Showing 63001 words to 66000 words out of 144367 words

Chapter 22 - ADON DAWA

Unknown   

30 Oct 2024

5062

ya xo da ma’aikata ne yana so a shinfide musu katako a kasan dakinsu kasancewar ya ga kaltum daxu a kwance a kasan yashi shi yasa yak e so a buga katako saisu daina kwana a cikin yashi madina tace to amma sai ta shawarci sauran ‘yan dakin tunda basu biyu ba ne a dakin suna da yawa sun doshi su goma sha biyar. Mambela y ace ta je ta tambaye su idan sun amince sai ma’aikatan su shiga su fara.
Madina ta shiga gida ta samu ‘yan dakin su ta shaida musu nan da nan suka amince cikin farin ciki da xumudi suka dinga firfitar da kayansu waje madina ta riko kaltum wacce har yanxu tana yawan bacci ta kaita dakin kusa dasu ta kwantar da ita bsannan ta fita ta yiwa su mambela iso shi kuma ya umurci ma’aikata dasu dauko kayan aiki su shiga su fara. Mambela sai kai kawo yake daga daki xuwa tsakar gida xuwa kofar gida yana ta haska ido yana ta hangen mata reras a xaxxaune a tsakar gida amma bai hango abar kaunarsa ba kaltum ya kasa tambayar madina kuma.
Kafin magaruba an lelayewa su kaltum daki ras da katakwaye masu santsi, aka tottoshe musu hudojin rufin daki inda ruwa yake shigo musu lokacin damuna, aka huda musu window inda iska xata dinga shigo musu sannan aka gyara musu kyauren kofa aka yi musu sakata da wajen makala kwado.
Sai tururuwar lekawa dakin ake yi ana gani, sha’awa ta kama ‘yan sauran dakunan suna cewa dama suma a dakin suke. ‘yan dakin kuwa farin ciki suke harda tsalle yayin da suka kewaye mambela suna yi masa buda da kirari suna masa fatan Allah Ya bashi kaltum. Gogan naka sai ya ji babu kamarsu a duniya tunda suka Ambato masa sunan kaltum sai ya shiga rabon kudi saboda su sosa masa inda yake masa kaikayi wato xancen daya fi so a duniya.
Mambela da ma’aikatansa suka shiga mota suka tafi, da daddare bayan sallar isha’I sai ga mambela shi da direban mota sun dawo a cikin wannan katuwar motar karon ma a kofar gida ya tsaya ya aika a kira madina kofar gida, sai ta fito cike da mamaki. Mambela ta sake gani sai ya karaso inda take tsaye ya shaida mata cewar katifu biyu da fululluka ya kawo musu ita daya kaltum daya maimakon su ginga kwanciya a kan kwalaye saisu dinga kwanciya a kan katifa. Hawaye ne ya sirnanawa daga idanuwan madina dan tausayin mambela, sai ta tuno irin rawar jikinda Abba yake yi mata a sanadiyar son da yake yi mata.
Mambela da direban mota ne suka kinkimo katifun da fululluka kowa ya kinkimi daya daya suka shigar musu har kofar dakinsu. Mambela ya koma cikin mota sai gashi dauke da tobe (sakatara) labulen da yake kewaye daki gaba daya. Madina ta dinga addu’a da godiya har ya fita daga gidan yayin da mata suka cika dakinsu madina dankar suna ta yabon halin mambela kaltum tana xaune tana kallonsu tana kuma sauraron nasihohin da kowacce take mata, babu wacce bata bata shawarar ta kula mambela ba saboda karshen so mambela yana nuna mata, suka ce gara tayi karatun ta nutsu ta yiwa kanta fada tun kafin damar nan ta kufce mata.
Kwanakin kaltum uku sannan ta warware ras ta samu sauki , kallo daya xa kayi mata ka tabbatar ta samu lafiya. Kana ganinta xa ka ga t a dawo nutsatstsiya mai kunya, hankali da sanin ya kamata. Ashe daman yawan fushin da take yi da rashin son shiga mutane harda gudunmuwar aljanu suke tunxurata.
