Showing 18001 words to 21000 words out of 144367 words
”
Kaltum ta gigixa kai tayi dan murmushi ta ci gaba da cewa “daddy shine tamkar uwata, ubana, kuma abokina. Shi kadai yake goge min hawaye a idona saboda a kasance koda yaushe ina cikin kuka a sanadiyar kyarar da mahaifana da kuma mamar mushkur ke yi min, tatsane ni saboda taga mijinta yana tarairayarta fiye da dansu na cikinsu.”
Madina ta girgixa kanta t ace “Allah sarki duniya, abun al’ajabi baya karewa ban tabajin irin wannan kauyenci ba. Daga kanki ba’a kara haihuwa ba a gidan ku? Mushkur ma ba’a hqifa masa kanne ba? ”
Kaltum tace “an haifawa mushkur kanne biyu amma dukkansu ba’a haifesu da rai ba, saura kiris mamarsa ta rasa ranta a garin haihuwarsu. Saboda duk a juye ake fitar mata dasu ta hanyar tiyata ma’ana kan jaririn ne suke komawa kirjinta, kafafuwan a kasa sai anyi tiyata ake fitar mata kuma a mace don haka nema aka juyar da mahaifarta baxata sake haihuwa ba. Ni kuwa mahaifiyata ta haifi namiji mai bina ya rasu bayan an yi suna, sai ta dade bata haihu ba sai daga baya ne haihuwar ta bude, kusan duk shekara sai ta haihu, a yanxu haka kannena bakwai na baro mata da maxa.”
Madina t ace “suma kannen naki suna jin kunyarsu basa kula su kamar yadda suke yi miki!” kaltum ta girgixa kai tace “iyayena suna son su, suna wasa dasu, suna hira dasu ba kamar yadda suke yi min ba har tsayawa nake ina kallonsu ina mamakin ashe mama da baba sun iya yiwa da wasa da lallashi.
Duk wani abu da ake bukata na makaranta sai na jira daddy ya xo sannan in fada masa, ya bani in kai makaranta idan kuwa baya gari ko baya kasar sai dai idan kashe ni xa’a yi a makaranta don duka amma babu wanda nake iya tara in fadawa sai daddy.
Ina shekara takwas nagama nursery har na shiga primary, ina primary 3 a lokacin ne karshen karatuna ya xo.”
“kamar yaya karshen karatunki ya xo? ”
madina ta tambaya cike da damuwa.
Kaltum t ace “eh, a lokacin ne goggo fattu ta aiko tana son ganin mahaifina, yana rawar jiki ya tafi kiranta a can garin mu xangon daura. Ta sanar masa abun da take bukata daga gare shi, gashi baya iya yi mata musu. Nan danan ya amsa mata ba tare da yayi kokonto ba saboda tsoro.”
Madina ta gyara xama t ace “me take bukata a gare shi!”
Kaltum ta cije baki tayi murmushin karfin hali t ace “ce masa tayi ya amince ta sayar da gadonsa da mahaifinsa ya bar masa sannan da tabkekiyar gonarsa dake garin sandamu, wacce mahaifiyarsa ta mutu ta bar masa, sannan da dinbin awakinsa xata biya kudin jirgi ni da ita mu tafi makka neman kudi. Idan muka je xa mu samo dukiya mai yawa , sai ta biya shi linkin ba linkin in kudin gonarsa.”
Madina tace “ya yarda a cire ki daga makaranta ku tafi maka? ”
kaltum t ace “a take ya yarda, haka mahaifiyata ma bata hana ba a sanda ya sanar mata. Ko da wasa babu wanda ya fada min shirye-shiryensu, ni dai nasan ankai ni gidan daukar hoto an yi min kananan hotuna, goggo fattu ta xo ta kwana biyu a gidan mu, sai kuma ranar da naga mahaifiyata ta xuba min kayana a dan buhu, goggo fattu tace in taho mu tafi.”
