Showing 36001 words to 39000 words out of 87071 words

Chapter 13 - Budurwar Kauye Hausa Novel

07 Oct 2024

13125

baijin magana ashe bai haquraba yana nan akan bakansa tunda har wani maganar aure zai tsiro

Daddy yace kibarni dashi yanason yaga bacin raina ne fiye da zatonsa


Cikin sati1 dik abun duniya ya dami papa

Baijin zai iya rabuwa da juhaina gashi abinda daddy ya fada yarasa ta inda zai bullo ma lamarin

Ko waya sukayi da juhaina ta tambayesa yatajisa wani iri cemata yayi baijin dadine kawai


Yanzun haka yana zaune a office tunani yake amma yarasa mafita

Qarar wayarsa ita ya dawo dashi daga dogon tunani daya tafi


Murya ahankali yace hello baby

Wani murmushi tayi sannan tace naam likitana, badai jikinba naji voice naka so cool haka

Sake gyarawa yayi ya kwantar da kansa yace kedai bari my queen fever ne yake damina amma yayi sauqi

Tace eyyer Allah ya qara sauqi n pls karage zama cikin AC da kuma shan abu mai sanyi dan nasan su zasu sakamaka fever

Cikin jindadin yadda ta damu dashi yace insha Allah my queen i promised u zan rage

Tace yawwa my king har kasa naji dadi amma kwana biyu ko waya mai dadi bamuyi

Yace no kada kidamu am feeling better fa

Tace toh shikenan sannan tasake qasa da murya cikin yanga tace am my king tinda kazo kacemun idan ka koma zakuyi magana da daddy kuma har yau bakacemun komaiba

Rintse idanuwansa yayi ya bude ahankali gamida danne damuwarsa yace wlh tunda kikaga banfada maki ba akwai dalili

Washegarin dawowana daddy yayi tafiya kuma two weeks zaiyi so idan ya dawo dik yadda mukayi zan sanar maki


Cikin jin dadi da gamsuwa tace Allah ya dawo dashi lfy

Ahankali yace amin


*****
Afannin TJ kuma su dad dinsa sunje masa tambaya inda baffansa da baban khairy suka gane juna dan abokaine sosai

Nan suka gabatar da abinda ya kawosu

Baban khairy yace tabbas da baida niyyar auren khairy nan kusa dan yafison ta kammala karatunta kamar sauran yan uwanta

Amma tunda yanzu abu yazama na gida ya amince amma dan Allah abarta taci gaba da karatunta

Nan suka yi godia sosai har aka tsaida ranan biki nan da wata biyu


Cikin ikon Allah lokaci na tafiya har aka fara hidimar bikin TJ

Inda naira tayi kuka kasancewarsa dan fari agidansu itakuma auta ce a mata

Sati guda ana shagali aka daura aure aka taho da amarya gidanta dake bauchi unguwar sokoto road


Sai muce Allah ya bada zaman lfy Amin


*****
Cikin watanni biyu nan papa hankalinsa ba akwanceba sabida kullum haka yakema juhaina hanya hanya akan maganar turowa gashi har yau baisami mafita ba

Fauziyya kuwa tana gidan momcy har yanxu sai bikin khairy da sukaje dambam sukayi sati 1 harda momcy

Auren TJ da kwana biyu juhaina ta kira papa awaya tana masa kuka akan ashe yaudaranta yakeyi ba sonta yakeba tunda gashi rabonsa da zuwa ma sati hudu kenan kullum yace aiki ya masa yawa idan baisontane ya fada mata yafi akan ya ringa yaudararta


Haka da kyar yasamu ya lallameta ta haqura ya kuma mata alqawarin nan da 2weeks zaa zo maganar bikinsu


Yau ya qudiri aniyar komawa wajen daddy akan maganar aurensa da juhaina dan gaskiya baxai iya haqura da itaba