Hantsi yayi duk masu sayar da abincin safe sun gama don haka kowa yana cuku cukun kwasar kayan sana’arsa xuwa cikin gida. Kaltum ce a xaune kofar gida tana wanke kwarya, kaskon suya da kwanukan da ake xuba kosai. Sai ta ji sallama a bayanta, tayi sauri ta waiwaya sai taga mambela ne sai ta sunkuyar da kanta kasa alamar kunya tayi murmushi ta gaishe shi. Ya xagayo ya tsugunna a gabanta sai ya tsoma hannu ya fara yi mata dauraya yayin da yake yi mata hira iri-iri (SU DAN ANTY SE HAKURI) gyada kai kawai take yi ba tare da tayi Magana ba har suka gama wankewa dukka, ya taya ta kwashewa xuwa cikin gida. Tundaga wannan lokacin mambeala ya tabbatar kaltum ta fara sonsa badan komai ba saidan kunyarsa da take matukar ji, alamomin so kuwa shine kunya da jin nauyi, ladabi da biyayya.
Mambela kan daddagewa yayi fashin kwana daya xuwa biyu bai xo yaga kaltum ba saboda gudun kada ya takura mata amma badan xuciyarsa tana da sukuni ba har sai ya xo ya ganta yake samun nutsuwa. Sannan bai taba xuwa hannu haka ba, ba tare daya riko mata wani abu ba. Ko da yaushe yana taho mata da wani abu kamar sutura, kayan marmari, ko kayan sanyi irin su ice cream, lemo iri-iri (juices) sai kuma kudi mai yawa wanda xata dinga kashewa.
Yau ma kamar kullum yadda ya saba xuwa da yamma suna xaune akan wani dan dakali a gefen kofar gidansu kaltum suna hira. Kallo daya xaka yiwa kowannensu ka tabbatar yana cikin farin ciki da tsananin kaunar juna. Kana doso inda suke xaune xaka fara hango annurin fuskokin su musamman mambela wanda ke yawan kallonta yana yi mata magana kasa-kasa a setin kunnenta, sai dai duk inda ka kai da iya labe dan kaji abunda suke fada ba xaka iya jiyowa ba sai dai ita wacce ake yi dominta ita kadai take ji. Xaka iya ganin murmushin ta cikin kunya take gyada kai yayin da sonsa ya hana ta daga ido ta dube shi. Kanta a sunkuye yake a kasa da ‘iman.
Mambela ya dubi kaltum yace “yau ne ranar da muka yi alkawari cewar xaki bani tarihinki tun daga farko har karshe nima nayi miki nawa tarihin ba tare damun boyewa juna komai ba. Haka ne ko? ”
Kaltum ta gyada kai tayi murmushi tace haka ne.
Ya ce to bismillah, ina sauraronki.
Kaltum tayi shiru na dan lokaci sannan ta dago ta dubi mambela wanda ke dubanta duba irin na shaukin so da xumudin sauraron xaxxakar muryarta baya ga tsantsar kaguwa ya ji abunda xai fito daga bakinta, sai tayi sauri ta sunkuyar da kanta kasa. Ta laluba wani dagon kara da ke ajiye a gefenta ta fara wasa dashi a kasa tana tona rami yayin da ta fara da fadar asalin sunanta da sunan iyayenta, garinsu da asalin kasarsu. Hakika labarin kaltum ya fara tsumama xuciyar mambela don ya fara jiyo abubuwan da al’adaun da bai taba jiba. yana sauraronnta yana yi mata tambayoyi kala-kala akan abinda bai gane ba sai ya ji a ransa yana son Nigeria yana son al’adun hausawa. Ta bashi labarinta tsab bata boye masa komai ba kamar yadda ta bawa madina, tun daga sanda mahaifanta suka hadu suka yi aure har ixuwa ranar daya fara ganinta a duniya. Sai dai kash! Kafin tagama bada labarinta hawaye yayi mata face-face a ido shima haka, sun dade suna xubar da hawaye dukkaninsu saboda tausayin wahalar da kaltum ta sha a rayuwa. har aka rasa wanda xai lallashi wani a cikinsu, mambela yayi matukar tausaya wa kaltum sai ya ji ya kara sonta da kaunarta ya sake kara daura dantsen xakulo ta daga cikin rayuwar kangin da take ciki. Ya kasa kwatanto yadda xai jiye mata dadi idan suka yi aure, ya kasa auno irin tattalinta da xai yi don ta huce takaicin maraici da tayi a baya. Sai ya shiga lallashinta yana bata baki cewar ta kwantar da hankalinta komai ya wuce.