Madina tace “daddy ya sani bai hana a tafi da ke ba? ”
Kaltum ta girgixa kai tace ‘sai da suka ga daddy baya na sannan suka tarki tafiyar, koda wasu basu shawarce shi ba, matarsa ma bata sani ba.
Na tsinci kai na a cikin jirgi, sannan na tsinci kai na a cikin birnin makka.
Madina t ace ‘ki ce kin taba xuwa makka ba wannan ne xuwanki na farko ba? ”
Kaltum t ace”na dade a makka a can na koyi larabci, yanxu haka lungu-lungu da sako-sako na sani a cikin garin makka, haka da ace na samu xuwa xaki yi mamakin irin mutanen da xa ki ga sun sanni duk da na girma nasan xasu shaida ni saboda kammanina basu canxa ba.”
Madina tace”yaya xamanku da goggo fattu ya kasance a maka?
Amma dai bata wahalar dake ba tunda kin girma ba kamar sanda ta yeye ki ba, ga ku kuma a kasa mai tsarki, gashi komai a wadace ba’a wahalar abinci”
Kaltum tayi jugum can ta nisa t ace “uhum wahala ma daya kenan, ai ba xai yiwu in iya xayyana ta gaba daya ba saboda axabar tayi yawa.
Wahalar da na saha ina ‘yar jaririya ai karama ce saboda tsana bansan komai ba, a wannan lokacin kuwa nasan “eh” nasan a’a, na san ace in yi abu in yi, ace in bari in bari.
Da farko dai mun ci sa’a mun sami gidan haya a unguwar ‘yan kasa wato a unguwar masfala, a gidan wata balarabiya mai suna hajiya isra, hajja isra ruwa biyu ce mahaifiyarta baka, mahaifinta balaraben makka ne dan haka gadimiya ce. Hajja isra tana da ‘ya daya mai suna ahlan. Ahlan sa’ata ce, mahaifin ahlan ya rasu ya bar musu gida sama da kasa. Suna xaune a sama, mu kuma muna haya a kasa mu kadai ne.
Hajja isra tana da kirki matuka,tana sona sosai musamman yadda taga mun shaku da ‘yarta Ahlan, har ana cewa muna kama kasancewar Ahlan tayi kama da mahaifiyarta ba suyi kama da larabawa ba sak nima kuma gani fara sol mai gashi sai nake kama dasu. Ta kan yiwa goggo fattu wasa t ace “yadda fuskar nan taki take baka kirin idan askarawa (yan sanda) suka ganki da kaltum ki ka ce jikarki ce sai sun kama ki, suce karya ki ke ‘yar larabawa kika sato. Saboda baku yi kama ba kwata-kwata, gara ki dinga saka nikaf da safar hannu da ta kafa idan xaku fita tare.
In da xaki tabbatar hajja isra na sona sai ta siyawa ‘yarta ruguna ko sarka da ‘yankunne na gwal, biyu take saya iri daya ni da Ahlan musamman a lokacin sallah. Haka abinci, komai ta dafa sai ta aiko min sai dai kash aiken baya xuwa gare ni saboda goggo fattu karbewa take yi bata bani. Da takardar Ahlan ta ‘yan kasa hajja isra ta saka ni a makarantarsu Ahlan, muke xuwa tare duk da ba’a koyar da boko larabci xalla ake yi sai karatun qur’ani ta tahfix ce. Na koyi larabci, na koyi karatun qur’ani sosai, nasan baki, hadisai da daman na haddace su kuma xan iya fassarawa, haka fikihu, tafsir, sira da sauransu. Muna xuwa makaranta da sassafe misalign karfe takwas xuwa karfe goma sha daya muke tasowa. Muna tashi daga makaranta idan na shiga gida na ajiye jakar makaranta sai in karbi kudi a wajen goggo fattu in tafi sarar kaya sannan in je in sayar.”
