Showing 6001 words to 9000 words out of 144367 words
kungiya suna sha’aninsu wasu suna caca, wasu kuwa suna hira suna shan jabna, yayinda wasu suke saye da sayarwasu. Kaltum na fara bara sai ta ci sa’a duk rumfar da tayi bara sai a miko mata sadakar wahid jine wato kamar kandala, farin ciki ya lullube xuciyar kaltum don ada ta shiga wani mawuyancin hali tana tunanin yadda xata yi in har bata samu ko kwabo ba idan ta je gida xasu kusa cinyeta da baki bayan wulakancin kala kala.
Ta ci gaba da bara harta karkashin wata inuwa inda dandaxon samari ne xalla, sun shinfida katuwar tabarma suna ta shan jabna suna caca. Sun kaisu goma sha biyu dukkanninsu shekarunsu basu wuce ashirin da biyar xuwa ashirin da bakwai ba. Shewa da ihu kawai suke yi da alama basu da matsala a rayuwa. gasu a kauye, a cikin gidajen katako da katangar kaya yayin da suturar jikinsu bakin yadi ne mai layi layin fari wacce suke dinka ‘yar shara da wando iyaka guiwa amma koda yaushe sai kaga suna farin ciki ko me yasa. Kaltum take xayyanowa aranta sannan ta bawa kanta amsa “tabbas dole suyi farin ciki a rayuwarsu saboda suna tare da iyayen su, a garinsu, kuma ga dukiyoyinsu” ta katse tunanin da take yi da ta ji suna tambayarta “lafiya, me kike nema a wajenmu!”
Tayi firgigit t ace “karama fi sabilillahi.” Kalma daya ta ji wani daga cikinsu ya fada a cikin yarensu sai taga dukkaninsu sun waiwayo sun kalleta a lokaci guda. Ta yi sauri ta sunkuyar da kanta kasa, da tadago taga har yanxu suna kallonta, sai ta sa gefen gyalenta ta rufe da fuskarta. Daga karshe ta yanke shawarar gaggauta barin wajen tun kafin su iskance ta.
Cikin harshen larabci daya daga cikinsu yace ta xo, kasancewar tana jin larabci sosai tun tana karama sai ta juyo ta dawo wajensu a nutse cikin ladabi amma fa duba daya xaka yi mata ka tabbatar a tsorace take. Ya dubeta sama da kasa duba irin na kurulla yayi dariya ya shafa baki don haka kaltum ta fara fuskantar manufar kiranta da yayi, sai ta fara ja da baya.
To pa, ko ya data kasance tsakanin kaltum da en samarinnan!
Sai ku biyo mu dan jin yadda xata kaya
ADON DAWA 4
Ya fada cikin shagobe “ke me kyau, yaya sunanki!”
Ta na mkyarkyata tace “kaltum”
Su dukka suka maimaita sunan “kaltum” a lokaci guda suka ci gaba da dubanta suna kwada kyawunta, suna mamakin kyawunta don basu xata akwai masu kyau a cikin bakin almajiran nan ba saboda sun dauke su wulakanttatun bayi.
Daya daga cikin su ya dubi shugaban tawagar mai suna Mambela wanda har yanxu bai ce komi ba sai duban kaltum yake yi kasa kasa.
Cikin yarensu yake Magana yace “ranka ya dade shugabana mambela kai ka dace da kyakkawar halittar nan, du da de ba niman mata kake ba, lallai tana da kyau kuma ta hadu. Ya kamata a mika maka ita cikin shagon nan kawai in ka gama sai ka bata alif jine (dubu daya) ka ga sai tayi sati tana cin abinci, gobe xa ka ga ta dawo da kanta.”
Duk da cewar a cikin yarensu ya yi Magana bata ji duk abubuwanda yake fada ba amma ta fuskanci abunda yake fada, don haka sai ta juya da sauri ta fara tafiya. Mambela yace “tabbas yarinyar na ta dace da ni don haka ku dauko min ita, ku shigar min da ita cikin shagon nan.” Ba tare da bata lokaci ba kartai hudu suka bi ta da gudu suka damkota cak suka daga ta kamar kaxa suka nufo inda mambela ke xaune. Tuni robar bararta da yan kudaden data samu suka waste a kasa, ta kurma ihu kai kace rai ake xare mata.
