Showing 114001 words to 117000 words out of 144367 words
ma masu kudine gara ace mahaifiyarku ta dawo hannun mahaifinku gaku ya yanmu muzauna tare ai yafi kwanciyar hankali ko ba haka bane?
Babu wanda acikinsu ya bashi amsa saima murtuke fuska da suka sake yi sai Tasi'u yafara tsorata da alama basa goyon bayan sa, har ya sallamesu suka bar falon babu wanda ya furta masa kalma daya shi yayi kukansa ya lallashi kansa.
suna fita suka dunguma kofar gida don su sami lungu da zasu fake suyi shawara kasancewar cikin gidan ko ina mutane ne, can wani kofar gida suka sami wani dakali suka zauna Abdul hakim ya dubi yan uwansa yace Allah sarki mamanmu Allah Ya yi mata jagora Ya taimake ta aduk inda take, mun saba mata mun zargeta alokacinda kowa ke zarginta maimakon mukasance mu kadaine masu bin bayanta aduk duniya, na tabbata dabadon abunda mukayi mata a asibiti ba da bata shiga duniya ta barmu ba, dako saboda mu zata zauna a kasar koda kuwa za a dinga jefinta ne don tsana...
saiya fara kuka yayinda dukka suka rushe da kuka.
Abba Tukur ne ya bayyana agabansu basuga tahowarsa ba saida suka daga ido suka ganshi a tsaye akan su, ya dubesu daya bayan daya sai yaji tausayin su, ya sunkuyar dakai kasa sai hawaye ya surnano daga idanuwansa yayi karfin hali ya fara magana amma kuka ya hanashi cigaba, ya dade a tsaye yana hawaye marar kakkautawa sai can ya tsagaita yarasa wanda zai fara lallashi
acikinsu saboda tsananin halin kuka da yaran suke ciki, ya ce 'yayan Madina nasan damuwarku wanda take dai-dai da damuwata nasan irin zafinda kuke ciki na rashin mahaifiyarku wanda yayi dai-dai da yanda nakeji idan ma bai dara naku ba, kubar kuka
ku tayani da addu'a iyayena sumin lamunin tafiya,
zanje na karbo adireshi a wajen yarinyan nan
kaltum inje in taho muku da ita kusani ina so na auri madina saboda ina sonta saboda Allah idan na auri Madina nagama samun farin ciki a rayuwata, nayi muku alkawari zan rike muku mahaifiyarku tsakani da Allah daku 'yayanta gaba daya, kada ku biyewa mahaifinku da yake fada cewar rashin kunya ce ni dan yaro inason in auri Madina, ku tuna auren Nana Khadija da Manzon Allah S.A.W
Ya aureta tana bazawara kuma ta girmeshi bai haramta ba kuma bai hanata yi masa biyayyh ba....
Abba bai rufe bakinsa ba yaji wata murya mai
firgitarwa daga bayan sa sai suka waiga da sauri a gigice,
Tasi'u ne ya fita a fusace daga cikin motarsa ya tunkaro Abba Tukur yana magana cikin fushi yana nunasa da yatsa kai Abba kafita daga harkan gidana tunkafin ta kaimu ga kotu, daman nasan kai kake tara yarannan kana yi musu hudubar banza to bari kaji na fadamaka baka isa ka auri Madina ba indai ina raye ko kai ko ni.
Abba yayi murmushi yayinda ya zura dukka hannayensa acikin aljifan wandonsa ya sunkuyar dakai kasa kamar mai tunani can ya dago yadubeshi yayi murmushin karfin hali yace kada ka manta ka saki Madina saki uku, aurenta dakai ya haramta sai in har ta auri wani ta fito sannan zaka iya mayar da ita, kaga ko bani zata aura ba sai ta auri wani sannan takoma gidanka inhar zata koma kenan,
malam Tasi'u banzata akwai ranarda zaka dawo kana son Madina ba bayan musgunawa dakayi mata ka wukantata ka koreta, banaji akwai wani nauyi ko kararta zanyi maka akan aurena da Madina ba saboda bazan kira rabuwarku da kaddara ba kana sane ka saketa iyayena sun lura inasonta sun kuma yarda in auri abunda nakeso don haka babu mai hanani auren Madina...
