Showing 126001 words to 129000 words out of 144367 words

Chapter 43 - ADON DAWA

Unknown   

30 Oct 2024

5073

daga bakin dunia cewar uwarsu tabar musu abun gori,
kaltum ta toshe bakin Madina gamida zaunar da ita tace aunty Madina kiyi shiru mana da karfi kike magana fa kada mutane su shigo su dauka wani abu ne.
madina ta rushe da kuka tace kaltum dole ne in godewa Ubangijina domin Ya amsa addu'ata dana dade inayi, farin cikin da nake yi ba dan in auri Abba ba sai don Allah Ya taimakeni Abba bai mutu asanadiyyata ba ya
warke ya tashi daram na tabbata zai yi musu bayanin duk abunda ya faru na gaskiya, Allah Ya wankeni 'yayana zasu huta da gori shine kadai fatana daman,
kaltum tace kwarai Abba yayi musu bayani sun gamsu sunyi nadama sun bazama nemanki don sunemi gafararki basu sameki ba dole tasa suka hakura,
Madina ta mike da sauri ta ce tashi ki rakani gidan su Abba,
kaltum tace ki bari gobe ko anjima kici abinci tukunna har a gama,
Madina ta girgiza kai tace bazan iya kara awa guda ba banje naga Abba da 'yayana ba, kafin kaltum tace wani abu Madina ta suri akwatin kayanta ta fice tsakar gida don haka kaltum ta dubi goggo Fattu wacce har yanzuke kwance tana kallonsu taji tausayinta ya kamata sai ta dawo ta tsiyayi lemo a kofi ta daga kanta ta bata sannan ta juya mata kwanciyar kamar yadda ta saba yi mata kullum idan ta juyata dama in aka jima sai ajuya ta hagu kota zaunarda ita ta jingineta ajikin filo don dai taji dadi a jikin ta, cikin sanyin murya kaltum tayi mata magana tace goggo zan raka Madina sauri take yi nasan kina jin yunwa ba yadda zanyi dana baki abincin kafin mutafi amma zan fadawa mama ta baki saidai tace bakya ci dayawa idan bani na bakiba ki daure kici dayawa anjima zan dawo,
goggo fattu ta gyada kai tayi murmushi sannan itama kaltum taji dadi tayi dariya ta fice kuka kawai Goggo Fattu keyi tana nadamar abunda tayiwa yarinyannan sai gashi duk duniya babu mai kula da ita irin kaltum yanzu ko ancewa sofi tazo ta bata abinci saita ga dama zatazo, hidimar mijinta dana 'yayanta ne kawai agabanta,
hankalin sofi a tashe take tambayan kaltum yaya bakuwarki tace tafiya zatayi ko abinci bataci ba?
kaltum tace hankalinta yayi wajen' yayanta bazata iya zama taci abinci ba ki barta kawai zan rakata idan daddy ya barni ga Goggo can a daki tana jin yunwa kibata abinci saina dawo zanci,
sofi ta amsa da to saikun dawo, kaltum ta fita tana waige waige tana neman Madina can a jikin get ta hangota tana amsa tambayoyi malam saleh mai gadi,
kaltum ta wuce kai tsaye cikin gidan alh Adnan a babban falo ta tsaya tana rada sallah ma can yaji ya amsa bayan yan mintina ya fito daga daki a alama a kwance yake yana hutawa, dubanta yakeyi cike da
mamaki domin ya ganta da gyale harda jaka
arataye ya tambaya lafiya ina zakije da tsakar rana?
ta durkusa agabanshi ta sunkuyar dakai kasa tana magana cikin ladabi daddy Madina zan raka wajen 'yayanta da Abba tace ko minti daya bazata kara ba don hankalinta yayi gaba.
alh Adnan yayi daria yace daman tana son Abba da yaranta ta tsallake su tabarsu dakyar ta yarda ta dawo?
ke ma daman kina son Adnan kika ki biyo sa'adu a dadin rai kikace dan ADON DAWA zaki bi?
sai kaltum tayi sauri dukar dakai kasa har ya gama bayanansa bata kara hada ido dashi ba daga karshe yace kije ki duba danladi yakaiku a motarki ya jira ki ku dawo tare kafin la'asar, kaltum ta amsa da to mungode ta mike ta fice tabar alh Adnan da tunani iri iri,
kaltum da Madina a cikin mota gidan baya babu wacce take magana a cikinsu kowaccensu na tunani yadda za a yi arangama da juna har sun kama hanyar yankaba Madina tace kada muje gidan general tukur gara ku kaini gidan sumayyah tukur a koroa road saitace danladi koroa road zamuje ba yankaba dan haka saiya juya kan mota ya doshi can.