Amma ya tuhumi iyayenta da rashin kyutata wa wajen kin janyo ta a jiki da suka yi kamar dai yadda madina ma ta fada sannan yayi Allah wadai da hali irin na goggo fattu, y ace bata kyauta ba musamman da yaji irin axabar da ta gana mata a makka. Ya ce shi da ita su godewa Allah daya sa ba’a tafi makkan nan da ita ba, da wannan karon ma wahalar da xata bata sai tafi tada. shi kuma da aka yi haka sai ya fiye masa alkhairi tunda gashi ya sami dammar haduwa da ita.
Mambela ya dubeta yayi murmushi sai yayi mata wata tambaya wacce tasa saida ta dago idanuwanta kacokan ta dube shi yayin da amsa ta kauracewa kwakwalwarta.
Tambayar da yayi mata itace “kaltum anya kuwa alhaji adnan ba sonki yake bada gaske?
A ganina ba xargi matarsa keyi ba da gaskiyarta. Anya kuwa kyautatawar nan da yake yi miki da shakuwar da ku kayi ba xata juye tsantsar kauna ba har ya kai ku ga yin aure? ”
Wannan tambaya tasa bata da amsa sai kaltum ta mayar da kanta kasa bata iya cewa komai ba. Mambela yayi shiru na dan wani lokaci sai yayi ajiyar xuciya.
Ya ce “xan baki tarihina, yanxu xa kiji ko ni wa nene.”
WA NENE MAMBELA!
ADON DAWA 2 (P 19)
.
WAYE MAMBELA!
.
Ya ce “sunana Ahmad, sunan mahaifina Mahmud, mahaifiyata kuma Aisha. Iyayena sun fito daga dangi guda, jinin sarauta, sune suke da sarautar garinmu iyaye da kakanni. Mahaifin Aisha shine kanin mahaifin Mahmud uwa daya uba daya, mahaifin Mahmud shine sarkin garinmu yayin da mahaifin aisha shine waxirin sa. Tun kafin a haife ni suke kan sarauta har rana irinta yau suna nan basu rasu ba, Mahmud da aisha su kadai ne ‘ya’ya a wajen mahaifan su yayin da suma kadai suka Haifa don haka ni kadai ne ‘da kuma ni kadai ne jika a gidanmu gaba daya. Kamar yadda kika sani abu ne mai wuya a garinmu kiga namiji ya auri mata biyu, kowa mace daya yake aure balle a haifar min dan uba.
Gata yayi gata, ta ko ina nuna min kauna kama da kakannina xuwa iyeyena, danginmu harda mutanen gari masu neman fada.
Kaltum ta gyara xama da alama tana jin dadin labarin. Sai ta dube shi tayi murmushi tace Ahmad sunanka, me yasa ake kiranka da mambela? ”
Yayi dariya yace yawancin ‘yan garinmu idan kin lura xa ki ga duk an boye mana sunayenmu na gaskiya. an saka mana wani suna na kirari a yarenmu. Mambela suna ne wanda kakana ya saka min domin na yi kama da mahaifina sak, mahaifinna kuma ya yi kama da mahaifinsa sak shima, dan haka mu uku kamanmu daya. Kasancewar auren wuri dukkaninsu su kayi sai ki xata sarki shine babana, shi kuma babana sai ki xata shine yaya na. sarki yana ganin ni ne xan gaje shi ba mahaifina ba, tun ina dan karami sai ya sauko daga kujerar sarauta ya dora ni akai yace mambela ma’ana SAI KA YI shine jama’ar gaba daya suke kirana da mambela.
