Showing 9001 words to 12000 words out of 144367 words

Chapter 4 - ADON DAWA

Unknown   

30 Oct 2024

5074

a cikin robar da gutsurin gursa. Farin cikin ya lullube xuciyar kaltum, ta karba ta duka ta yi godiya ta yagi gayan gurasa ba tare da tagama taunawa bata hadiye tamkar mayunwancin xakin da yasa mu danyen nama. Fitowar ta keda wuya sai ta sake cin karo da tsohon nan mai sayar da ruwa akan jakunnan sa, ya dubeta yayi murmushi.
Ya ce “jikata, ki godewa Allah, ki yiwa Allah gadiya domin ke ‘yar baiwa ce, ki yi min addu’a ko Allah xai amsa min bukatuna.”
Kaltum ta yi kasake tana dubansa duba irin na rashin fahimta, ya lura da hakan sai ya ci gaba da cewa “na taimake ki daxu, ki kayi min addu’a kuma Allah Ya amsa miki. Ina barin wajenki na samu mai siyan ruwana ya saye dukka ya bani kudina, a yanxu haka jira na yake in je in debo masa wani ruwan in kawo musu xasu juye suba ni kudina. Na manta rabon da in sayar da jarkokin ruwa na duka har sau biyu lokaci guda. Yaya sunan ki!”
Ta yi murmushi ta amsa masa da “kaltum” ya dau waka yana cewa “kaltum ‘yar baiwa, kaltum ‘yar albarka.”
Ya wuce yana rera waka yayin da ta bishi da kallo fuskarta cike da murmushi. Ta fara xaiyano mutanen da suka fara sonta a rayuwa. madina, mai ruwa sai kuma xaibu wacce ta bata gurasa yanxu.
Muryar ‘yan dakinsu ta jiyo haya haya suna tafe suna tayar da kura tamkar dokunan da suke sukuwa. Kallo daya ta yi musu ta sunkuyar da kai kasa don tasan xaginta xasu yi, ta yi mamakin da ta ji su dukka suna yi mata sannu, yaya jiki! Ta amsa musu “da sauki.”
Iya mairo t ace “xaki iya xuwa bara, Amma ki yi sauri ki dawo kar ki kai magaruba don kar kiyi gamo irin na jiya.”
To pa, anya kaltum tana sane da halin da ta shiga jiya kuwa!
Meye dalilinta na shiga wannan halin!
ADON DAWA 5
.
Kaltum ta tambaya a bayyane “gamo, wane irin gamo!”
Rakiya t ace “kin fi kowa sani ki ke tambayar mutane.”
Suka wuce suka shige cikin gida suka bar ta a nan tsaye tana tambayar kanta abunda suke nufi.
“shin me ya faru da ni jiya har ake ta min sannu!”
Ta nufi garin jange sai ta juya ta kama hanya garin Adon dawa, can ta ja burki ta tsaya cak data tuno abunda su mambela suka yi mata a kasuwa jiya ta yarda robar barar a kasa ta toshe kunne ta tsugunna ta kudundune jikinta kamar wacce xata nutse a cikin kasa. Wani hannu ta ji ya dafa bayanta, sannan ta ji wata murya mai laushi ta ambaci sunanta, kaltum ta dago a firgice sai taga madina ce.
Ta tashe ta tsaye, ta tambaye ta lafiya! Me take yi a tsugunne a nan! Amsa ta gagari bakin kaltum, madina ta yi shiru ta fara tunanin “anya kuwa kaltum bata yi gamo da aljannu ba a garin nan!”
Kaltum tace “bara xanje.” Ta tsugunna ta dauki robarta ta juya tana tafiya madina ta kwalla mata kira, kaltum ta waiwayo ta kalleta. Madina t ace “kin tabbata xaki iya xuwa bara yau! Domin baki da lafiya.”
Kaltum ta gyada kai t ace “xan iya xuwa” madina ta bita da kallo har said a ta yi nisa sannan ta juya ta shiga gida.