Yamma lis ya nufi gidansu cikin saa ya samu momcy da daddy afalo suna waya da aunty mabarukha akan tace zatazo nan da 1week dan yara sun sami hutun makaranta


Sai da suka qare wayar sannan ya gaidasu adaqile suka amsa dan tun akan maganar fauziyya baya samun fuska

Shima cikin daurewar fuska yace daddy nadawo akan maganar munefa


Daddy ya dubesa yace wanne magana kenan

Maganar auren danace maka ina sonyi ya fada kai tsaye

daddy yace akan baka haqura ba kenan da abinda nafada maka

Yace gaskiya daddy tana sona inasonta to akan me zaa hanani aurenta bayan halal ne ba haramba


Daddy yace toh ai naga bazaka iya riqe mata biyu bane shiyasa tunda guda 1 ma ta gagareka ka riqe

Cikin bushewar ido yace wannan fa ku kuka riqeta agidannan ba ninace tadawo nan da zama ba kuma koma mene ne dai kawai nifa nafada maku aure nakesonyi


Momcy ta dubeshi cikin takaici da mamaki dan batayi zaton rashin kunyarsa da rashin mutuncinsa sunkai nanba

Tace papa ka maimaita abinda kace

Cikin rashin damuwa yace haba momcy, kumafa kun hada abinnan ne batare da neman shawrina ba

Fisabilillahi ina zankai wannan qazamar qaramar yarinyan yar qauye wlh abin kunya ne innunata amatsayin matata, god forbid

Amma ga juhaina wayayya mai ilmi amma kuce baku yabba ba, to nidai nafada maku waccar zabinkuce ba test dina ba so saikusan yadda zakuyi da ita


Momcy takaici da baqin ciki su suka hanata magana


Daddy ya nisa sannan yace naji batunka, amma saika ban takardan sakin fauziyyah sannan na amince da batunka

Kawai daddy na saketa saki 1, shikenan toh yaushe zaajemun KD tambayar?......


โœ๐ŸปFaty Mmn Faty
[3:01PM, 8/19/2017] โ€ช+98 903 074 3573โ€ฌ: ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

August,2017


3โƒฃ7โƒฃ & 3โƒฃ8โƒฃ
Momcy salati kawai takeyi da jin maganganunsa,cikin kuka tace ashe papa har iskancinka yakai haka

Kaje indai matan mazamanine saikayi dana sani

Daddy cikin fushi yace kaje saina nemeka

Papa yace zuwa yaushe kenan daddy

Daddy cikin tsawa yace nace kaje saina nemeka get out i said

Yana fita momcy tasaka kuka tana cewa ka haifi dan yafiqarfinka

Riqota daddy yayi yace haba saudah, meye hakan

Kirabu dashi badai duniyaba, kuma namaki alqawari watarana sai yayi kuka da hawayensa akan Fauziyyah sabida haka ki kwantar da hankalinki sannan nasan aminina zai fahimceni wannan bazai shiga tsakanina dashiba

Share hawayenta tayi tace shikenan Allah ya kyauta yanzun mezamuce wa fauziyyah da iyayenta

Daddy yayi shiru sannan ya nisa yace yanzu muje musameta mukwantar mata da hankali sai mufada mata inyaso gobe insha Allahu zanbar dik abinda nake natafi dambam nasanar da mahaifanta

Momcy cikin jimami tace toh Allah ya kaimu daganan suka nufi dakin fauziyyah


Zaune take tana shirya kayanta acikin akwati wadda aka wanke aka goge mata

Taji sallamar momcy tana amsawa taga daddy ma ya shigo ,dasauri ta miqe sai taji zuciyarta na bugawa ganin daddy har dakinta

Murmushin dole daddy yayi yace aa daugther kiyi zamanki muma zama zamuyi

Komawa qasa tayi ta zauna tana sauraronsu

Shiru sukayi nadan lokaci kafin daddy yayi gyaran murya yace Fauziyyah

Dagowa kanta tayi tace naam daddy

Yace kinsan cewa yana daga cikin rukunnan imani yarda da kaddara alkhairi ko sharri ko