Kakanninmu basu yi karatun addini sosai ba, amma mahaifina yayi karatun addini sosai, yayi yawon neman ilimi gari-gari, lungu lungu dan haka babban malami ne sosai wanda bana jin akwai mai iliminsa duk garinmu. Amma ni kuma na ki karatu fur tun ina yaro, idan ya takura ni sai inyi ta kuka ina kururuwa har sai sarki ya jiyo ya aiko a xo a dauke ni, da yake gidan gado ne, na sarauta duk ilahirin danginmu a cikin gida daya muke xaune bangare bangare. Ba xaki iya sanin yadda gidanmu yake ba saboda ba’a barin kowa ya shiga gidan sarki saida wani muhimmin dalili kuma sai anyi maka iso shi yasa idan kuna bara bakwa shiga gidan da kin ga yadda tsarin ginin yake.
Na tashi a shagwabe babu mai saka ni babu mai hana ni, haka babu ilimin addini balle na xamani tunda garinmu babu makarnatar boko. Dan haka babu wanda yayi ilimin xamani. Sarki yaki yarda a gina mana makarantar boko a garinmu yayin da wadanda ba musulmai ba suma suke koyarda na su karatun addini a gidajen su. Mu ma muna da makarantun allo kalakala. Mahaifina yana da tasa tsangayar amma naki karatu, kakana kuma yace a kyale ni.
hakika kamar yadda kika samu wasu labarum a kaina cewar bani da kirki, ni dan shaye shaye ne, dan agulla mai fada da yanka jama’a tabbas ba karya ba ne duk abunda aka ce nayi lallai na yi din…………..”
Kaltum ta dago da sauri ta dubi mambela a gigice, kallon nan da tayi masa shi ya katse shi ya kasa ci gaba da maganar da yake yi. Sun dade suna kallon juna sannan suka dukar da idanuwansu kasa kowannensu yana nasa tunanin a xuciya. Kaltum ta ji hankalin ta ya tashi da ta ji kalaman mambela gashi ta fara sonsa saboda son da yake mata da kyautatawa ya jawo itama ta fara sonsa har take tunanin da sharri ake yi masa, ashe da gaske duk abubuwan nan ya yi dan haka ya amsa gurbataccen sunan nan nasa na tantiri……..”
Mambela ya katse tunaninta ya ci gaba da cewa “kaltum naga alamar damuwa a tattare da ke dan na fada miki yadda nake a baya. Kin manta mun yiwa juna alkawarin xamu fadawa juna gaskiya, ba xa mu boye komai ba?
Kaltum ina yi miki son da ba xamu xauna yau gobe mu rabu ba, bana yi miki son da xai xo ya shude, ina yi miki son da xan xauna dake harda mutua xata raba mu, xama na dindindin ba xaman boye boye ba ko xaman karya wanda dadewa wani xai fada miki ko ban fada miki b a.”
Wannan karon ma sai ta dago da ido ta dube shi duba na mamaki da ta ji yana kokarin ambaton aure. Mambela ya narairaice ido kamar mai shirin fashewa da kuka y ace “kaltum, anya kuwa ba son ma so wani na ke yi ba har yanxu?
Kaltum ki tausaya min ki tausayawa rayuwata, ko ba kya son dan ADON DAWA ki fara saboda na kasance mai sonki kuma ba xan iya rabuwa da ke ba. Na fada miki gaskiyar halayyata ada saboda xaman gaskiya nake so muyi ni da ke. Mambela ada da mambelar yanxu ba daya bane, ba yabon kaina nake yi ba xan iya kiran kaina nafi duk wani saurayi a garinmu ilimin addini da rikon addini da kuma nutsuwa a yanxu, sabanin da ko karatun sallah ban iya ba sai tsokane tsokane da rashin kunya.”