a fusace Tasi'u zaikaiwa Abba mari sai yarike hanun nan da nan alh Isa da malam muhammadu makwabtan su suka garzayo da gudu suka shiga tsakaninsu, akaja Tasi'u
zuwa motarsa Abba kuma aka kaishi gida.
hankalin 'yayan Madina yakara tashi ya sake tashi amma gaba dayansu sunfi amanna da aurenta da Abba akan ta koma gidansu, gidan wahala da tashin hankali, fatarsu ma aga Madina tukunna sannan afara zancen aure, yaran madina sunfison Abba sunsan shi mahaifinsu dayake wannan fada ina yaga kudin jirgin da zai je ya daukota a sudan?
idan yadaukota ma ai bazai iya auranta ba saboda babu wani sauran igiyar aure a tsakanin su, rabuwa uku ce Abba kuma in har an amince masa agidansu yanada kudinda zai iya hawa jirgi ya taho da ita kuma sun yarda da sonda yake mata idan ya aureta zai riketa amana ba ita kawaiba harsu kansu tun bayan da yashekara akwance a asibitin london ya warke ya dawo yake basu duk wani abu da sukeso aboye naci kona makaranta basu taba tambayansa wani abu sun rasa ba ko basu tambaye shi ba shi dakansa sai ya kirawosu ya basu kudi mai yawa duk da ma yana tsoron basu kudi mai yawa kar mahaifinsu yagane to inaga ya auri mahaifiyarsu kuma?
Abdul Malik yanzu jami'ar ABU zaria yake yana level 3 yayinda Abdul hakim yake level 1 a BUK, Shahida kuwa a sakandari take aji biyu duk wannan fadace fadace da ake yi har ana ambaton kotu duk fa akan Madina ne to bata nan, ba amasan inda za a same taba,
gata batada niyyar dawowa kuma .
lalle Tasi'u dagaske yake kuma yadau abun dazafi saboda da daddare yashiga har cikin gidansu Abba ya iske mahaifinsa da mahaifiyarsa a falo ya lankwashe kafa yakawo karar Abba akan ya rabu da matar sa Madina,
abun yabasu mamaki domin su basu zata akwai ranarda Tasi'u zai sake waiwayan Madina ba bayan juya mata baya dayayi yanunawa duniya yagaji da ita baya kaunarta, irin tsawon lokacin da mummy hafsat take batawa wajen gargadinsa kada yasake ya rabu da Madina amma baijiba sai gashi yau agabanta yana kuka yana maimaita nasiharda tayi masa abaya yana nadama,
takaici yahana genaral tukur furta koda kalma daya tak har Tasi'u yagama yatashi ya tafi,
mummy hafsat ce mai bashi hakuri amma ta shaidamasa basuda ikon hana Abba son abunda yaji yanaso kasancewar Madina batada igiyar wani akan ta,
da alama baiji dadin abunda sukayi masa ba ba haka yaso jiba so yayi suce zasu tsinewa dansu idan bai rabu da zancen Madina ba.
barister Abba Tukur ne da kaninsa engr Anas suka dira akofar gidansu kaltum da misalin karpe biyar na yammacin laraba, suka ajiye motarsu a wurin get yayinda suka tura kai cikin gidan, mai gadi ya taresu don jin wanda suke nema dasuka shaidawa malam saleh kaltum suke nema saiya yi matukar mamaki gami da fargaba ya tambaya cike da firgici lafiya kuwa kuke neman kaltum?
lafiya mana maigadi inji Anas yayinda yake murtuke fuska saboda rashin jin dadin tambayanda yayi musu kasancewar yasan basu san shi ne mahaifinta ba, sai bai tamuba ya shaida musu cewa batanan ta tafi makarantar islamiyyah sai karfe shida zata dawo,
sai suka koma wajen get suka shiga mota suka zauna zaman jiranta suka ci gaba da shawarta abunda yake tafe dasu,
tajikin madubi Anas ya hango kaltum ita da kannenta suna kokarin tura get zasu shiga gidansu ya fito ya kwala mata kira ta tsaya cak tana dubansa cike da mamaki ta rasa inda ta taba ganin fuskarnan, ya karaso gareta yayi murmushi yace kada fa ace baki gane ni ba kin manta gidan sojojin nan da kike zuwa a yankaba inda aka kusa zaneki da belt kwanakin baya?
idan kin manta ai bazaki manta gidansu shahida ba yar Madina,
sannan kaltum ta tuna da fuskar ta kwace da dariya tace Anas ashe kaine?
malam saleh ya fito wuf ya dubi kaltum ya juya ya dubi Anas ya tambaya cike da bacin rai waye wannan ?