Qirjintane ya tsananta bugawa dakai ta iya amsawa dan sai taji magana ta gagareta

Yace Alhamdulillah ,toh abinda zanfadamaki kidaukeshi kaddarace kuma mai wucewa

Sannan yaci gaba da fadin kwanakin baya Alamin yazomun da wata magana wai yanason yaqara aure

Cikin sauri ta dago kanta tana maimata aure azuciyarta

Daddy yace toh nan nace banyardaba daganan baikuma tada zancenba sai yau dinnan yasake dawowa da maganar

Fauziyyah dai tunani take aranta itakuwa me tayima ya Alamin ya tsaneta har haka baicin yayi watsi da ita baikuma isheshiba har kuma wani maganar aure zai tsiro

Maganar daddy ce ta dawo da ita daga tunanin dake

Yana cewa nikuma nace inhar bazai gaquraba sai dai ya sakeki inyaso yayi auren amma dake dan yaune shine ya furtamun kalmar ya sakeki

Wani razana da tayi yasa momcy tayi saurin riqota

Momcy tace kiyi haquri Fauziyyah tabbas papa ya cutar dake amma Allah zai saka maki kiyi haquri kinji

Shiru tayi batace komaiba sai take ganin kamar amafarkine ko ido biyune

Cikin dauriya tace sagaske kenan ya Alamin ya sakeni momcy tace kansa ya yima kiyi haquri

Aifa nan taji wasu hawaye masu zafi suna mata zarya afuska

Nan su daddy suka ta rarrashinta har suka samu tayi shiru

Washegari ta tashi da matsanancin zazzabi wanda yasa daddy ya fasa zuwa dambam dan tare yake son sutafi da ita

Kwananta biyu da taimakon Allah da rarrashi har suka samu ta sami natsuwa ta kuma dangana tunda har abinci ta karba taci sosai bakaman kwanaki biyun da suka wuceba


Ranan kwana na uku da faruwar alamarin daddy yace fauziyyah ta shirya sutafi dambam


Hakan ko akayi suna isa direct gidansu fauziyyah suka wuce


Agida yasami Abba dan yamasa awaya akan yana tafe

Afalon Abba dik sunyi shiru shida daddy dan maganar tazoma Abba abazata

Cikin damuwa daddy yace wlh nibansanma wacce kalma zanyi amfani da itaba wajen baku haquri

Abba ya nisa yace kada damu nafahimce komai kuma wlh ni bandauki zafi da maganar nanba bakomai Allah yasa haka shiyafi alkhairi ka kwantar da hankalinka aminina maganar yara bazata raba tsakanina da kaiba

Daddy yace nagode nagode Allaha bar zumunci sai dai kuma ina neman alfarma awajenka

Abba yace tsakaninmu kawuci haka fadi komeneneshi inhar baifi qarfinaba

Daddy yace inason nakoma da fauziyyah amma baxata cigaba da zama awajenaba sai nan da wani lokaci kafinnan nacika alqawarin dana daukarma zuciyata

Nan da kwana hudu mabarukha zata zo kuma sati daya kacal zatayi ta koma dan mijinta zaiyi tafiya zuwa Australia

Toh inso sutafi tare da fauziyyah ta koma makaranta acan wajenta

Shiru Abba yayi kafin yace bakomai Allah ya shige mana gaba damacan ai baa gabana takeba

Cikin farinciki daddy yayi tayiwa Abba godia sannan suka shiga ciki ya gaisa da mama

Sannan yafito ya nufi fada akan bayan sallan laasar zai dawo sutafi


Fauziyyah kuwa tun zuwanta mama take kwakwarta akan anya kuwa lfyrta kalau amma haka taqi fada mama maike faruwa dan har yanzun sai tanaga kamar bahaka bane yayane itama dai batasan yadda zata kwatanta abinba