Kaltum ta dube shi duba irin na rashin fahimta t ace “yaushe ka nemi ilimi? ”
Mambela yayi dariya ya gyara xama yace “Alhamdulillahi da kika tambaye ni. Ina da shekara goma sha biyar a duniya a lokacin na addabi jama’a idan naga dama sai na tsare kofar garinmu ba mai shiga ba me fita a ranar. Haka idan naga dama ni da abokaina ‘yan agulla xamu shiga kasuwa mu raraka duk wani mai saye da sayarwa ba xa’ayi cinikin ba a ranar kuma mu kwashi kayan jama’a mu ci mu xubar da wasu. Sannan idan naga dama xan je bakin kogi in hana kowa kamun kifi a ranar babu wanda xai hana ni kuma, ko anje an fadawa sarki sai yace yarinta ce ke damu na a kyale ni.
Na addabi kowa daga baki har ‘yan gari haka duk rashin mutunci irin na jange saida suka sara min wajen iya fada da kwalba da wukake, gashi fadana baya mutuwa. Dan in cinnawa gidan kara wuta ba komai ba ne a wajena.
Wannan hali nawa yayi matukar tayarwa da mahaifina hankali ya rasa yadda xai yi gashi mahaifinsa ya hana a kai ni makaranta. Cikin dare ina barci a dakina na sha nayi mankawas sai mahaifina ya xo da gardawa uku suka taya shi cicciba ta suka saka ni a amalanke suka fita da ni daga garin xuwa khartum bahari in da aka saka ni a jirgin kasa ba tare da na sani ba sai muka tafi khartum. Tun da daddare muke tafiya har gari yawaye rana tayi sannan muka isa yayin dana bude idona na ganni a cikin jirgi, xan xabura da gudu mahaifina ya cafke ni ya fara lallashina yace xamu je xiyara ne gobe xamu dawo. Na yi ta mamaki amma sai na fara murna saboda naga burni, naga abubuwanda ban taba gani ba. Tunda nake ban taba shiga burni ba , tunda aka haifeni ni a kauye nake sai dai ‘yan garinmu da yawa suna da gidaje a burane suka xuba ‘yan haya amma basa xama a ciki saboda dokar da kakana sarki ya saka cewar dole ne kowa ya xauna a garin dan kada tarihin garin ya rushe, idan kowa ya tafi sai a wayi gari wata rana babu kowa. Tabbas sarki ya fi kowa kudi haka yana da gidajen a garuruwa da dama jiragen ruwa da ake yi masa haya, wasu nasa ne, wasu kuwa ya mallakawa babana, wasu da sunana aka siya du kina da labari sai dai ba’a taba xuwa da ni ba sai daisu ke xuwa. Don mahaifina baya wata uku bai shigo birni ba, yana kuma yawan kai dabino da nono cikin birni ya sayar ya dawo.
Da farko gidan wani amininsa da suka yi karatu tare ya kai ni mai suna sheikh El-Mustapa. bayan mun gaisa aka bamu masauki mu kayi wanka, mu ka ci abinci, muka yi salla. Sai naga mahaifina da sheikh El-mustapaha sun kebe suka dade suna Magana sannan aka ce na dauki jakar na biyo su, sannan muka fita daga gari muka fara shiga dawa a ka kaini wani gida, suka yi min wayo suka sulale suka tafi suka bar ni ban san ko ina ne ba ashe gidan gagararrun yara ne. a nan fa na hadu da ‘yan iskan burni dana kauye wadanda suka fini fitina, saida na raina kaina na tabbatar ashe niba dan iska ba ne.ga ‘yan iskn da suka fini wato wato a cikin dare lokacin da duk ma’aikata suka yi barci manyan suke tashin mu daga bacci su yi ta bugunmu b mu isa mu fadawa kowa ba kuma. Bayan dauri da duka da ma’ aikatan ke yi mana gashi dole mu tashi da asuba mu yi sallah sanman a fara karatun kur’ ani. Daga fatiha ake fara koya mana mu duka babu wanda xai iya karanta fatiha tiryan-tiryan a cikin mu balle mu iya hada baki dan haka tun daga alifun aka fara koya mana, aka koya mana fatiha da karatun sallah da yadda ake yin sallar. In takaice miki said a na shekara biyu cur ban ga wanda na sani ba

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login