Cikin kuka tace “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un. Laa ilaha illa anta subhana inni kuntu minaxxawalimin.”
Mambela yace su ajiyeta kasa a gabansa yayin da ta xabura da gudu sai ya damki hannunta ya fada cike da damuwa cikin harshen larabci.
Ya ce”kaltum bkya son kudi ne! bakya son mambela dan sarki, mai kudi da dukiya!”
Ta fada cikin firgicewa da kuka mai tsanani .
“eh, bana so.”
Ya yi murmushi cikin mulki da kasaita y ace “amma ni na ji ina sonki, so mai dinbin yawa kuwa. Yaya xa’a yi ken an!”
Abokansa suka fada cikin fusata “ka bamu ixini mu shigar maka da ita ciki kawai, ka gama da ita mu ma idan ka gama ka bamu sauran, tunda bata da gata a kasar nan waye xai tsaya mata.”
Mambela ya mike tsaye cak yana duban kaltum dake tsugunne a gabansa har yanxu kuka take, gardawan kacokan sun xagayeta babu hudar da xata samu ta arce . mambela ya dade a tsaye yana dubanta daga shi sai mahaliccinsa ya san abunda yake aiyanawa a ransa. Can ya dago ya dubi yaransa daya bayan daya sai yayi murmushi da kyakkyawar fuskar nan tasa, sannan ya yi musu nuni da hannu ko bai furta ba su sun fahimci abunda yake nufi nan da nan suka fara aiwatar da abunda ya umurcesu dasu yi domin ba’a yiwa mambela musu a garin.
Kartai uku ne suka damko ta suna kokarin shiga da ita shago. Ta kurma ihu ta ci gaba da kiran “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un.”
Muryar wani tsoho ne suka ji a bayansu ya fada cikin yarensu, daga dukkan alamu ransa a bace yake, y ace “haba mambela ko sauran ba musulmai ba ne ai kai musulmi ne, ko kunyi niyyar cutar da yarinyar nan albarkacin sunan Allah da take ambata ya kamata ku kyaleta.”
Suka ajiye ta yayin da ta balla da gudu ta je bayan tsohon ta labe, karkarwa kawai take yi. Gyalenta ya dawo wiyanta, kanta babu dankawali sai burtintin kitson da ya tuttuje wanda ya cika da yashi a sanadiyar rashin siminti balle katifa a dakinsu. Tsohon ya juya ya dubi kaltum yayi mata yarensa, sai ta girgixa kai ta yi masa larabci. Ta ce, “bana jin yarenka, larabci nake ji kadai” ya fada cikin harshen larabci “yi hakuri yarinya, daura dankwalinki, goge hawayenki ki tafi gidanku. Ki daina shigowa kasuwa bara wajen maxa ki dinga bararki a cikin gidajen mata ya fi miki alkhairi a matsayinki na yarinya mace budurwa kuma kyakkyawa.”
Ta gyada kai t ace “ nagode, ba xan sake xuwa ba. Baba karaka ni gidanmu tsoro nake ji kada su bini su sake tare ni a hanya.”
Ya ce to muje in raka ki.
Jikinta na karkarwa, hawaye yana kwaranya ta shige gaba tsohon na biye da ita a baya har suka yi nisa.
Mambela ya cije baki ya gyada kai ya dubi abokinsa.
Ya ce “xan jinyata tsohonna idan be daina shiga shirgata ba. Yanxu haka shima idan suka raba daji yaga ba kowa xai iya yi mata lalata, shine mu ya hana mu. Xamu hadu da kaltum wata rana wallahi ba xan hakura da ita ba duk ihunta.”
Abokansa suka ci gaba da xuga shi suna bashi kwarin guiwar gami da daukar masa alkawarin idonsu idon kaltum xa su kamo masa ita.
Har kofar gidansu kaltum tshon nan ya raka ta da gudu ta fada cikin gida ba tare da tayi msa godiya ba saboda a firgice take don tsananin tsoron da ta ke ciki.