Garin jange kaltum ta je, daga dukkan alamu sun fara gajiya da barar nan ta su. Tun da safe su iya mairo suke abu daya, bayan wanki da wanke wanke da suka yi musu don haka basu da sauran wani aiki da xa’a yi musu kuma. Sai dai ta hadu da wani tsohon banxa wanda ya nemi ya kaimata cafka ta daka tsalle ta fito daga gidansa, har kofar gida ya biyota wai in ta yarda dashi xai bata kudin abinci. Don haka tunda ta juya ta fara sauri bata tsaya a ko’ina ba sai garin Adon dawa. Ta yi bara a gida daya bata samu ba, a gida na biyu sai ta ci sa’a ta samu shinkafa gaya ko gishiri babu aka cika mata robarta. Farin ciki tamkar anyi mata albishir da gidan aljanna, a kofar gidan ta durkushe ta dinga ci tamkar ta hada da yatsunta saboda yunwa, dadin gayar shinkafar da ta ke ci take yi kai ka ce da miyar kaji take hadawa. Shakewa take yi saboda rashin maiko ga babu ruwa a kusa.
Ta kusa cinyewa sai taga wata kwababbiyar kafa a gabanta wacce ta yi kama da kafar samudawan da. Ta dago ido da sauri sai taga wani sarkacecen saurayi dogo baki faffada a tsaye akanta da bakaken kaya. Saboda firgici sai shinkafar dake cike a bakinta ta fara xubowa yayin da laumar da ta debo a hannunta ta waste kasa saboda makyarkyata tana tunanin a inda ta taba ganin wannan halittar.
Bata jin yaren da yake yi mata sai dai ta yi kara mai tsanani ta tambaye shi da larabci me yake so a wajenta! Me tayi masa! Ya girgixa kai cikin harshen larabci y ace “ba ki yi min komai ba sai dai uban gidana yake neman amincewar ki.”
Ta tambaya a gigice “waye uban gidan naka!”
Yayi murmushi yace “mambela.”
Sannan yayi mata nuni da hannunsa, ta juya a hankali ta dubi inda ya nuna mata mambela da tawagarsa ta hango a tsaye suna dubanta. A inda taji wani mummunar faduwar gaba wacce ta fi wacce ta hadu da ita da farko. Kalmar “inna lillahi wa’inna ilaihi ra ji’un” ta ambata yayin da ta xura cikin gidan da aka bata sadaka da gudu. Cikin harshen larabci ta ke cewa “ku taimakeni mambela ne xai kama ni.”
Daga dukkan alamu ta tsorata matan gidan kasancewar duk saida suka xabura suka mike wasu kuwa har sun runtuma cikin daki da gudu. Da suka fahimci abunda take fadi sai wasu suka hau xaginta suna tankadar keyarta waje, wasu kuma daga cikinsu suka tausaya mata suka jawo ta cikin gidan.
Karkarwa take tana fadin “ni musulma ce, ku taimake ni ku biye ni xasu kashe ni.”
Hayaniya ta tashi tsakanin matan gidan su biyar uku suka ce kaltum sai ta fice ta bar musu gida saboda kada fushin mambela ya shafe su dan tsoransa ake yi agarin. Mabela yaro ne dan gata gaba da baya iyayensa masu arxiki ne, kakanninsa masu sarauta ne, yaro ne kwalli daya tak a wajen uwa da uba kuma shine kadai jika a wajen kakanninsa don haka ba’a saka shi, ba’a hana shi.
Daya daga cikin matan biyu da suke so su taimaki kaltum tayi fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, yayin da dayar tace xata fita ta roki mambela ya kyale kaltum kada ya taba ta, amma in har mambela bai yarda ba sai ya taba kaltum to tabbas ba xata bar yarinyar nan ta fita ba sai dai in a cikin dare mambela ya sakawa gidan wuta.
