Showing 108001 words to 111000 words out of 144367 words
idan yayi alamar zai tambayeta saiya fasa domin kusan kullum idan sukaje gidan a hanyar su ta dawowa kuka ta keyi shi yasa ma baya samun damar tambayar ta, a yau kuwa ya sami damar jero mata dogayen tambayo yi a jejjere saidai kash guntayen amsoshi take bashi ya dubeta ta madubi yayi murmushi yace kina nufin wannan gida damuke zuwa bakya shiga?
kaltum ta gyada kai tace eh nan ne.
yayi murmushi yace yau dai zaki shiga ciki ko?
wannan karon ma gyada kai tayi tace eh zan shiga, Danladi ya fahimci kaltum bata son tambayoyin nan don haka sai yayi shiru.
a inda ya saba ajiyeta anan suka tsaya wato karkashin wata katuwar bishiya dake kallon kofar gidan Tasi'u, kaltum ta bude kofar mota amma bata fita ba, idonta ne cak akan kofar gidan Tasi'u tana fatan kuma tana addu'ar Allah Ya fito mata da Shahida,
Allah mai karbar addu'a sai ga Shahida ta fito burum daga gida sanye da hijabi kuma rataye da wata jaka mai kama da buhun sikari da alama makarantar islamiyyah zata tafi, idon shahida akan motar su kaltum a inda idanuwansu ya kyallaro junansu sai su kayi wa juna murmushi a lokaci guda.
kaltum ta daga mata hannu alamar kira babu
kokonto a zuciyar shahida saita tunkaro inda kaltum take zaune wato a cikin mota tana isowa saita zube akasa ta kwashi gaisuwa, kaltum tayi caraf ta dagota tsaye yayinda take rike da hannunta tana mai ambaton sunanta, shahida kin ini lfy?
ina zakijene da rana fatso-fatso?
shahida tayi dariya, islamiyya zan tafi.
kaltum ta tambaya cike damamaki islamiyyah da rana bada safe ko yamma ba?
shahida tace ina zuwa da safe duk ranar asabar da lahadi a taso mu shabiyun rana mu koma tahfiz karfe biyu zuwa hudu na yamma sannan bayan magrib muje na dare.
kaltum ta gyada kai tace lallai ashe yanzu kinkusa saukewa ki zama malama kamar mamarki?
shahida ta dubi kaltum cike da mamaki domin a iya saninta matan babanta dukkansu biyu jahilaine, to wacce mamar ta take nufi?
ta rike hannun shahida tace kinci abincin rana ko?
shahida ta girgiza kai tace a'a ba a gama ba
shine na taho karna makara idan na dawo zanci.
kaltum tace haba dai ya za'a yi ki iya karatu cikinki da yunwa?
shigo mota kici cake da meat pie da lemo a wajen party aka bani, shahida tashiga bayan mota kusa da kaltum ta zauna,
kaltum ta jawo ledoji dake ajiye a gefenta ta mika mata guda biyu kowanne akwai dankwalan cake da meat pie ga lemon kwali da daurin cin-cin,
shahida ta tsinci kanta cikin farin ciki ta karba ta fara turawa daga yadda take cusawa kasan tana tsananin jin yunwa.
.
Allah sarki, dan halak baya manta alkhairi, ko sharri aka masa sai ya saka da alkhairi, ku dubi yadda kaltum ta sakawa Gg Ftt da alkhairi akan tsiyar da ta mata, haka ma kala,
Kuma ku duba yadda ta sakawa Madina da alkhairi akan erta da irin alkhairin da ta mata.
Da patan xamu ke lura da duk wata gaba na wannan littapin mai kyau domin mu dauka, kuskuren cikin sa kuma mu nemi tsari wajen Allah da kiyayewa. Kamar yadda yau kaltum tayi shigar ta bai dace ba, kamata yayi ko wace irin sutura ta sa ta dauko hijabi ta daura akai ba gyale ba, yadda xai suturta ta a ko ina kuma a ko wannan biki
ADON DAWA 34
.