Madina tana nunamishi hanya har bakin get din gidan dr sumayyah anci sa a kuwa bata manta gidanba duk a akwai yan canje canje a unguwar ba ta manta lambar gidan ba da alama dai tana ciki saboda motoci har guda ukune a tsaye a farfagiyar gidan har kaltum ta fito daga mota madina na zaune cikin mota bata da niyyar fito wa, lafiya kika ki fitowa?
kaltum ta tambayi Madina.
madina ta girgiza kai tace saida nazo kofar gidannaji bazan iya shiga ba saina tuna marin da sumayyah tayimin da bakaken maganganun da ta fada min gara mu tafi basai mun shiga ba,
Kaltum sai kawai ta tura get ta shiga cikin farfajiyar gidan da sauri bata kula da kwalla kira da Madina take mata ba haka bata saurari dogayen horn dinda danladi ke matsa mata ba burinta kawai ta ganta a cikin gida, dai dai falon shiga taci karo da sumayyah da kaninta Abba suna fitowa da alama tafiya zaiyi don yana rike da makullin motarsa a hannunsa sukayi kicibus suka tsaya suna kallon juna aka rasa wanda zaiyi magana wakike nema yammata?
sumayyah ta tambayi kaltum, Abba ya
dubi sumayyah yace baki ganeta bane?
kaltum ce wacce ta kawo mana labarin inda Madina take,
sumayyah ta rike baki tace na tuna kaltum lafiya?
kaltum tayi murmushi tace lfy klau,
sumayyah tace ya ake ciki da zancen nemo Madina?
babanki yayi masa alkawari zai kawo masa Madina Abba ya damu yanzu haka zance ya zo muka yi ina tabashi hakuri kalli idanuwansa kiga yadda sukayi ja kwana yake bai yi bacci ba ku taimakemu...
Abba cikin gigita yace kaltum kada fa kice anje nemanta ba asameta ba?
kaltum ta girgiza kai tace kafin ince muku wani abu kuzo bakin get kuga wani abu ta juya da sauri ta fara tafiya yayinda cike da fargaba suke biye da ita a baya babu wanda a cikinsu yakawo abunda take shirin nuna musu ko a mafarki koda wasa basu taba zaton zasuga abunda ta nuna musu ba, kwatsam saiga Madina a zaune acikin moto tamkar a maparki bakin kowannensu ya kasa rufuwa,
sumayyah tukur ta kwalla kara ta fada cikin daga murya lah Madina kece?
AlhamduLillah Allah nagode maKa, suka rugo da sauri suka rungume juna yayinda hawayen farin cike yake zubowa daga idanuwanta su dukka hudu sai aka hau kallon kallo tsakanin
Abba da Madina saboda kallonta Abba har karkace kai yakeyi batareda ya iya mata magana ba,
(Sadin maa nace, "Allah Sarki So, Boss se yaya? ")
ta fashe da kuka tace Abba Abba kaine wannan ashe zansake ganinka a rayuwata?
saiya share hawaye yace Madina mai yasa kika tafi kika barmu?
meyasa baki zauna ba kikaje kika jefa rayuwarki cikin wahala?
sumayyah taja hannun Madina ciki da sauri
yayinda Abba da kaltum ke biye dasu a baya har babban falo suka zazzauna sumayyah ta jawo wayarta ta bugawa mummy hafsat tana dauka sumayyah ta fashe da kuka tace mummy ki taya mu murna ga Madina a gida na.
mummy hafsat ta dau dogon salati ta karasa da hamdala sannan tace abawa Madina kan wayan cikin farin ciki da fara a madina take gaishe da mummy hafsat sai data ji muryarta sannan ta yarda Madina ce,
ke kuwa madina me yayi zafi haka dazaki tafi kibarmu haba?
madina idan baki zauna danmuba ai saiki zauna don Abba mai sonki da kananan 'yayanki.
Sai hawaye ya surnano daga idanuwan madina tayi shiru kanta a sunkuye akasa batasan amsar da zata bata ba.