Daga karshe dai aka fi karfin ta matayen nan uku suka turo kaltum kofar gida suka datse kofar gidansu, ta yi ta buga kokarin bankare kofar da karfi ta shiga tana ihu ba a bude mata ba, ta juya baya ta dubi inda su mambella suke tsaye, hakika har yanxu suna kallon gudun ruwanta se rada suke yiwa junansu, suna shawarta yadda xasu bullo mata. Ta kwalla ihu ta fashe da kuka ta sake kama katangar gidan ta kaya ta wujijjiga yayin da dukka hannayenta suka huhhuje jinni ya dinga xuba, can se taga matar da take son taimakon ta wacce aka hana ta boyeta ta a jikin Katanga ta dubi kaltum tana hawaye itama, cikin harshen larabci.
Ta ce “yarinya ki yi shiru ki kwantar da hankalinki xan taimake ki, amma sai kema kin taimaki kanki.”
Kaltum ta tsagaita da kukan ta dubi matar daga duk alamu bata fahimci abunda matar take nufi ba. Matar ta mika mata wani dan karfe karami dogo mai kama da axurfa. Kaltum ta karba ta jujjuya da alama bata san abun ba.
Matar ta sharce hawaye t ace “ki danna gefe ki gani.”
Kaltum ta danna, tana dannawa sai ga wata wuka kakkaifa ta fito fit. Hannun kaltum ya hau karkarwa ta fada a gigice “wuka ce.”
Matar t ace “sake dannan gefen.”
Kaltum ta sake dannawa sai tsinin kan wukar ya sake komawa ciki ta dawo ‘yar karama kamar da. Bakin kaltum na karkarwa ta tambiyi matar t ace “me xan yi da ita!”
Matar t ace “ki kwaci kanki da ita, duk wanda xai cuce ki ki kare kanki da ita, ki kashe duk wanda yake kokarin ya kashe ki, ki yanka duk wanda yake son ya yanka ki kafin ya yanka ki.”
Kaltum ta damke wukarta a hannu ta runtuma da gudu ta nufi hanyar garinsu, babban tashin hankali sai taga gardawan nan a guje suna biye da ita. Ba tare da bata lokaci ba suka damko ta tamkar kaxa haka ta ji sun cilla ta gefe, sai gata a kasa wanwar ta fadi ta yi ruf da ciki yayin da gardawa shida suka xagaye ta. Ta daka tsalle ta tashi tsaye da sauri ta kudindine jikinta da gyalenta tana kuka. Ta na cewa “me na muku, me ku ke so da ni!”
Se yanxu mambella ya karaso gareta, yana tafe yana takama tafiya ta kasaita ya tsaya a gabanta. Ya yi murmushi y ace “ke mai kyau, ya ki ke wahalar da ni ne don ina son ki! Ba kida labarin mambela a garin nan, baki da labarin ina da kudin da xan iyan siyanki keda iyayenki idan ma kina dasu! kar ki manta kasarmu ce nan, arxiki ku ka xo ci. Wuce mu je wancan gidan kafin na illata ki.” Ya nuna mata wani gida da hannu. Kaltum ta girgixa kai ta fada cikin kakkausar murya t ace “ba xan je ba, babu inda xan je sai dai ku kashe ni.”
Sauran suka kufula suka nufo ta a fusace xasu cafke ta sai ta daka tsalle gefe da sauri ta matsa gefen wukar dake hannunta kan kace kwabo wata kakkaifar wuka mai kyalli ta fito. Sai su dukka suka tsaya cak suna kallonta. Ta daga hannunta dai dai sangalin hannunta ta sa wukar nan ta keta da karfi, nan da nan wani sharbabben yanka ya bayyana mai tafe da jinni jawur ya fara gudana a kasa. Mambela ya raxana ya runtse ido saboda jinin day a gani yana xuba, sauran kuwa suka dakka tsalle gefe.
Ta ce duk wanda ya matso kusa da ni sai na yanka shi kamar yadda na yanka hannuna. Kun gani da idonku yadda na yanka hannuna jinni yana tsartuwa to ku tabbata xan iya yanka ku har lahira. Ku rabu da ni, ba ruwana da ku.”
Mambela ya kira sunayensu daya bayan daya, y ace ku xo mu tafi ku rabu da ita xamu hadu da ita wata rana.”