TRUE LIFE STORY
.
shahida ta tsinci kanta cikin farin ciki ta karba ta fara turawa, daga yadda take cusawa kasan tana tsananin jin yunwa. dakuma marmarin abunda takeci don bata saba ci ba,
tausayinta ya kama kaltum saitaji kwalla ta cika mata ido tana tuna sanda Madina take ciyar da ita asanda takejin yunwa, Allahu akbar, haka duniya take duk abunda ka shuka shi zaka girba idan ka shuka alkhairi shi zaka girba idan ka shuka tsiya ita zaka girba ta bibiyeka 'yaya da jikokin ka,
Madina ta taimakawa miskiniyar yarinya alokacinda take da iko da halin taimako yanzu ga yarinyar tazo ta taimaki yar miskiniyar yarta ba tare da ta taba zaton ko amafarki kaltum zata hadu da ire-iren zuri' arta ba,
kaltum kallon shahida kawai takeyi tamkar Madina take gani a idanuwanta sbd kamarsu da sak hatta farcen yatsun hannunsu iri daya ne, maganarsu, kallonsu, dariyarsu duk iri daya, kaunarta ta sake harde zuciyar kaltum kamar yadda takejin Madina a ranta, shahida ta lura kallon yayi yawa saita fara takura tanajin kunya,
kaltum tayi sauri ta kawar da idanuwanta kasa, can ta dago ta dubi shahida tace ina Mamar kine?
shahida ta kora lemon kwali tace tana gida.
kaltum ta girgiza kai tace ba sa'ada ba ina nufin mamarki data haifeki Madina.
shahida ta dago da sauri ta dubi kaltum yayinda ta tsaya cak daga abunda takeyi tajima bata iya cewa komai ba sai ta fara magana cikin sanyin murya tace mamana Madina ta bata an rasata.
da kaltum ta fara hawaye sai shahida ma ta fara kuka,
kaltum ta dafa kafadarta tace shahida daina kuka mamarki bata mutu ba tana raye kuma bata bataba tana nan.
shahida ta zubawa kaltum ido tana mata duba irin na karyatawa,
kaltum ta sharce hawaye tace kinaso kiganta?
shahida ta girgiza kai tace nasan bazan taba ganinta ba don bazata sake zuwa ba har abada,
kaltum ta gyara zama tace meyasa kika ce haka Shahida?
shahida ta sunkuyar da kai kasa tace ance mamana mayya ce ita ta cinye yaya Abba.
kaltum tayi caraf ta toshe mata baki tace karki sake fadar wannan maganar, kada kisake fadawa kawayenki wannan maganar
sai ayi miki gori, sharri ce akeyiwa mamarki, Madina macece mai kirki ga hakuri Allah zai wanketa in sha Allahu daga sharrin da akayi mata, kada ki fitar da rai zaki sake ganin mahaifiyarki don haka kiyita addu'a Allah Ya dawo miki da mamarki kema ki zauna da uwa kamar sauran kawayenki.
hawayene kadai yake kwaranya daga idanuwan shahida sai gyada kai kawai takeyi, kukane yakecewa kaltum harsaida danladi yayi magana don tausayinsu don tun dazu yana zaune agabar mota yana sauraron su yaji hawaye ya cika masa ido yace kaltum yayakike kuka keda kike lallashinta ai saiki tayar mata da hankali idan taga kina kuka.
get din gidan general tukur aka bude wannan karon ma zukeken saurayin nan ne ta ranan idanuwansa kiri-kiri akan kaltum da shahida kamar yadda suma suke duban sa har ya wuce su, saiya dannan rivas ya dawo baya yazo dai dai inda suke ya zuge gilashin wundon kasa ya kwalawa shahida kira a fusace,
shahida tahau karkarwa ta fito da sauri ta nufi wajensa sai kaltum taji ta tsorita ganin yadda yake harararta saita rufo kofar mota da sauri tacewa danladi direba ya fizgi mota su kara gaba don haka yakara tabbatarwa basuda gaskiya kuma bada alkhairi suke tafe ba saiya tsorata musamman daya tambayin shahida tace bata santa ba, batasan sunanta ba kuma gashi kullum sai ta zo ta kirata tana bata alewa ko biskit kuma tana tambayarta ina mamarta Madina?
ANAN MUKA KAWO KARSHEN LITTAFI NA 3
ADON DAWA
LITTAFI NA HUDU
TRUE LIFE STORY
NA JAMILA UMAR TANKO (JUT)
PART 35
TARE DA SADIN MAA.
