringa godia sabisa baqaramin dadi taji ba

Daddy yace kada kidamu jeki abinki kada kimakara

Papa kuwa yana zuwa gida afalo ya samu momcy bayan sungaisa yace bari yaje wajen daddy

Tace toh sannan ya wuce

Momcy kuwa jin fauziyyah shiru gashi kada time ya wure mata yasa ta kwala mata kira

Dauther kiyi sauri kizo kiyi break kada kimakara

Fauziyyah kuwa ta fito tazo daidai kan steps da zata sakko falo taji kiran momcy

Dama sauri take taxo ta nuna ma momcyn kyautar da daddy yamata

Itama cikin daddan voice nata mai dadin sauri tace yess me arihoo momcy(ina zuwa momcy)

Daidai papa yasaka qafarsa zai haura kan steps da zai kaishi side din daddy yaji wata murya mai dadin gaske cikin harshen indianci tana magana

Saida yadan matsa baya data bugeshi dan cikin sauri ta wuce batama lura da mutum ba

Papa kuwa ganin kyakykyawar mace kuma ba india yasa yabi bayanta da kallo amma dake tariga da wuce sai bayanta daya kallah

Wadda hips nata yake masa gwaliyo

Lumshe idanu yayi ya bude gashi ta buleshi da qamshin turarenta

Cikin sauri ya riqe gini dan baisan yayi missing step ba

Jiki a mace ya shige dakin dadi amma muryarta sai yawo yake masa akwanyarsa


Bayan sun gaisa gagara haqura yayi yace daddy baquwa akayi agidanne

Daddy yace baquwa kuma

Papa yace eh kamar ma ba india ce kuma daga nan ta fito

Wani murmushi daddy yayi yace aa kam indai wacce tabar nan yanzune sai dai qanwarka

Papa yace qanwata kuma wacce qanwata nikuma inada qanwace


Daddy yace qanwarka fauziyyah mana yar gidan Abbanku na dambam

Cikin sauri ya dubi daddy yace Fauziyyah kuma itace ta fita anan


Daddy yace yawuce wai itace mana amma bar wannan maganar ina jinka yadda abin zai kasance yasa na ce kazo da safe


Ina papa hankali yayi gaba baimasan daddy yana yiba


Saida daddy ya lura baima tare dashi sannan ya tabashi yace kana jina Alamin

Cikin sauri ya firgita yace me kace daddy

Wani murmushi daddy yayi wanda shikadai yasan maanarsa........




✍🏻Faty Mmn Faty
[7:13PM, 8/26/2017] β€ͺ+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾🌾


🌾🌾🌾



Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017



4⃣6⃣
Daddy yace maganar bude asibitin nan ne dama najika shiru haryanzu baka fadi wani suna zaa sama ba sannan wacce rana ya dace sabida buga IV

Papa dai yayi shiru yana jin dadi amma harga Allah dakyar ya tsinci kadan daga abinda yake fada masa

Sabida hankalinsa da tunaninsa baya tare da daddy

Cikin wani yanayi yace zanyi tunani akai zuwa gobe zan sanar maka

Yafadi hakan ne kawai dan yasamu ya tashi awajen dan ya tabbata bazai samu natsuwa ba har sai yayi tozali da farin cikin rayuwarsa dan yana da good assurance batayi aure ba tinda ya ganta agida da wannan lokacin

Daddy yace is ok sai najika toh

Aiko daddy na rufe bakinsa ya miqe cikin sauri yana cewa barinje office

Daddy yace Allah ya kiyaye hanya

Yana tafiya ya amsa da Amin

*****
Fauziyyah kuwa cikin sauri ta nufi wajen momcy tana murna

Rungume momcy tayi tana cewa dekho momcy meri gari key (kalli momcy key din motata) daddy ne ya bani kitayani godia

Cikin faraa momcy tace masha Allah, Allahu ya tsare hanya

Amin ya Allah ta Amsa

Momcy tace kije kiyi break kada kimakara

Toh ta amsa sannan ta wuce dinning, dan kadan ta iya ci sabida murna tadawo falo tace zata wuce

Har bakin qofa momcy ta rakota tana cewa ganan motar taki jiya dare aka kawota Allah ya tsare sai kindawo sannan ta juya ta koma ciki

Itakuma qarasa wajen motar tayi sannan ta bude ta shiga tana jin wani dadi aranta