Abbama daya shigo shiru yayi baice komaiba har daddy ya dawo Abba ya kira fauziyyah ya mata nasiha sosai sannan yace kuma tare zasu koma da daddy

Harga Allah ranta baisoba amma haka ta haqura ta bishi

Bayan suntafi sannan Abba ya mayarma mama abinda ya faru

Nan mama tace batasan zancenba ita atafam saidai adawo mata da yarta tunda abin walaqancine

Ita dama tajima jikinta yana bata ba lafy fauziyyah takeba

Da kyar da nasiha Abba yashawo kanta ta haqura dan yasan zuciyar iyaye mata da rauni take shiyasa bai fada mata ba sai bayan sun tafi ya kuma godema Allah daya bashi ya mai jin maganarsa


Bayan dawowarsu fauziyyah da kwana hudu aunty mabarukha ta zo bauchi ita da yaranta uku dik maza


Ranta ya matuqar baci da taji labarin abinda ya faru

Daddy yace sabida haka nakeso kitafi da fauziyyah wajenki kisama mata makaranta ta koma daga naira 1 zuwa biliyan 1 zan kashe dan fauziyyah tasami ingantaccen ilmi

Aunty mabarukha tace tace insha Allahu daddy namaka alqawarin kula da fauziyyah yadda ko kai idan kaganta sai kasan lalle mace ce mai ilmi

Kuma gashi dama yanzun ne zaa koma first term so kafin hutun ya qare zaa sama mata lesson teacher

Shikuma yaje Allah ya shiryeshi amma saiya ga sakayyah

Cikin jin daddy yace haka nakeso Allah ya taimakemu

Momcy ta shigo nan suka cigaba da tattunawa


Sannan ta kira fauziyyah tafada mata tare da aunty mabarukha zasu tafi

Taji dadin hakan dan gaba daya zaman bauchi ya fita aranta


Ana gobe zasu tafi taroqi momcy tabarta taje gidan aunty niima da kuma gidan khairy

Momcy tace sai dai driver yakaiki gidan khairy amma niima kanma zataxo anjima

Sai dayamma sannan ta shirya ta tafi gidan khairy


Agida tasamu TJ sai taji kamar ta koma dan bata qaunar abinda zai kuma hadata da ya Alamin so dataga TJ sai taga kamar tare data gansu

Bayan sun gaisa TJ yace ashe abinda yafaru kenan Allah yasa haka shiyafi alkhairi amma gaskiya Dr bai kyautaba sam

Murmushi tayi tace lah bakomaifa nihakanma yafimun

TJ yace idan da rabo saiku sasanta kuma shimuke fata

Fauziyyah tace hmmm kaidai mubar maganan nan kawai kada na furta abunda ba kyau

Shiryawa yayi ya fice nan yabarsu da khairy suna tada abinda ya wuce

Sai gab da magriba driver ya dawo daukarta

Sai anan take fadama khairy tazo mata sallama ne amma ta roqeta ko mujinta kada tafadawa gashi gashi

Khairy tamata fatan alkhairy ta rakota har bakin mota sannan ta tafi


Washegari sukabi jirgi sai birnin tarayya Abuja


*****
*2weeks later*
Papa yana kwance yana tunanin sati biyun da yayima juhaina alqawari ya cika kuma har yau daddy bai nemeshiba sai yaji qarar wayarsa

Sai daya tashi zaune ganin sunan maikiransa amma haka ya bude idanunsa da toka ya dau wayar yana cewa

Barka da yamma Abba

Yawwa Alamin ya aiki

Yace lfy lau Abba

Abba yace batun yarinyar da kake so nakira inji awanne gari ko unguwa take dan insha Allahu jibi zamuje maka tambayar