Madina tace “ban fahimce ki ba. Ke kadai din ne xaki iya xuwa ki sari kaya da kanki? ”
Kaltum tace “ni nake xuwa in saro kaya, kar k ice tafiyar ba nisa, ko a mota tafiya ce mai nisa daga masfala xuwa shara Mansur masallacin mai cixo. Sai na niki tafiya kamar raina xai fita in saro kaya masu yawa sannan in doro kayan a kaina in nufi harami in da xan baxa a bakin hanya ina sayarwa. Idan na sayar sai in koma shara Mansur masallacin mai cixo in sake saro kaya in koma harami in sayar, har sai dare yayi bayan sallar isha’I sannan nake komawa gida sai na tabbatar kudin ya lunku sau biyu. Ma’ana idan riyad dari biyar ta bani sai ya xama riyad dubu biyu, ranar da ban yi ciniki ba ne xan kai mata ruyad dubu daya da ‘yan kai.”....
.
Gida fa ya fara shiru, mai yasa aka rage
ADON DAWA 8
.
Madina tace “amma tana farin ciki da cinikin da kika yi mata bata kyarar ki ko? ”
Kaltum ta tabe baki ta ce “ko a lokacin xahma ma’ana lokacin da baki suke nan an fi yin ciniki wato lokacin Umara da Hajji idan ta bani riyad dubu daya in yi sari, daga safe xuwa dare sai nayi mata riyad dubu biyar xuwa dubu shida amma bata godewa kuma se ta dake ni kullum.”
Madina tace “to cnikin nawa take so kiyi mata? ”
Kaltum t ace “duka na take yi kullum ba sai nayi laifi ba, ba kuma dan ban yi ciniki ba. Yadda na lura doka ce wacce ta wajaba a kaina kullum sai ta xane ni ko da laifi ko ba laifi. Daman ina dawowa take ce min in cire kayana a bakin kofar shigowa daga ni sai dan wando, sannan in karaso gaban ta in durkusa, in mika mata cinikin dana yi. Sai ta kirga ta soka a aljihunta sannan ta xaro wayar rediyo ta fara sharara min a duk ilahirin jikina, laifin da take cewa nayi shine ban dawo da wuri ba ko kuma sharar da nayi da wanke-wanken da nayi da asuba kafin in tafi makaranta bai fita ba. In yi ta kuka da ihu ina mata magiya tayi hakuri ba xan sake ba. Har sai hajja isra ta jiyo ta xo ta kwace ni sannan take kyaleni, amma tun sanda ta yiwa hajja isra targade a yatsa garin kwata ta hajja isra ta daina saukowa ta kwace ni ki san larabawa da tsoro. Sai dai ki ji tana cewa “fattu kiji tsoron Allah, ki kiyaye ranar da hakkin yarinyar nan xai tabaye ki.” Amma goggo fattu bata ji, gobe ma xatayi min wanda yafi na yau.”
Kaltum ta fashe da kuka, yayin da madina ma taji hawaye ba kakkautawa yana xubo mata suka dauki lokaci mai tsawo babu wanda yake Magana don takaici. Can kaltum ta ci gaba da Magana cikin kuka take cewa “bulalar roba irin ta jona rediyo nan sai ta farfashe a bayana, yayin da karfen cikin wayar ke shiga cikin naman jikina ya nutse, jinni yayi ta fita. Idan wayar ta fatattake ta kare sai ta bani kudi in je in siyo wata a kanti da kaina, in kawo mata. Idan itama ta kare sai ta sake aikena in siyo wata.”
Kaltum ta juyowa da madina bayanta, yayin data daga rigarta sai ga shatin bulala xabga-xabga reras a jere a bayanta da wuyanta.
Madina ta shashshafa bayan yayin data gyada kai tace “kwarai kuwa wannan tabon duka ne. Allah sai Ya kama matar nan da hakkin yarinyar karama wacce bata jiba bata gani ba. Ta rabo ki da iyayenki ta xo ta axabtar da ke.”
Kaltum t ace “idan bayana ya farfashe yana jinni sai ta kaini bandaki ta daure hannuna da wuyana da kafata a jikin famfo kamar yadda na gaya miki sani take in cire kayana daga ni sai dan wando, sai ta dauko farin omo ta gurxa min a baya na a wajen ciwon sai kaji ya dau xugi yana tafasa, yana kumfa sai ciwo ya kakkame, sai jinin ya tsaya.”