Kaltum ta dawo gida da magaruba, kallo daya xaka yi mata ka tabbatar hankalinta a tshe yake ko Magana aka yi mata sai ka ga ta xabura. Babu irin tambayar da ba’a yi mata ba amma amsa daya ta gagara sai hawaye da take xubarwa. Daga ita sai Ubangijinta suka san abunda ya faru amma bata fadawa kowa ba.
Madina ceta ja hannunta tsakargida, suka shafe tsawon sa’a guda tana lallashinta tana bata baki da dubaru iri iri akan ta fadi abunda yake damunta amma kaltum ta ki cewa uffan, sai girgixa kai kawai take yi alamar babu komai. Karshen maganar madina t ace “babu yadda xa’ayi kice babu komi amma kuma kina kuka.”
Ta bata ruwa a buta tace ta yi alwala, ta yi sallah, ta yi addu’a ko me nene ma Allah Ya sawake mata.
Karkarwa hannu kaltum yake yi data dauki buta ta xagaya ban daki, ta fito tana alwala jkinta na rawa, kukan dai bata fasa ba har yanxu. Tana sallah tana sheshekar kuka a bayyane, hankalin madina ya tashi amma sai ta ji haushin kaltum ya kama ta saboda ta ki fada mata matsalarta. Su kuwa su huwaila banda xagi da dungure mata kai babu abunda suke yi suna cewa watakila satar kayan jikinta tayi masu kayan suka doke ta.
Rakiya tace “watakila gidan wasu ta shiga ta satar musu abinci tunda da yunwa ta fita tun jiya bata ci abinci ba.”
Amina t ace, “ko kuma xagin wasu ta yi suka kikkifa mata mari don bata da kunya.”
Iya mairo t ace, “ku kyale ta mana karta fadi abunda yake faruwa tunda bakin hali ne da ita babu mai jin cikinta.”
Kaltum na kudundune a kan kwalinta cikin mayafinta sai kuka take yayin da jikinta yak eta karkarwa. Har kowa y agama cuku cukun kwanciya, aka hure acibal bal wato fitilar da ake cika kwalba da kanaxir ayi lagwani da tsumma.
Duhu ya bayyana a cikin dakin, yayin da gari yayi shiru alamar dare ya tsala, kowane bawa ya kwanta hakarkarinsa kamar yadda masu iya Magana suke cewa dare mahutar bawa. Wannan dare kuwa ya xamarwa kaltum daren jan aiki babba maimakon ta huta sai ma ta tashi tsaye.
Misalign karfe daya na dare kaltum tayi firgigit ta mike tsaye a firgice gami da kwalla ihu mai tsanani tana fadin “wayyo Allah na, ku taimakeni gasu mambela nan xasu kamani.”
Ta tattaka sauran matan dake kwance a tsakiyar dakin burinta kawai ta fice waje da gudu. Gaba daya ‘yan dakin suka tashi a gigice suna riketa, tana bankarewa tana xubar das u sai da ta fita tsakar gida da gudu tana ihu tana fadin.
“su mambela ne xasu kamani, gasu nan xasu kashe ni.”
Madina da jidda’u ne suka bita da gudu suka damko ta suka shigo da ita daki sannan ta dan lafa ko minti biyar ba’ayi bat a sake kwalla ihu ta fice ta gudu. Wannan karon harda iya mairo a masu bin ta da gudu suka cafko ta. Ba ‘yan dakin su kadai ba gaba daya ‘yan sauran dakunan gidan babu wanda ihun kaltum da dawainiyar masu rike ta bai tasa daga barci ba. Kowa ya fito ido luhu luhu saboda barci suna tambayar “me ke damunta!”
“ba mu sani ba.” Amsar da su madina ke bayarwa ken an. Su duka suka kewaye kaltum suna tambaya,
“waye mambela, mutum ko aljan!”
Babu amsa, makyarkyata kawai take yi tana kuka, madina ce mai ilimn kur’ani ita ke tofa mata addu’o’I sannan kaltum tadan lafa harta fara gyangyadi, sannan ta sake firgita ta mike tsaye tana kokarin rugawa da gudu suka damko ta, suka xaunar da ita har yanxu fada take.
“ga mambela nan da abokansa xasu kamani.”