DAGA Al-Hada Hada Hausa Book stories
.
misalin karfe biyar na yammacin litinin kaltum yar makaranta sanye take da uniform na makaranta harda jakar littatafanta agoye a bayanta tana tafe a bayan babur na adai-daita sahu Keke napep, bata tsaya ako inaba sai a kofar gidan su shahida ta zaro kudi ta biya mai napep yatafi,
ta kalli kofar gidan tsaf tana tunanin yanda zataga shahida, garin waige-waigenta ta hango wannan zukeken saurayin zaune akan motar sa yana dubanta daga kofar gidansu wato dan gidan general tukur daga yanda yake kallonta kasan akwai magana, bayan duban mamaki da ganinta akwai duban dama ke nake nema babu mai kubutar dake daga wajena yau saikin fadi abunda kike zuwanan kike nema,
bata tsorata ba saima ta harareshi ta kawar da kai gefe ta cigaba da tsayuwa akofarsu shahida, ya tsaya kawai yana duban ikon Allah yayinda kansa yayi masa gingiringim yayi sauri ya cire bakin gilashin da ya ragemasa ganinta sosai yayi sauri yayi kamar ya kwallawa sojojin dasuke yi musu gadi kira su kamo masa yarinyan nan sai ya fasa ya zura mata ido don yaga gudun ruwanta amma tabbas ya kudiri niyyan a yau dai bazai bari yarinyannan ta subuce masa ba sai ya damketa yaji wacece ko waye ya aikota kuma me take nema a wajen shahida.
tsawon mintina ashirin tana tsaye shi kuma bai daina kallon ta ba sai ga shahida da kannenta sun taso daga islamiyya suna isowa wajensa suka duka suka gaishe da makwabcinsu cikin ladabi ya amsa gami da cewa shahida ga bakuwarki can tana ta jiranki tun dazu,
shahida ta dubi kofar gidansu domin can ya nuna nan da nan shahida ta isa inda kaltum ke tsaye suka rike juna cike da murna,
kaltum ta rike hannun shahida tayi mata magana cikin sirri sai shahida ta waiwayo ta kalli gidan general tukur gami da nunawa da hannu abun mamaki sai gani yayi sun dunguma gidansu yana kallon kaltum duba na mamaki yayinda take masa duba na gani kashe ni bana tsoro,
suka wuceshi kai tsaye suka tura katafaren get din gidan suka cusa kai basu dauki dogon lokaci ba wajen amsa tambayoyin sojoji masu gadi kasancewar sunga kaltum da yar gidan wato shahida shahida ce ke gaba yayinda kaltum ke biye da ita tana tafe tana duban gidan yayi mata kyau kuma ya tsaru tunda farfajiyar daga farfagiyar gidan har zuwa babban falon gidan, abunka da gidan yan boko komai an jere shi inda a inda ya cancanta kasancewar babu kananan yara dazasu bata waje dan haka ko ina tsaf-tsaf kamar an tande da harshe, babu kura ko datti ko da yake ba abun mamaki bane kasancewar hadiman gidan suna da yawa mata da maza kowa da bangarenda yake kulawa dashi.
a babban falo kaltum ta zauna yayinda shahida ta kutsa kai can ciki tana rada sallama domin basu sami kowa a falonba kalle-kalle kawai kaltum keyi yayinda idanuwanta suka dira wani rusheshen hoto enlargement amanne a jikin bango da alama dai hoton yan gidan ne kakaf uwa da uba da ya yansu,
nan da nan kwakwalwarta ta fara tuno mata lbr da madina ta bata don bata manta da sunayensu ba tace aranta ga general tukur da mummy hafsat ga babbar yarsu Surayya ga yan autansu tagwaye hassan da hussaini daga nan kuma takasa tantance Abba da mabiyinsa Anas saboda girmansu daya kamarsu daya kayan jikin su ma iri daya a hoton, kuma irin wannan fuskar ta wuce a kofar gida don haka ba tantama kanin Abba ne, taci gaba da jimamin mutuwar Abba a ranta yayinda hawaye ya cika mata ido a yayinda ta ayyanowa Abba da Madina rayuwar aure domin sundace da juna kowannensu kyakkyawane, Abba Allah Ya jikanka ka yafewa Madina itama bata kinka,