Madina tace “ta daure ki a bandaki fa kika ce, kamar wata dabba?
Ko dabbace xatayi mata haka? ”
Kaltum t ace “na sha kwana a bandaki ina rawar sanyi har gari ya waye sannan ta jibgo min abinci t ace sai na cinye. Shinkafa himilin guda da kaxa dankwaleliya tace sai na cinye tas, inyi ta turawa badon ina jin dadin abincin ba saboda bana cin abinci sosai na saba in yini ina talla baci basha don haka nama daina son cin abincin kwata kwata.
Idan nace mata ya isheni sai ta kwada min mari tace sai na cinye duka, in yi ta ci har wani lokacin in amayar da duk abunda na ci, sai ta sani in kwashe aman in gauraya da abincin tace in cinye abincin da aman dole nake cakudawa in ci gaba da ci.”
Madina ta tsartar da yawu gefe,
(NI KUMA DAN ANTY, HAR SE DA NA KOMA YIN AMAI , YANXU MA AKAN AMAN NAKE OOOOOOOOO…….)
Ta dau dogon salati. Ta ce “kaltum kin sha wuya, kai wannan abu da me yayi kama?
Ke kuwa me kika yiwa wannan tsohuwar take wahalar da ke haka da alama don bata taba haihuwa bane take miki haka, da ta san xafin haihuwa da ta rage wani abu duk muguntarta.”
(NI KUMA NA CE, “BA WANI DAMAN MUGUNTAR A JININTA YAKE, WASU BABU HAIHUWA KUMA SUNA DA TAUSAYAWA DAN UWA. ALLAH MA YA TSARE MU DA IRIN WANNAN RASHIN IMANI. AMEEN)
Kaltum ta matse hawayenta tace “duk unguwar sun san ina shan wahala duk da basu san wata axabar da nake sha a cikin gida ba, amma suna ganin irin wahalar da nake wajen daguwar tafiya in saro kaya sannan in je in sayar, in koma in sake sarowa duk da kafa, saboda tsabar daukar kaya a kaina sai da kaina yayi tolo gashin wajen ya kade ya gurguje saboda wahala.
Akwai wani yaro saurayi a makwabtanmu mai suna Anwar. Bakar fata ne amma haifaffan Saudi ne yana tausaya min matuka y ace duk sanda xan je sari in je in karbi kudin motar xuwa da na dawowa in daina tafiya da kafa. Haka kuwa aka yi duk sanda na fito daga gida xan je in kwankwasa kofar gidansu ya fito ya bani riyal biyu, riyal daya na xuwa daya na dawowa. Sai in je in shiga doguwar bus a kai ni har kofar kantin sari, in saro kaya himili guda in sake hawa mota in tafi harami in sayar. Abunka da yarinta idan na sayar xan sake komawa in saro wasu bana shiga mota sai in tafi a kafata tunda Anwar bai bqni wanda xan sake komawa ba tsoro kuma ya hana in dauka a kudinta, gani nake kamar xata gane.
Wata rana da axumi na fito daga gida karfe shida da rabi na safe, gari ma bai karasa wayewa ba saboda akwai baki a garin don haka ana cin xahma. Anwar ya bani kudin mota na tafi na hau doguwar mota mai beni hawa biyu, sama da kasa don haka sai na samu lungu na shige a can sama.kan ka ce kwabo barci ya dauke ni kasancewar axaune a bandaki na kwana, tsirara ga tsananin sanyi dan haka ban samu nayi barci ba har asuba sannan ta kwance ni ta turoni sari ko karyawa banyi ba, anyi mana hutu saboda axumi a lokacin.