Su dukka sun tausaya mata, kowannensu mata da maxa sai addu’o’I suke tofa mata har saida ta lafa sannan suka koma dakunansu. Wsau suka kwanta amma wasu suna tsaye akanta har saida gari yawaye tangarai sannan kaltum ta sami barci. Sai kowa ya shiga neman ruwan alwala da sauransu.
Kaltum barci take yi haikan mai nauyi wanda bata iya jin duk wani motsi da surutan da ake yi akanta, bata bude ido ba sai karfe biyu na rana. Ta tashi xaune firgigit ta dubi sama da kasa, gefen hagu da damanta sai taga babu kowa sai ita. Ta dinga kokarin tuno komai. Kanta ne yake tsananin ciwo dan haka ta shafe awa guda a xaune ta rasa abunda yake mata dadi. Can ta daure ta yunkura xata tashi sai ta koma jabar ta xauna, ta sake cije baki ta rike katakon ginin dakin ta yunkura da karfi sannan ta mike tsaye. Ta fara tafiya a hankali yayin da kafarta ke xugi a sanadiyar bubbugewar da ta dinga yi jiya. Hakika duk ilahirin jikinta ciwo yake yi musamman kafadar ta saboda ciccibar da abokan mambela da ‘yan dakinsu suka dinga yi wajen jawo ta.
Ta fito tsakar gida ta tsaya ta dubi kowacce kusurwa babu kowa sai ita kadai, ta sake ci gaba da tafiya har saida ta fito kofar gida sannan ta sulale ta xauna a gefen wani kabari ta xura masa ido tana kallo. Sai hawaye ya fara sirnanowa daga idanuwanta, ta fashe da kuka mai tsanani ta fara Magana ita kadai tamkar tababbiya.
Ta ce “a ina nake! Ni wacece! Wa nake da shi a duniya! Me na ke yi a duniya!”
Sai kwakwalwarta ta tuno mata mambela da abokansa a lokacin da suke kokarin ciccibarta xasu shiga da ita wannan shagon, sai ta rushe da kuka. Ta ce “inna lillahi wa’inna ilahi raji’un. Yaya xan yi da rayuwata! Kowa ya tsane ni, kowa baya sona, kowa yana hantara ta, ga kishirwa ga yunwa. Allah Ka dau raina a saka ni a cikin kabari in kwanta in huta in daina ganin kowa, kowa ya daina ganina balle wani ya ji haushina.”
Ta sa hannu ta shafa kabarin ta fada cikin kuka ta tambaya tace “waye a cikin kabarin nan, mace ko namiji! Ina so in xama kamar ku, in mutu kamar yadda kuka mutu. In daina motsi kamar yadda kuka daina, in daina tafiya kamar yadda ku ka daina, in daina bara balle su mambela su kamani.” Yayin da kuka ya ci karfinta ta kasa ci gaba da Magana.
Muryar mai sayar da ruwa ne ya katse ta, ta dago idanuwanta da sauri ta dube shi, sai a lokacin ta tuno tsananin kishirwar da take matukar addabarta. Ta fada cikin wata marainiyar murya “saga dagiga moya hilwa wala murra!” ma’ana mai ruwa tsaya ruwan dadi ne ko na xartsine!
Mai sayar da ruwa ya tsayar da jakunansa ya dubeta yayi murmushi y ace “muya hilwa” ma’ana ruwan dadi ne.”
Ta ci gaba da Magana cikin harshen larabci tace “ka sauke min jarka daya.”
Ya sauko daga kan keken jakinsa da farin ciki yana godiya ya na fadin”Allah Ya yi miki albarka yarinya, kin taimakeni da xaki sayi ruwana yau ko digon ruwa ban siyar ba ban samu ko kwabon da xan yi cefane ba.
Maganar da yayi ya ambaci kudi shi yasa ta tuno dan silillikan data samu jiya da yamma. Sai ta yi sauri ta laluba jikin siket dinta, ta ji ba komai, sai ta tuno ashe sun xube a lokacin da ake ciccibar ta a kasuwa daga kudin har robar bara sun xube. Sai ta ji hankalinta ya tashi ta shiga tunanin abunda xata fada masa. Ya katse tunanin da ta ke yi ya tambaya, “a ina xan juye miki ruwan!”