Matsalan kaltum bata tautauna halinda take ciki da mahaifanta don haka basu taba sanin labarin Madina ba balle ta shaida musu taje ta nemo danginta,
idan takama nan saita saki ta zargo can, zancen dai a cukurkude bai fahimceta ba don
haka yayi mata umurni ta shiga gida ba zata gansu ba,
Anas baiji haushiba saidai ma mamaki daya hanashi magana saboda baizaci mai gadi yana da ikon hana yar maigidan abunda takeso ba, ya tsaya yana duban malam saleh kawai har ya rufo get ya shige yabarshi tamkar gunki,
hankalin Abba ya tashi saboda yanaso ya shaidawa mai gadin cewar suba samarinta bane kawai maganar Madina zasuyi, Anas yace su tafi kawai har yaushe zasu tsaya suna rokar maigadi da wata tsummar rigar sa?
suje saisu dawo wata rana,
Abba yakasa sukuni kwana biyu da tafiyarsu yaji bazai iya jurewa ba har saiya dawo yaji labarin madinarsa don haka bai gayyaci Anas ba saiya figi motar sa yayi gidansu kaltum tunda yaga hanya, yazo da yamma tunda yasan jummaa ne babu issalamiyyah tsayuwar sa abakin get din kenan yayi dai dai da lokacin da alhaji Adnan ya iso daga Abuja don bazai ya shiga da motarsa ciki ba saboda Abba yatare kofa, kallon-kallon aka hau yi a tsakaninsu alhaji Adnan, ya fuskanci tabbas Abba bai sanshi ba ne maigidan ba, kuma so yake yashiga da motar ciki don haka sai ya fito ya dubi Abba yayi murmushi yace ranka yadade kozaka matsa gaba inaso inshiga da mota ciki.
Abba yayi sauri ya shiga mota yace kayi hakuri na tareka don Allah idan ka shiga ciki Kamin sallama da kanwarka kaltum,
mamaki ya dabaibaye zuciyan alh Adnan ..
ADON DAWA 38
.
TRUE LIFE STORY
.
mamaki ya dabaibaye zuciyan alh Adnan ya ratso har fuskarsa ya dubi Abba ya dubi tsalaleyar motar da yake ciki,
bayan ya matsar da motarsa sai alhaji Adnan ya danna horn malam saleh ya bude masa get ya kutsa ya shiga cikin gida, bayan yan sannu da dawowa sun iso suka kwashi tsaraba zuwa cikin gida wato kaltum da kannenta kenan daga yanda alhaji Adnan ya amsa mata da yadda ya kalleta ya watsar tasan ba haka ya saba yi mata ba, tabbas akwai dalili daga yanda malam saleh yaga yau alh Adnan baya fara'a yasan ba lafiya, don haka sai hankalin kowa ya tashi,
alh adnan yafito kofar gida batare dayayi bayani ba,
tabbas malam saleh ya zargi ko yan gulma ne suka fada masa cewar samari sunzo neman kaltum shekaran jiya.
alh Adnan yakarasa har jikin motar abba a inda ya iske shi a tsaye yayi masa sallama ya mika masa hannu suka gaisa,
alh Adnan ya dubi Abba yayi murmushin karfin hali yace kaltum kake nema ko?
daga ina yayi?
murmushi yace sunana barista Abba Tukur a unguwar yankaba nake .
alh Adnan ya kura masa ido yana dubansa can yayi ajiyar zuciya yace naji sunanka yaro sai kuma inji dalilin nemanta da kake yi, daman ka santane kokuma tasan da zuwanka?
abba yayi dariya domin yaji tambayoyin sunyi masa kama da tambayoyin da lauyoyi sukeyi wa mai laifi a kotu, ya ce kaltum tasanni amma batasan yau zanzoba nazo shekaranjiya mai gadinku ya hanata zo wajen mu dalilin zuwana bawani abu bane illa dai ina so tazama ido na ko ince itace fitilar da zata haskaka min hanya wajen neman allura cikin duhu.
alh Adnan ya dago da sauri ya dubi Abba yayinda ya caka masa mashin harara ya fada cike da gadara yaro ban fahimceka ba?