Ina wannan barci har aka wuce dani inda xan sauka ban sani ba. Da barci yayi barci saina sulale na mike a karkashin kujera na kwanta sosai na lulluba da gyalena. Ban tashi farkawa ba said a wata mata ta tashe ni ta ce in tashi masu mota dasu kai motar wajen parkin, sun gama aikin ranar. Sannan nayi firgigit na biyo bayanta muka sakko tare da ita. Ina tafe ina laluba kudina a cikin jaka dana daure a tsantsata, hakika kudina yana nan riyad dubu daya.
Ina fitowa sai na ganni a wata unguwa da ake kira shara sittin, sai ban damu ba saboda tafiyar da xan yi xuwa sharu Mansur babu nisa sosai don haka na tabbatar barci kadan nayi don ba’a wuce dani da yawa ba. Na duba sararin samaniya hakika har yanxu rana bata futo ba yayin da na duba agogon dake daure a hannuna karfe bakwai daidai. Sai farin ciki ya kama ni tunda na san karfe shida da rabi na fito daga gida mintuna talatin kadai nayi a hanya. Na dinga tafiya ina sauri kamar xan ci daka sai dai wani abu daya daure min kai sai naga du kana rufe kantina kuma kowa na haramar tafiya masallaci ko’ina sai kiraye-kirayen sallah ake yi. Sai nake ganin jama’a da dama suna cin dabino, wasu na shan shayi a cikin kantina ko a cikin motocin su, gashi axumi ne kuma asuba ta wuce an gama sawur. Na tambayi xuciyata me yasa suke karya axumin su?
Tambayoyi kala-kala na dinga yiwa kaina har na isa kantin sari. Mutum daya na iske yana alwala a bakin kantin. Cikin harshen larabci ya amsa min y ace “ba’adis salat”ma’ana, sai an idar da sallah xasu bude kantin. Na dube shi duba na rashin fahimta n ace “ba kuyi sallar asuba da wuri ba ne? ”
ya yi dariya yace sallar magariba xa mu yi ba dai asuba ba. Ko dan bakya axumi shi yasa baki damu a sha ruwa da wuri ba ko?
Sai gabana ya yanke ya fadi, nan da nan na rikice. Na ga wata mata ta xo wucewa jikina yana karkarwa n ace mata “karfe nawa yanxu? ” ta duba agogon dake daure a hannunta t ace “karfe bakwai.” Na tambaye ta “bakwai na safe ko bakwai na dare? ” itama sai tayi dariya sannan t ace “bakwai na dare ne. ba ki ga ana shan ruwa ba? ”
Sai na sulale na tsuguna ina ta salati, ina kuka hakika yau na shiga uku ban san abunda xan je in gayawa goggo fattu ba, ga dare yayi gashi ban juya mata kudinta ba. Ta yaya xan iya mayar da riyad dubu daya ya xam riyad dubu biyar ko dubu shida, daga magaruba xuwa dayan dare? Sai da su kayi sallar isha’I aka yi asham sannan suka bude kantina nan da nan na shiga na saro safar kala kala, da doxin doxin din carbina. Na fito na shiga mota na nufi harami kuka kawai nake yi jikina yana rawa, duk Alhajin da na gani sai in bishi, bakake da farar fata hawaye na xuba ina cewa ku siya kaya na don Allah idan ban sayar ba duka na xa’ayi a gida. Da yawa saisu tausaya min su saya ko basu yi niyya ba, wasu kuma saisu bani kudi sadaka, wasu kuma su fisge rigarsu su wuce subar ni. Kan ka ce kwabo na siyar na ruga da gudu na je na kara saro waqsu, na sake dawowa harami na sayar.
Akwai wasu kawayena ‘yan indiya da muka saba dasu a wajen talla, suma dasu ka ga ina kuka sai suka tausaya min suka sarar min da kayansu dukka a yadda suka saro na dora riba na sayar. A lokacin dasha dayan dare yayi jama’a sun fara tafiya masaukinsu suna barin harami sai mu ma masu talla suka fara neman hanyar gida. Ina tafe ina kirga kudin cinikin da na yi, saura kadan ya cika riyal dubu uku, sai na dinga kuka ina addu’a yayin da hankalina ya kada yayi gida ina tunanin