Abba ne ya taso da sauri ya mika mata hankici fari mai kamshi ya fada cikin lallausar murya madina goge hawayenki ki daina kuka
(WAI INA BOSS NE?)
Ta dago ido ta dubeshi saita yimasa lallausan murmushi ta gyada kai alamar naji sannan ta karba a nutse take sharce hawayen,
ya koma kujerar da yake zaune a saitinta ya kura mata ido ko kiftawa bayayi fuskarsa cikeda annuri kamar wanda aka yiwa albishir da gidan aljannah,
kaltum kuwa Abba kadai take kallo
tana mamakin irin wannan so dayakeyi wa madina duk da lalacewarda tayi,
SADIN MAA NA CE, AI SO BB WASA, YADDA NA KAMU DA SON JAMA'AR GIDANNAN
tayi baki ta rame ba kamar yadda take da kyau kamar da ba saita dinga ayyanawa a ranta dama itama a nemo mata mambelanta
(yess bosss)
kamar yadda aka nemowa Abba madinarsa,
madina ta mikawa sumayyah waya tace mummy tace yanzu zatazo nan gidan aida ta bari naje na gaishesu ita da daddy,
dr sumayyah tace ai daddy baya kasar kinsan mummy bazata iya hakuri ba ta zo ta ganki ba yanzu saboda ta damu da rashinki kullum tazo cin abinci sai tace Allah sarki Madina ce mai dafa min abinci kala kala musamman idan ta tuna sakwararki wani lokaci sai dai kaga tana hawaye.
Madina ta girgiza kai tace rayuwa kenan yaya za ayi da kaddara idan Allah Ya kaddarawa bawanSa bai isa ya tsalleke ba cikin ikon Sa da yardarSa Ya dawo dani gida na ganku lafiya Shine abun godia.
daddadar muryarta da lafazanta masu ma'ana sai suka ratsa jijiyoyin jikinsa ya lumshe ido don dadi ya bude ido ya dubeta yaji kamar ya hadiyeta ya fada aransa inason madina Allah Ka yarje min in aureta Ka bani ikon riketa amana, (SADIN MAA NA CE, AMEEN ABBA)
sumayyah Tukur ta harareshi tace tashi ka tafi wancan falo ka zauna kabamu waje mu tattauna da aminiyata kazo ka tsura mana ido,
Abba yayi dariya yace sister sumayyah keya kamata kitashi ki bamu waje mu tattauna, sumayyah tace indai Madina ce sai ka gaji da ganinta karewa ma gidanka za a kaita kuje can ku karata, sai Abba yaji gabansa ya fadi kar Madina ta fada abunda zai daga masa hankali sai yaga ko kusa bata bijireba saima murmushi datayi kawai tace Allah ne mai yadda Ya so da bayinSa Allah Ya zaba mana mafi alkhairi.
sai hira sumayyah takewaya Madina tana fada mata irin mummunan hali da suka shiga a sana diyyar rashinta sannan sunyi nadama
da sukaji gaskiyar al amari cewar ba laifinta bane, ta kara da cewa hudubar shaidan ne ta shigesu suka manta da kaddara har suka zargeta kuma harda zugar makiya wadanda daman basa so su gansu tare, suka zuga su kuma suka tunzura suka yi mata abunda sukayi mata, hawaye ne kawai ke zubowa daga idanuwan Madina shi kuwa Abba babu abunda yafi daga masa hankali shi ne idan yaga tana kuka yace da 'yayarsa 6star sumayyah don Allah ki bar zancen nan kina sata kukafa... shigowar mummy hafsat da ' yayan madina shi ya katse hirar da suke yi murna da hayaniya ta gauraye falon, Madina ta tashi da sauri ta rumgumi mummy hafsat sannan ta rungumi 'ya yanta su dukka ukun suka kankame ta suna kuka don farin ciki da kyar sumayyah ta bambare su daga jikin uwarsu suka zauna,
mummy hafsat ta shiga lallashinsu domin har yanzu basu tsagaita da kukanba saiga Tasi'u ya shigo wur janjan yana fadin ina matata Madinar take?
fuskar Abba zaka kalla kaga yadda ya bata rai yana hararar Tasi'u yayinda kishi ya tashi,
(ta yadda nima tawa kishin ya tashi sabida jama'ar gidannan me albarka) Sady.