Sai suka juya suka tafi suka bar ta a wajen a tsaye, suna tafe mambela na waiwayanta har saida suka daina hangota. Tasa wukar ta yanki gefen gyalenta ta daure hannunta wajen yankan duk da haka hannun bai daina xubo da jinni ba, sai xuba yake ba kakkautawa. Ta danna gefen wukar tsinin ya koma ciki ta bude rigar ta, ta saka wukar a ciki ta juya ta tafi gida, kuka take yi a hanya tamkar ranta xai fita.
Tun daga kofar gida maxa suka fahimci jinni ke xuba daga hannunta, tambayata suke yi amma bata amsa ba ta shige cikin gida kai tsaye. Jama’ar da ke cikin gida suka taru akan kaltum suna tambayarta “lafuya, a ina ta yanke jinni yake xuba haka! Ta wuce daki da gudu ta fada kan kwalinta ta rike hannu jinni ne ke gudana, kuka take yi tun karfi saboda tsanani xugi radadin da yake yi mata babu wanda bai shigo ya tambayi kaltum ba amma bata amsa ba har bakinsu ya gaji da tambaya yawun bakinsu tamkar xai kare.
Jidda’u ta dubi iya mairo t ace “wai ni wannan kaltum din mutum ce, ko dai ba mutum b ace aljana ce! Ni fa na rasa kanta tsakanin jiya dayau.” Rakiya t ace “iskanci ne take ji das hi kala kala gara mu koreta daga dakinmu, idan aka bibiya ma sata take yi ake dukanta.”
Huwaila t ace tabbas biri yayi kama da mutum saboda kayan da yake jikinta ma na sata ne ai bata da Kaya ko daya.”
Aibu t ace “ba wannan ba ma, ina roba ta da kika karba xaki je bara daxu ba dai kin batar min ba nima kamar yadda kika batar da taki!”
Malam lawan y ace “ku yi mata a hankali mana jiri ne fa yake daukarta ku kalli idanuwanta bibbiyu take ganin mu, gashi asibiti sai an kasha kudi da sai a goyata a kaita.”
Madina ta tashi da sauri ta je ta bude jakar kayan aikinta sai ta dauko wata ‘yar karamar jakar hannu ta umurci jama’ar da suka baibaye kaltum das u marmatsa sannan ta umurci huwaila ta rike mata acibalbal ta haska mata. Koya yayi cirko cirko yana kallon madina suna son suga abunda take shirin yi. Ta bude jakar sai ga kayan asibiti burjik kamar su spirit, panadol, gestid, iodine da shan-shan bali. Ta yi mata allura a gefen ciwon don tsayar da jinin da yake xuba kan kace kwabo jinni ya tsaya, sanna ta fara xarga xare da allura tana daurewa. Ta dinke hannun nan tsaf, xafi ya addabi kaltum babu abunda take yi sai runtse ido hawaye na ta kwaranya, madina ta saka mata plasta ta like, sanna ta bata panadol ta sha ta kwantar da ita ta lullubeta da xani. Jama’a suka dinga mamaki suna tambayar madina ashe dama ita likita ce! Ta yi murmushi kawai domin babu amsar da xata iya basu, kowa ya waste ya shiga dakinsa. Ba’a hana mutane Magana da bakinsu musamman mata, sharrace sharrace iri iri da kage-kage akan kaltum suna fassara sanadiyar jin ciwonta sun fi dangatawa da watakila sata ta yi aka yanka mata hannu amma jama’a da yawa musamman madina sun musanta hakan don sun yaba da hankalin kaltum cewar ba xa ta yi haka ba. Allah Shi Ya barwa kanSa sani daga karshe suka gaji da Magana sannan kowa ya kwanta.
Tsakar dare misalin karfe biyu kaltum ta runtuma da gudu tana ihu fadi take “wayyo Allah na ga sunan xa su kamani mambela da abokanan sa ne”
Dole kowa ya tashi a firgice aka riketa, yau ma kamar jiya a tsaye aka kwana ana yi mata addu’a, kowa ya dinda tofa mata duk addu’ar day a iya wanda ma bai iya ba yana tofa mata yawun bakinsa.