Abba ya girgizakai yakara yin wani siririn murmushi yace ranka dade karkadamu nazo neman alfarmane a wajen ku kanwarka kaltum ne tazo min da labarin ta baro matata a sudan tana can tana bara shine nake so tamin kwatance ko ta taimakamin ta rakani inda Madina take mu dauko ta don mu mun rasa inda take har mun zata ma ta mutu...
alh Adnan yakatseshi tunkafin yarufe bakinsa
cikin sakin fuska da dariya yake magana don ya fahinci abba ba zance yazo ba yace yi shiru yaro na fahince kana so kace min kaima matarka tana cikin yan gudun hijira ko ince masu tarar aradu da ka masu tafiya makka da kafa ko?
to sai dai mu musan abunyi domin kaltum bazata sake leka wa sudan ba da sunan takawaba ba balle rakiya, kai da kasan wahalarda nasha kafin akawo min ita ai da bazakace zaka nemi izinin rakiyarta ba, kaltum karatun jarabawane a gabanta banaso a dinga maganar sudan da ita saboda ina ganin alamun damuwa a tattare da ita idan aka ambaci sunan sudan don haka banaso ka sake sakata ma acikin maganan duk abunda kakeso ko kake nema ka nemeni nayi maka alkawari zan taimaka maka iya taimako saboda nasan yadda kake ji.
ba karamin tashin hankali bane ace an gano matarka ko yarka ko kanwarka awata kasa tana bara ba, sai sunyi bara sannan suci abinci mace musamman budurwa ai bala'in yayi bala i sai fatan Allah ya kiyaye gaba, yanzu dai ka rubuta numban wayata ka kirani gobe da safe muyi magana daga abuja nake yanzu nagaji,
sai godiya abba yakeyi ba iyaka yayinda farin ciki ya mamaye zuciyanshi yaji tamkar ance masa ga Madina nan adaki za a fito masa da ita, ya dauko waya alh Adnan yana karanto
masa yana rubutawa ya fada cike da ladabi wani suna zan saka?
alh adnan yayi murmushi yace ka rubuta kaltum Adnan.
Abba ya maimaita sunan kaltum Adnan...
alh Adnan yace karka damu ka rubuta haka sai kafi ganewa,
ya juya ya bar Abba a tsaye cike da mamaki yayinda yabishi da kallo har saida ya shige cikin gida zuciyarshi cike da tambayoyi shin wannan mutumin yaya yake da kaltum?
Gashi dai sunso suyi kama amma yace shi ba yayanta bane kuma baici ace babanta bane don shekarunsa baici ace ya haifeta ba ita ba matar aure bace bare kuma ace mijinta ne to ko kawunta ne ?
Amma da gatanta to meyasa suka bari ta tafi sudan ?
Gara ace Madina ace rashin gatane kodayake a labarin ta ta ambaci wata tsohuwace ta tafi da ita ta ambaci wani masoyinta abar kaunanta mambela don haka wannan ba mijinta bane koma dai wanene wannan yana sonta kuma yana kula da ita sosai tabbas yana tattalinta..
tunanin da abban Madina yake yi kenan a zuciyar sa har ya iso gida bai iya barci ba daga ya rufe ido sai yaga kamar Madina sai yayi sauri ya jawo hotonta yaga Madina ta lalace ta susuce ta fita hayyacinta idan yayi kuka saiyayi adduar Allah ya bayyana masa ita amma jikinsa yakanyi sanyi idan ya tuna Madina zata iya zuwa taci gaba da bujirewa aurensa.
bayan gari ya waye Abba waya yasa agaba yana kirga awannin yana jiran goma na safe yayi sannan yakira kaltum bayaso yadoka masa sanmako.