kaltum ta fada azuciyarta yayinda taci gaba da duban fuskar Abba da kaninsa kasancewar ta rasa waye Abba a cikin su, shahida ne ta katse mata tunanin da ta keyi tace wai ki shigo inji mummy hafsat tana falonta, kaltum taji zuciyarta ta harba sai yanzu tafara fargaba, ta fara tunanin abunda zai je ya zo, kada fa haryanzu suna kufule da Madina kuma ace suna nemanta su kama ta fushin da sukeyi da Madina ya shafeta gashi ta shigo lungu ko duka ne kafin ta samu ta fito angama dirkarta, ga uwa uba sojoji masu jajayen ido a bakin get sai yanda Allah Ya yi da ita yau kenan, ta fara jero salati a zuciyarta na neman agaji daga rabbis samawati Ya taimaketa ta isar da sakon da ta kudira a ranta ba don ta sami wani abu ba kuma badon ta burge kowa ba sai don ta taimaki Madina ta wanketa daga zarginda akemata domin tunda ta dawo ta kasa samun sukuni da kwanciyar hankali har saita fitar da abunnan aranta zata huta koda fadarshi shine hanyar ajalinta,
shahida na gaba kaltum na biye da ita a baya har suka isa katafaren falo na alfarma a inda idanuwanta ya hasko mata wata lafiyayyiyar mata mai kamala, yanda mummy hafsat ke duban kaltum haka itama kaltum ke dubanta, dukansu mamaki ne fal a idanuwan su,
kaltum bata zauna a kujerunda suke farko-farko ba har saida ta karasa gaban mummy hafsat ta zube kasa ta kwashi gaisuwa cikin fara'a ta amsa tayi mata izinin ta tashi daga kasa ta hau kan kujera saboda sanyin tiles,
kultum ta gyara zama ta girgiza kai tace nan ma ya isa mummy hafsat,
kiran sunan ta datayi shine ya kara mata mamaki kasancewar ko amafarki bata taba ganin mai kama da kaltum ba balle tace yar gidan wane ne ba, ta gyara zama ta dubi kaltum tayi murmushi cike da zumudi ta tambayeta yar makaranta yaya sunanki ?
Daga ina ?
Kaltum tayi murmushi ta amsa sunana kaltum daga nassarawa G R A nake ina makaranta a crensent collage ajina shida, haryanzu dai bata amsa mata tambayanta ba saima hargitsa mata tunani datayi mummy hafsat ta yatsuna fuska kadan tayi shiru can tace ke yar gidan waye kenan?
kaltum tace yar gidan malam sale a gidan alh Adnan muke....
a fusace kyakkyawan saurayin nan ya turo kofa ya shigo damin dama labe yake ajikin kofa yanaso yaji abunda kaltum ke tafe dashi sai yaji ta shiga shirme kuma daman bai yarda da ita ba, ya daka mata tsawa mai firgitarwa har saida kaltum ta zabura ta dafe kirji,
yace mummy kirabu da yarinyannan bata da gaskiya tunba yau ba take zuwa gidan nan tana leke-leke ba, munafuka ce, ki barni da ita kawai in sa su Ashiru masu gadi suyita gana mata azaba harsai ta fadi wanda ya turo ta a mota da take zuwa wani direba yake kawota shine take amfani da shahida tana tambayanta sirrin gidan nan, yau kuma ta shigo da kanta gashi nan tana kame-kame yau sai kin gwammace baki shigo gidan nan ba.
yayinda yake kwanto belt din jikinsa mummy hafsat ta jawo kaltum jikinta ta daga hannu wa dan nata ta dakatar dashi gami dayi masa gargadi kada ya sake yakaraso gabanta balle yataba yarinyan nan da sunan duka, a tsaye yake rike da belt din sai tsuma yakeyi don bacin rai yayinda kaltum ta rushe da kuka hakama shahida kukan takeyi sai kakkarwa jikinsu yakeyi mummy hafsat tana rike da hannun kaltum tana durkushe agabanta, tasa hannu ta share mata hawaye tace daina kuka fadamin meke tafe dake?
waye ya aikoki?
me kike nema?
kaltum ta share hawaye tace babu wanda ya turoni nina nemo gidan dakaina nazo..
ya sake kufula ya cije lebe yaji tamkar ya damko wuyan ta ya shake, mummy hafsat harararsa takeyi alamar karya kariso, ta dago da kan kaltum sama tace yarinya kimin bayani yanda zan fahimceki ban san ki ba amma kekin sanni har kina kiran sunana dasai agida ake fada min balle ince a wajen aikina kika sanni ke yar sakandarine ko jami'a bakije ba balle ince ke dalibatace, meke faruwa ne kaltum ?