kayi mata sannu da zuwa ka tafi mana saboda nan gidan surakai ne ba gidanmu bane bai kamata ma aringa irin wadannan maganganuba,
Madina ta dago ta dubi Tasi'u sai taji ranta ya baci yana tsaye akanta yana ta surutai barkatai kamar tababbe itadai tunda ta gaisheshi bata kara bashi amsa ba,
yace Madina ke kuwa meyasa zaki zauna a can?
kuskurene mukayi kuma kowa ya gane Madina ki rike amana ki tuna nine mutum na farko da kika fara sani a arewa, nine mijinki uban 'yayanki na girmeki nafiki hankali nafiki sanin dunia haka kuwa ya kamata miji ya kasance tsakanin sa da matar sa,
Abba yasan habaici Tasi'u yake masa don haka saiya fusata yayi magana cikin fushi yace ina ganin bai kamata a fara yiwa madina irin wadannan zantuttukaba barkatai don yanzu ta zo ko hutawa batayi ba ita ya dace ta zabi wanda zata zauna dashi basai anzabar mata ba, saboda tafi kowa sanin abunda yafi dacewa da ita a rayuwarta, tasan halin wahala da takaicin data dandana a baya, zata yi hasashe wacce irin rayuwa za tayi nan gaba.
Tasi'u ya fusata ya juya ya dubi mummy hafsat yace mummy kinajin yaron nan ko idan manya suna magana saiya dinga tsoma baki alhali niban ambaci sunansa ba.
mummy hafsat tace tashi ka koma wancan falon karka sake magana, Abba ya mike ya fice daga gidan ma gaba daya,
Tasi'u dai ya lankwashe kafa yana ta magiya Madina ta dawo gidansa,
takaici yafi damun 'yayansu ma basu madinarba ma,
Abdul Malik ya fusata yace haba baba ka bari ta huta mana kafin ka sako wata magana a ina aka taba yin saki uku kuma a koma a zauna?
Tasi'u yace ai nasan tayi aure a sudan ko batayi ba ma zata iyadawowa ta tausayamin ina son ta da ba tanan a gidana sai duk ya mutu,
Madina ta girgiza kai tace Allah Ya saukake ni banyi aure acan ba,
sumayyah tace kinga babu zancen kome tunda saki ukune kuma batayi wani aurenba,
kema bayan kanin naki zakibi?
sumayyah haka zakimim?
Tasi'u ya pada ransa a bace,
mummy hafsat tace Tasi'u don Allah kabar
maganan a nan saikun hadu daga kai sai ita,
Madina duk hukuncinda ta yanke shikenan ai wannan ba maganar da za ayita bane agaban yara ba, sannan matar nan yanzu tazo ko wartsake gajiya batayi ba.
Tasi'u ya gyada kai yace hakane gaskiyane ai
shiyasa ake neman shawarar manya toni zan tafi Abdul Malik kuzo mutafi,
Abdul Malik ya girgiza kai yace ba yanzu zamu tafi ba, tare da mummy hafsat mu kazo daman,
Tasi'u yayi kasake don shima bayason tafiyan bai gaji da kallon abar kaunar sa madina ba duk da hautsinewar datayi batada
kyauwun nan nata irin na da amma duk da haka tafi sauran matansa tsari da kyan gani, yayi ajiyar zuciya yace to banyarda wani acikinku ya kwana ba ina gida ina jiranku kafin magruba mekukeci na baka na zuba kuda uwarku zata dawo gidanku kacokan ma ku kwana a dakin ta,
kowa ya zuba masa ido yana dubansa kamar wanda yake kallon tababbe a talabijan babu wanda ya iya magana har ya fice a farfajiyar gidan suka sake jiyo muryarsa yanayiwa Abba hayaniya duk dai akan Madina Allah cikin ikonSa sai Abba yaki kulashi ko kallo ma bai isheshiba yayi surutunsa ya gaji ya tafi.
Madina ta juya ta dubi 'yayanta tace me yake damun mahaifinku ne?
ya gamu da matsalar kwakwalwa ne bayan
tafiya ta?