alokacinda agogon alh Adnan ya buga karfe goma da wayar Abba tare suka isa kunnuwansa alokacin da yake tautaunawa da mai gadinsa malam sale a katafaren falonsa ya dubi agogo ya juya ya dubi wayarsa baisan lambar ba dan haka bai damu da sai ya amsa ba yaci gaba da bayanansa amma wayan bata daina ruri ba da zarar ta gama saita kara daukar kururuwa dole tasa ya saka hannu ya amsa ko dai wanene tabbas bakone don duk wanda yasanshi yasan dokarsa ba ayi masa waya kafin karfe 12 rana, alh Adnan ya amsa
sallamar mai yi masa waya sai ya kasa kunne yana sauraronsa Abba ya fara da gabatar da kansa dakuma inda yake da alama har yanzu alh Adnan bai gane ko wanene ba daga yanda yake amsa masa Abba ya fahimci haka don haka sai ya bashi labarin yadda suka hadu jiya cewar mijin Madina da take sudan tareda kaltum sai yanxu ya fahimce shi don haka sai ya saki ransa suka gaisa cike da faraa,
cikin fargaba Abba ya tambaye shi yace alh kace yau inkira zaka bani shawara ka taimake ni alh in samo madina kamar yanda Allah Ya taimakeka ka tsinto kaltum.
alh Adnan yayi murmushi yace samari ka kwantar da hankalin ka zan taimakeka abu daya ne nace bazan iya yi maka ba shine daka roki alfarmar kaltum ta raka ka sudan wajen Madina, bazan barta ba saidai zan hadaka da wanda na sani acan su taimakeka.
Abba ya yi godiya sannan ya gyara zama yana sauraronsa yayinda farin ciki ya lullubeshi...
malam saleh yakara tura hula keya yaci gaba da durgushewa yana sauraron abunda bai taba sani ba arayuwarshi wato maganan kaltum da Madina, koda wasa kaltum bata taba basu labarin rayuwarta a sudan ba saigashi alh Adnan ya sani harma suna tattauna da wani akan haka.
alh Adnan yabawa Abba labarin yadda akayi aka kawo kaltum gida yayi masa alkawari zai tuntube alh saadu yaji yan da za ayi ya nemo musu Madina a bur sudan ayi ciniki ya fadi yanda za a biya shi, ya umurci Abba yakirashi da yamma don yaji yanda suka tattauna.
Abba yayi farin ciki matuka yanata godiya har suka kashe wayan malam saleh ya jinjina kai
yayi murmushi yace wata yar gudun hijira ce ake nema ?
Alh Adnan ya kyalkyale da dariya yace yar gudun hijira ne kawar kaltum,
malam saleh yayi dariya ya sake lankwashe kafa yace daddy amintar nan taka da kaltum sai Allah kaga harta fada maka labarin kawarta a sudan mukuwa agida bata taba bada labarin tasan wata asudan ba ko da wasa bata taba zancen sudan da wani acikin mu ba, ka santa da miskilanci dakai kadai take hira shine kwanaki muke tattaunawa da sofi muke cewa ga kaltum ta kusa gama sakandari a cikin watan nan zasu gama, samari har sun fara biyota ranan ma saida na fita na fatattaki wasu a kofar gida bana so taci gaba da karatu a gida gara tayi jami'a agidan mijinta idan mijin ya yarda, saboda dandazo gidan nan zai zama dan ma bata kulasu shine mukayi shawara da zaiyu kuma idan kanada ra'ayi da sai na damka maka kaltum duniya da lahira hankali na zaifi kwanciya babu wanda zata aura yafi kulawa da ita fiye da kai duk da dai madam saliha ta kufula yanzu in taji zatace cin amana ne amma ai bai haramta ba, Alh sunan mun haifi kaltum ne kawai amma kai ka rainata da wahalhalunta dukka da taimakon Allah da taimakonka ne kaltum ta zama mutum,
badan haka ba ai da tuni ko a kwabo ba wanda zai dauke ta, saboda a kauye ko a sudan ta dauwama tana bara tunda bamuda kudin da zamu dauko ta, banida abunda zan iya saka maka taimako da rufin asiri da kayi min nida zuriata aduniya bazai misaltu ba, don haka na dauki yarinyan nan sukutum na baka nasan duk da haka ban biyaka ba kuma har abada bazan iya biyanka ba, ranka ya dade a duba maganata sosai agani idan da yuwuwar yin hakan ayi idan kuma