Dik iskancinsa dayaji kunya ta kamashi cikin sanyin murya yace akaduna take

Abba yace toh inyaso kashirya gobe zamu shigo bauchi nida Alhaji Sabo qanin daddyne inyaso jibin sai mu wuce tare dakai harda daddynma

Toh nagode Abba Allah ya qara girma


Abba yace bakomai nan sukayi sallama ya kashe wayar kuma yayi hakane dan jin irin furucin da daddy yayi akan shi baruwansa da wannan auren

Da kyar su Abba suka shawo kan daddy ya amince suka tafi kaduna tare

Atare da papa suka tafi kaduna kuma anmasu tarba ta mutunci nan suka tsaida magana maganar aure nan da wata 1 kacal dan ko wani fanni ashirye suke

Papa da juhaina suna zaune acikin garden din gidansu juhaina ta dubi papa cikin shagwaba tace my king

Naama my queen ya amsa

Tace umm ya maganar dakace kowa gidansa da banne ko inace bakacanzaba

Murmushi yayi ya riqo hannunta yana duban idanunta yace ki kwantar da hankalinki Alamin nakine kekadanki

Cikin rashin fahimta tace kamarya likitana fahimtar dani bakacemun kanada mata ba


Yes amma dakenan yanzu single nake cos na yanka mata red card nata so kinga ni nakine ke kadanki


Nan taji wani dadi ya mamayeta koba komai yanzu aikin dake gabanta ya ragu sai dai tayi qoqarin ganin bai dawo da itaba dan gaskiya batajin zata iya zama da Dr Alamin tana ganinsa da wata mata.....


โœ๐ŸปFaty Mmn Faty
[3:01PM, 8/19/2017] โ€ช+98 903 074 3573โ€ฌ: ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ


Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€

Written by Faty Mmn Faty

August, 2017


3โƒฃ9โƒฃ
Washegari dasafe suka biyo jirgi suka dawo bh

Gida papa ya wuce dan Abdu yazo daukarsa

Bayan yayi wanka ya kwanta dan ya huta amma sai da yajima yana waya da queen nasa kafin yayi bacci

Bashi ya tashiba sai wajen5 tukunna

Cikin sauri ya gabatar da sallan laasar sannan kira TJ awaya ya sanar masa yana zuwa gidansa anjima kadan

Sake wanka yayi ya shirya tsaf abinsa ya nufi gidan TJ

Afalo yasamesa shida amarya suna zaune suna kallon wani film a setlite

Fiskannan ba yabo ba fallasa ya qaraso ya zauna

Nan suka kashe hannu

TJ yana cewa ashe kana kusa kenan mutumin

Yace no inafa gida nakira ka kawai dai ban biya ko ina bane

Khairy ce tace ina yini ya Alamin

Lfy lau ya amsa mata

Tashi tayi ta fice kitche ta kawo masa ruwa da juice ,tana ajiyewa ta juya abinta daki dan ita haushi papa yake bata ko yaushe fiska kamar an aiko masa da saqon mutuwa


Ya hanya toh TJ ya tambayesa

Umm normal fa kuma albishirinka

Toh goro fari tass ma kuwa

Papa yace anfa tsaida magana nan da 1 months juhaina tazama mallakina

Kashe hannu sukayi TJ yace shege mutumina kace kawai komai ya kankama

Atare sukayi dariya papa yace kai dai yanzu kawai shiri zamu fara dan kasan dole muyi party kalakala sabida baqin da zasu zo

TJ yace tabbas yanzu dai muje kaci abinci dan nasan kyar inkayi lunch ma inyaso sai muduba muga yadda abin zai kasance dan bama da enough time

Papa yace wlh kuwa kaman zanbiya Eatry sai nace barindai fara zuwa nan sai mufita tare