Kaltum tayi ajiyar zuciya ta matse hawaye game da gyara zama ta sunkuyar dakanta kasa ta fada cike da fargaba mai yawa don bata san abunda furucinnan nata zai haifarba, farin ciki ko bakin ciki,
awajen Madina naji sunanki ita tabani lbrinki da kwatancen gidanki.
su dukka ukun suka maimaita a lokaci guda MADINA!!!
Zuciyoyinsu cike da mamaki shahida ta mike zunbur ta dafe kirji a inda aka hau kallon kallon a tsakaninsu su hudun ba tare da wani ya kara iya cewa komai ba,
kaltum ta dubi kowannensu daya baya daya ta ce eh Madina mamar Abdul Malik Abdul hakim da shahida tsohuwar matar Tasi'u itace ta bani labarin rayuwarta kakaf harma ta sako zancen nan gidan general tukur da mummy hafsat tayimin dalla-dalla akan rasuwar Abba, Madina ba itace silar hatsarin Abba ba, ba mayya bace bata taba sanin yadda ake maita ba, Madina musulma ce mumina mai rikon addini wacce bata dauki rayuwar duniya da zafi ba, ta fada ta maimaita irin tsananin son da takeyiwa Abba musamman bayan ya mutu hawayenda,
kaltum ke fitarwa saida na mummy hafsat ya linka nata yayinda na shahida ya linka nasu dukka, saurayin ya jefar da belt kasa ya dafe kai yayi wuf ya fice itama shahida sai ta zankada da gudu waje akabar kaltum da mummy hafsat sunata kallon kallo,
zuciyar kaltum ta cika da fargaba kasancewar bata fuskanci matsayin labarinta a wajensu ba, bata san matakinda zasu dauka ba ita dai daman ta kudiri niyyar saita isar da sakon nan dayan biyu ko ta mutu kotayi rai, Shahida ce ta shigo tare da samari guda 2 ko ba a fada ba yayun tane fuskarsu iri daya su dukka sak Madina da alama daya daga barci aka tasoshi daya kuwa shirin filin ball yayi zaije kwallo hankalinsu a tashe tun kafin su shigo cikin falon idanuwansu sun leko suna ta kokarin hasko kaltum zasuyi magana mummy hafsat ta dakatar dasu ta nuna musu alamar suyi shiru sannan ta yi musu nuni da kujeru alamar su zauna, haka kuwa akayi kowa ya zauna yayi carko-carko ga tagumi iri-iri yayinda zuciyoyi suka hau bubbuge-bubbuge wajen tsaro labari daban-daban,
sautin ajiyar zuciyarsu ne kadai yake tashi a falon hakika sun kagu a fara bayani, wayar mummy hafsat ne ta dau ruri yayinda ta mika hannu kan teburin dake gefenta ta dauka ta duba sai ta ambaci kalmar AlhamduLillahi sannan ta danna, Sumayyah tukur ce ta fada cikin farin ciki da tsantsar Kauna,
mummy kina gida?
Gani nafito zanzo na ganki tunjiya nake missing dinki har mafarkinki nayi nace meyayi zafi in hakura da aikin mana yau nazo na yini guda naga uwa ta?
tayi murmushi ta lumshe ido donjin dadin kalaman yar tace kizo ina gida babyna ki karaso da sauri kiga ikon Allah, da baki neme niba daman yanzu zan nemoki,
sumayyah tayi daria tace Allah mummy. Allah Ya sa alkhairi ne,
mummy hafsat tace alkhairi ne ma saikin karaso dai kiyi tuki a hankali ba gaggawa bane,
wata muryace tayi sallama sai dukkansu suka daga kai suna kallon mai shigowan sai ga wani saurayi sanye da bakar riga da wando suit farar riga ce aciki wuyan sa daure neck tied, kafarsa ba takalmi sai dai akwai bakar safa da alama daga bakin kofa ya cire takalmin sai dai yana dan dingisawa da alamar bacin rai a fuskarsa domin dakyar yake magana, abun mamaki sai sukayi kama sak da saurayin da ya fice yafice inji kaltum tafada aranta ko