Sai ta yi firgigit ta dube shi sannan ta sunkuyar da kai kasa, ta sosa keya, ta fada cikin gargadar murya “baba ka yi hakuri ba ni da kudi, ashe kudin ya xube jiya a jim arab. Ko xaka bani kofi daya in sha sadaka saboda Allah kishirwa nake ji.”
Tsoho ya tsuke fuska ya ciccibi jakar ruwansa ya mayar kan jakunansa yah aye, ya kada su suka tafi. Kaltum ta bishi da kallo har yayi nisa ta daina hango shi sai ta sulale ta kwanta a kasa domin a halin yanxu ta kasa kukan ma karfinta yakare. Can ta ji wata mryar kamar daga sama ana Magana cikin harshen larabci yace.
“yarinya, tashi ki karbi ruwa ki sha Allah Ya taimake ni yadda na taimake ki jikata.”
Ta daga ido da sauri sai taga mai sayar da ruwa ne ya dawo . ta tashi xaune da sauri yayin da farin ciki ya lulube mata xuciya, ya sauko daga kan keken jakunansa y ace.
“a ina xan juye miki jarka daya!”
Ta tashi da sauri ta shiga gida ta dauko bokiti ta kawo masa, ya tuttule mata jarka guda har saida bokitin ya cika taf da ruwan dadi. Ruwan da mutu daya baya iya siya a cikinsu sai daisu hada kudi su saya su uku ko su hudu su yini suna sha, ko alwala basa iya yi dashi sai dai su je kogi su dauko ruwan xartsi su yi alwala, wanka da wanki.
Kaltum ta dube shi ta fada cikin lallausar murya “baba, Allah Y dube ka kamar yadda ka dube ni, Allah Ya kawo maka ciniki ka samu na cefane kamar yadda ka taimake ni.”
“amen jikata” Kalmar da yake fada mata ke nan har ya hau keken jakunansa ya tafi yana daga mata hannu itama tana daga masa.
Ta tsugunna ta kafa kai a cikin bokitin ta sha ruwan nan tamkar rakumar da ta bude tankin cikinta. Ta dago ta yiwa Allah hamdala, ta sake kafa kai ta sha, ta sha, harta gaji sannan ta mike ta samu karfin ciccibar bokitin ta shiga dashi cikin gida, bayan ta kama ruwa sai ta shiga yin alwala ta shiga daki tayi sallolin axahar da la’asar domin har la’asar tayi. Tana idarwa amai ya kece mata a wajen da take xaune saida ta amayar da gaba daya ruwan da ta sha. Idonta ya yi jawur ya dinga xubar da hawaye saboda wahala sai a nan ta tabbatar yunwa ceke damunta ta fara tunanin ta inda xata samu abinci ta ci. Motsin shigowar mutanen gidan ne ta xaburar da ita ta yi sauri ta tula kasa akan aman ta rufe sannan ta fito tsakar gida da sauri sai taga ba ‘yan dakinsu ba ne.
Su na ganinta suka fara tambayarta yaya jikinta ta amsa da sauki. Duk da ta shiga rudani bata fahimci sannun da suke yi mata ba . tana tambayar kanta da kanta.’daman ba ni da lafiya! To ciwon me nayi da har ‘yan wasu dakin suke yi min sannu!”
Ta tambayi xaibu ko taga su iya mairo! Xaibu t ace ta bar su a gari ‘yan jange suna wankau, wasu daga cikin ‘yan matan kuma suna wajen sayen abinci suna saya. Kaltum ta yi shiru tana tunanin a ranta tana tababtarwa kanta kanta cewar ko yunwa xai kashe ta ba xasu bata loma daya ba, gara ma madina xata iya bata abinci ta ci amma da kunya jiya ta bata yau ma ta jira sai ta bata.
Xaibu ta katse tunaninta t ace “baki fita bara ba ne yau!”
Kaltum ta gyada kai tace “ban je bara ba saidaI yanxu xan tafi. Ko xaki bani aron robarki in tafi bara tawa ta bata jiya.”
Xaibu ta shiga ta dauko mata roba,