Abdul Malik yayi dariya yace lafiyarsa Kalau mama,
madina ta dubi sumayya tace anya alamaran
Tasi'u akwai hankali a ciki kuwa?
sumayyah ta kwashe da dariya tace zafin so ne da tsananin kishi yake damunsa.
mummy hafsat ta tabe baki tace nadama ce hakkin zalunci suke tambayarsa ni wallahi har alamarin nan ya fara bani tsoro tun kafin ki dawo yake neman tashin hankalin balle yanzu da kika dawo bamu san wahalar da zai ballo mana ba.
Madina tayi tagumi tace Allah ma zai yayyafa wa abun ruwan sanyi Allah Ya sa ya gane gaskiya daga nan suka bar hirar Tasi'u,
Abba ya shigo aka dinga hira wasa da dariya yayinda sumayyah da masu aikinta suke can akicin suna ta hidimar dafa abinci iri iri suna fitowa da shi, ana jerawa a gabansu madina..
Jama'a gaskiya kishi na nima ya motsa PA, har yana neman sanya min hawan ruwa, kowa kullum se Dan Anty kawai ake ta ambato domin an pi son sa an pipita sa a kaina bayan nima ina yin ku kuma kun sani..
ADON DAWA 44
.
TRUE LIFE STORY
.
sumayyah ta kwashe da dariya tace zafin so ne da tsananin kishi yake damunsa.
mummy hafsat ta tabe baki tace nadama ce hakkin zalunci suke tambayarsa ni wallahi har alamarin nan ya fara bani tsoro tun kafin ki dawo yake neman tashin hankalin balle yanzu da kika dawo bamu san wahalar da zai ballo mana ba.
Madina tayi tagumi tace Allah ma zai yayyafa wa abun ruwan sanyi Allah Ya sa ya gane gaskiya daga nan suka bar hirar Tasi'u,
Abba ya shigo aka dinga hira wasa da dariya yayinda sumayyah da masu aikinta suke can akicin suna ta hidimar dafa abinci iri iri suna fitowa dashi ana jerawa a gabansu Madina
kaltum ta sami hira da ciye ciye saita manta da direba a waje ta kuma manta da gargadinda alh adnan yayi mata kada ta dade ta dawo da wuri,
bayan sunyi sallar magruba ne kaltum ta zaro
wayarta acikin jakarta saita ga 10 missed calls din danladi 5 missed din alh Adnan nan da nan sai hankalinta ya tashi sukaga tahau rawar jiki har ta kasa yafa gyalenta dai dai, kaltum lafiya saurin mekikeyi haka?
madina ta tambayeta.
na manta a gida ance kar in dade wayata a jaka bansan suna ta kirana ba shine nakeso naje gida da wuri, a tsaitsaye tayi masu sallama ta suri takalminta ta tafi bata ma tsaya ta saurari rakiyar madina keyi mata da rokon da takemata ta dawo gobe ba burinta
kawai ta ganta a cikin mota ta ganta acikin gida gaban alh adnan sannan tayi shirin amsa dogayen tambayoyinsa,
danladi ya dubeta da alama ransa ya baci ya fisge mota batareda wani daga cikinsu yayi
magana ba saida suka yi nisa kaltum tace danladi kayi hakuri na barka kanta jira bansan lokaci ya ja ba anata hira wayata a jaka ban ji kiranku ba.
dan ladi yace ai bani ne abun ji ba daddy ne kinga irin fadan da yake yimin a waya wai me yasa za mu dade haka nace kina cikin gidan yace in aika a kira ki narasa dan aike kuma nayi kiran wayar ki ba amsa niyanzu nasan duk fadan akaina zai kare,
sai kaltum ta dafe kirji tayi shiru tana karanto duk addu ar data gifto bakinta suna isa bakin get taji wata jijiya ta harba acikin kirjinta tamkar zuciyarta ce ta tsinke don fargaba daga yadda saleh ya bude get a fusace tasan yau ba lafiya saita fara kuka, suna tsayawa da mota saita fito a hankali tana mai tafiya a hankali tamkar wacce kwai ya fashewa mata a ciki,
alh adnan ta tsinkayo a tsaye akan baranda ko zama ya gagare shi da alama fuskar nan ba annuri daga ita har danladi sai sunkuye sunkuye suke yi da kai kasa aka rasa wanda zai fara wucewa gaba yaje yayi bayani.
tsawa ya daka musu saisu dukka suka hargitse fargabar ta karu yace bazaku karaso
bane ina tsaye ina jiranku sai wata sanda kuke yi

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login