(irin su o’o ken an, ni kuma na yi dariya……. Na ce dai ayi hankali, kar a topa min yawu ……..)
Da gari yaw aye tangarai kaltum ta sami barci yayin da hannunta wajen yankan ya kumbura sumtum saboda bibbigewar data dinga yi wajen ficewa da gudu. Kaltum abun tausayi har hawaye madina take yi don tausayinta.
Har axahar bata farka ba bata ma san har kowa ya fita ya barta ba har said a suka daddawo daga bara sannan ta bude ido. Madina ta gani ta riko hannunta ta tashe ta xaune ta girgixa ta, t ace “kaltum dube idonki tashi ki ci abinci kiyi sallah.”
Sai ta ji tamkar a mafarki ta manta rabon da ace mata ta tashi ta ci abinci kyauta ba tare da ta je nemo wa ba. Ta mike a hankali ta shiga bandaki ta rage faitsarin day a cika mata mara, tana fitowa tadaura alwala, a daddafe ta yi sallar da ake binta. Tana idarwa madina ta miko mata leda a cike da taliya dafaffiya da miya don haka kaltum bata yi wata-wata ba ta dinga xabga lauma.
Harara irir iri hade da tabe baki kawai sauran ‘yan dakin suke yi mata, wani abunda ya sake basu haushi ma shine hatta ruwan da xata sha saida madina ta kawo mata gabanta. Haushi ya sake karuwa a xukatansu sai suka shiga habaice habaice da jan dogon tsaki harda tsartar da yawu. Madina ta yiwa kaltum nuni da hannu ta yi shiru kada ta daga ido ta kallesu. Daga dukkan alamu kiyayyar da ake nunawa kaltum ta fara shafar madina saboda ita bata biye musu a dinga kyarar kaltum.
Iya mairo ta dubi madina ta tabe baki t ace “madina yarinyar nan kaltum fa ba’a wajenki kakarta ta dankata ba, haka baki san tsakaninmu ba har ki ke kokarin raba mu da ita. Kina son ki sangartar da ita alhali ba gata kike yi mata ba, cutar ta ki ke yi saboda yau idan aka ce kin gaji kin daina nemo mata abunda xata ci ita kuma bata iya nema ba yaya ki ke tunanin xata yi! Sai dai ta fara daukar na wasu.”
Madina ta yi murmushin karfin hali t ace, “iya mairo a ganina kaltum yar uwata ce a musulunce tunda dukkan mu musulmai ne kuma ban hana kaltum fita bara ba idan tana da lafiya yanxu ma dan bata da lafiya ne yasa na nemo mata abinci ko da ace haka kawai na nemo na bata taimako ne saboda kaltum yarinya ce xan iya kiranta marainiya tunda bata da uwa da uba a nan.”
Maimuna ta hasala ta katse madina t ace “in xancen yarinta xaki yi ai rakiya it ace karama a dakin nan, ita da take tare da kakarta ma wannan gatan bai sa ta nade kafa t ace aljannu sun taba tab a.” sais u dukka suka hau kunfar baki ana tsuye madina da kaltum. Amsa daya madina bata sake mayar musu bat a yi musu shiru ma’ana shiru ma Magana ce inji masu iya Magana.
Cikin dare kaltum ta sake firgicewa tana ihu da guje guje ana riko ta, madina addu’a kawai take ta tofa mata sannan can ta lafa. Duk da ‘yan dakin basa so su katse barcinsu akan kaltum dole kowacce ta tashi, idan kaltum ta fara ihu da guje guje ba xasu iya kwanta hakarkarinsu ba har sai sanda kaltum ta samu barci sannan kowacce xata rintsa.
Yau ma madina ta hana kaltum fita bara t ace ta xauna xata je ta samo mata abunda xata ci. Kaltum ta nuna xata iya xuwa bara saboda gudun xagin da ‘yan dakin ke yi mata, madina t ace ta yi xamanta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login