TJ yace ai zanci abinci saiga wayarka nace toh barin bari saika zo sai muci

Ok muje to,dinning suka qarisa

Ya bubbude masu wamers yace bismillah Dr

Aroma ne yaji ya bugi hancinsa ga kuma ya birgesa a ido nan yadauki plate ya debi white rice wadda taji vegetables da chips sai stew wadda tasha naman dajajatun

Spoon 1 yakai bakinsa yaji abincin yamasa 100๐Ÿ’ฏ

Shiru yayi kawai yanacin abincin dan har yamafi na resturant dayake zuwa cin abinci

Gagara haqura yayi yace man wai a ina kuka sami mai aiki wadda ta iya girki haka

Murmushi TJ yayi yace haba wuce nan nayi aure kuma nazo inacin abincin mai girki never

Papa cikin mamaki yace kana nufin wife nakace tayi wannan girkin

TJ yace yeah itace dan bamuma da mai aiki agidannan komai ita takeyi

Shiru papa yayi yana tunanin wannan yarinyan itace ta iya abinci haka sannan gidan ko ina tsaf sai qamshi kawai , da atunaninsa mai aikice ta gyara gidan dan wannan tayi qanqanta tayi haka sannan kuma yar qauye inama tasan wani gyara haka

Maganar TJ ce ta katse masa tunani yana cewa aikasan Allah nifa kullum sake godema Allah nakeyi

Dan wlh bani da matsalar komai , gata da haquri ga tsafta dik abinda dik abinda nakeso shitakemun

Shiyasa na shafama kaina ruwa na tattara dik wata sabga nafakata a gefe dan wlh yadda yarinyarnan takemun biyayya har kunya nakeji tasan halayena nada kuma kullum inaroqon Allah ya yafemun zunubaina dan da dan hali nane bazan samu ta gariba

Papa yayi shiru yana sauraronsa axuciyarsa yace lalle ashe shima zai more tinda wadda ya auri qaramar yarinya ma gashi dik ya canza sabida kwanciyar hankali baran shida matarsa wayayya wadda ta mallaki hankalin kanta

Nidai Mmn Faty nace lalle dasauranka papa dan abin badaga nan takeba wai andanne ma bodari kai

Suna cikin hiransu wayar daddy ta shigo masa

Hello daddy yafada bayan ya dau wayar

Inaon ganinka yanzun shine abinda daddy yafada masa ya kashecwayarsa

Alamin ya dubi TJ yace man zan wuce yanzun daddyne ya kira kuma yanason ganina

Ok sai gobe insha Allahu zan shigo gida

Harka fara fita kenan

TJ yace no sai nanda two weeks zanje sayama khairy form din school ne

Tabe baki yayi yace ok saika shigo na wuce

Harbakin mota ya rakashi sannan ya tafi


*****
Daddy da momcy suna zaune afalo inda papa yake gefensu azaune yayi shiru yana sauraron daddy

Alamin ya kira sunansa

Naam daddy ya amsa yana kallon daddy

Daddy yace toh nakirakane dan inmaka godia ka kyauta sosai akan abindakayi

Kaci nasara ko ,great ,welldone amma kasani wannan auren tinda kai kaga zaka iya toh kasani ba nairana ko daya da zai shiga ciki

Saika hada masu lefe sannan ka tanadi wajen ajiye matar dan ina buqatar gidana

Papa yace ok daddy wannan bamatsala bace zaayi komai yadda ya dace shikenan zan iya tafiya

Daddy yace eh kana iya tafiya

Bayan ya fita daddy ya dubi momcy yace saudah anya kuwa yaronnan yana cikin hankalinsa

Momcy tace mekagani


Yace gashi baiko damuwa da fushinmu baran yagane abinda yakeyi ba daidai bane

Momcy tace Alhaji nifa abinda yasa kaga nayi shiru bana magana wlh nafiganin laifinmu akan na papa

Daddy yace kamar ya laifinmu kuma

Tace toh icce tun yana qarami ake tankwarashi amma mu dik abinda papa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login