Ahankali tamata key sannan tafara tafiya cikin natsuwa har bakin gate inda mai gadi ya bude mata gate ta fice

Direct NYSC office ta wuce sabida akwai abinda zatayi acan kafin ta wuce asibiti


*****
Papa yana fitowa yaga wayam bakowa afalo sai motsi dayaji acikin kitchen

Leqawa yayi sai yaga momcy ce itakadai

Ziciyarsa ce yaji ba dadi dan fauziyyah yaso yasake kallo

Asanyaye yace na wuce office amma idan nadawo zan biyo

Toh adawo lfy tace dashi sannan ya fice

Motarsa ya shiga ya wuce asibiti driving yake amma hankalinsa na wani waje

Tinani yake yanzu fauziyyah ce tadawo haka yarinyar da ya raina yanzu itace tazama big girl haka

Ikon Allah ne kawai ya kawoshi lfy yana parking ya wuce office nasa

Zaune yake amma yakasa tabuka komai tunani kawai ya addabi zuciyarsa har yafarajin yarasa maike masa dadi

Ya jima azaune amma ko file daya baigama dubawa cikin sauri ya ture su gefe ya miqe

Dan jin kansa yakeyi yamasa nauyi ga wani irin faduwar gaba da kunci dake damunsa

Gara ya tafi gida ya kwanta kawai

Wayoyinsa da key nasa ya zara ya fito

Cleaners da masinja suna gaisheshima amma hannu kawai yake daga masu

Yana fitowa ya nufi parking space sai yaga wata mota mai kyau kalar mata ta tsaya agefen motarsa

Kafin ya qaraso sai yaga ta fito tana rataya jakarta

Sake zuba mata idanu yayi tabbas fauziyyah ce amma badan daddy yafada masa ba bazai ganetaba

Sai alokacin ya lura ashe kayan NYSC ne ajikinta tambayar kansa yake yaushe kenan haka tafaru

Fauziyyah kuwa dago kanta dazatayi wazata hango yana nufota ya Alamin

Tabbas shine dan bazai taba bace mata ba dik da yadan canza yaqara kyau yadanyi qiba kadan sannan daganinsa naira tazauna masa fiye da da

Ahankali tasauqe idanunta tanajin zuciyarta tana bugawa da sauri sauri

Nan take taji wani zafi azuciyarta dan bata qaunar abinda zai hada ta papa ko ahanyane

Daidai da ya qaraso jikin motarsa amma ya qudira aransa zai mata magana dan bazai iyah ganinta ya wuceba

Itakuma yitayi kamar bata ganshiba zata wuce kamar daga sama taji muryarsa wadda kodaga bacci tafarka bazata manceba


Yan mata shine abinda ya furta yana kallonta

Cak ta tsaya dan jitayi kamar ya caka mata wuqa wai yan mata

Dagoda kanta tayi ta sauqe dara2n idanuwanta farare tas masu kamar madara akansa

Nan yaji wani abu wadda bai san mene ne ba kawai yasamu kansa da lumshe idanuwansa yana tasbihi ga ubangijin halitta dan fauziyyah ta tafi dashi gaba daya

Muryarta ta dawo dashi daga duniyar tunani daya tafi

Cikin halin ko inkula da rashin damuwa tayi kamar bata sanshiba

Ya tsina fiskanta tayi tana masa duban rashin sani tace konhei tum(wane ne kai)

Kutt dan zaro idanu kadan yayi sabida mamaki wai harshine fauziyyah zatace bata ganeshiba

Amma sai yadaure yayi wani qayataccen murmushi yace mera naam Dr Muhammad Alamin Abubakar(suna na Muhammad Alamin Abubakar)

Ya tsina fuska tayi ta wani juya idanuwanta tace eyyerh sowwie am not talking with people that i dont know

Tana fadin haka ta wuce abinta bata sake koda kallonsa ba

Shiru kawai yayi yabi bayanta da kallo

Cikin qunan rai ya bude motarsa ya fada yana tuna irin walaqancin da fauziyyah tamasa ta yankwanashi

Afusace yafigi motar wadda dakyar yataka birki yabawa scurity pass sannan ya wuce

*****
Juhaina ce ta dubi munnir tace wai saurin me kakeyi ne kamar wadda ba agidan zaka kwana ba

Yace kinsan najima bangankiba wlh ina kewarki sosai muje ciki narage zafi

Murmushi tayi sannan tace haba

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login