Showing 3001 words to 6000 words out of 144367 words
tafin hannunka ba ka iya gani, ta duba gabas da yamma kudu da arewa sai taga kamar wani mutum dogo da fararen kaya a tsaye a bakin kofa yana tunkaro ta, nan da nan ta kwanta ta kudundune, jikinta na rawa tana makyarkyata ta fara addu’a kafin ta karasa wannan sai ta kama waccan addu’ar.
Irin wannan raxanar ceta afkawa goggo fattu wacce ta haye kan tudu. Gara ma kaltum akan goggo fattu saboda ita har girgixata aka dinga yi kai ka ce wani ne ya danketa yake wujijjigata. Ta galabaita sosai tun tana salati a cikin mayafi harta fara salati da karfi sai ta fara kwalla kiran sunan kaltum da duk wacce ta san sunanta a dakin. Can kaltum ta yi karfin hali tana cikin mayafinta tace “goggo, menene!”
Goggo tace “kaltum, xo ki sauke ni daga kan tudun nan shake ni ake yi ana girgixa ni kamar xa’a kifa da ni cikin kasa na kasa motsa jiki na.
To pa!!! ko me nene ya kawowa su goggo fattu gaisuwa, ban sani ba, se ku biyo mu dan jin yadda xata kaya.
.
To da patan littapin ya muku?
ADON DAWA 3
BABI NA UKU
A lokacin dasu kaltum suka cika sati uku a bur sudan dole tasa suka fito neman abunda xa su kai bakinsu, mata da maxa, yara da manya kowa ya ja xugarsu suka shiga gari.
Tawagar ‘yan mata su biyar kaltum, rakiya, huwaila, jidda’u da amina suka fankama garin ADON DAWA don yin bara. Suka kuwa ci sa’a suka samo kudi da yawa wanda xai ishesu su ci abincin yinin yau. Kalmar da suke ambata itace “karama fisabilillahi” sai kaga an miko musu kudi. Su kan basu wahid jine wato kamar naira daya kenan, wasu se su basu hamsin jine ficika kenan idan kuwa suka ci sa’a sai a rana daya saisu hada maitan jine daga nan saisu wuce cikin gari maka makan wajen sayar da abinci (restaurant)su sayo abunda suke so, kamar su kisra wato sinasir ko su sayi esha wato gurasa, wani lokaci saisu hada da ful. Ful wake ne manya manya sai a dafa shi ba gishiri ana ci da gurasa. Idan suka samo kudin bara da yawa saisu sayi baitil mandi shima dafaffiyar shinkafa ce fara sai a kwarara madara akai, a yanka tumatiri da albasa, a yanka karas da kabeji, sannan a dora gasashshiyar kaxa a barbada dan gishiri sannan a ci.
Daga dukkan alamu yunwar da ke addabar su ta fara sauki har sun sami karfin da suke iya debo bokitai da manyan darukan ruwa akansu, su niki tafiya mai nisa sannan su samo ruwan da xa suyi amfani dashi wajen wamka, wanki da wanke-wanke. Ta cikin makabarta suke bi sannan su isa gabar kogin da suke debo ruwan.
Ruwan baya shawuwa saboda jajawur ne mai dandanon gishiri.
Jikin kaltum yakan yi sanyi har takan fashe da kuka idan taga yadda ake binne mutane a makabarta. Saboda sahara ce don haka suke yin dogon rami mai xurfi sosai, wanda mai hakawar sai ya shige ciki sosai yayi xurfi.sai an daina hango shi sannan ya miko hannunsa a kamo shi waje dan ba xai iya fitowa ba. Sannan saisu taru su saka gawa, sannan su jera bululluka a maimakon itace saboda yashi ne itatuwa ba xa su tsaya ba. Allahu Akbar!
Allah Ya sa mu cika da imani, Y a jikan musulman da suka riga mu gidan gaskiya.
Ameen.
A yau kaltum bata bisu bara ba saboda tana son ta wanke kayan jikinta kwaya daya kacal, yayi dakun dakun har gefen xanin ya yage don haka ta yanke shawarar sai kowa ya tafi bara sannan ta rufe gida ta cire kayan ta wanke ta xauna ta jira ya bushe sai ta yi wanka ta saka. Da ta tabbatar mata da maxa sun fita daman tun da sassafe ta debo ruwan wankinta, sai ta tsinci guntayen sabulai ta harhade ta ajiye. Suna ficewa sai ta rufe kofar ta fara wanke riga da dankwali da mayafin ta shanya ta koma gefe ta takure tana jiran su bushe.
Ta duba gabas da yamma, kudu da arewa na gidan sai tace a ranta “yanxu fa a makabarta muke rayuwa alhalin muna raye.”
Ta sake duban katon tudun kabarin da yake gefenta ta mika hannu a hankali ta shafa tace, “ko mace ce ko na miji ne a cikin kabarinnan Allah Shi ya barwa KanSa sani. Allah Ya jkansu da gafara.”
Ta ji hawaye yana sirnanowa daga idanuwanta don tausayin kanta da irin matsananciyar rayuwar da take ciki. Ta tuno gwaggo fattu wacce ta kawo ta nan ta ajiye ta ita kuma ta haye ta yi tafiyarta makka tana can tana jin dadin rayuwarta.
Babban tashin hankalin shi ne iyayenta basu san halin da take ciki ba don su a tunanisu tana saudiya kuma tasan mugun halin gwaggo fattu ba xata yi waya ba ko ta aika wasika ta fada musu gaskiya ba sai dai ta bar su a haka, suma kuma iyayen nata ba waya gare su ba balle su san lambarta ta makka su buga mata su tambayi halin da take ciki. Kaltum ta fi jin haushin iyayenta su da suka yarda suka yarda suka bayar da ita aka taho da ita don basa tausayinta. Ta ji ta tsani kowa a duniya kamar yadda kowa baya sonta, sai ta fashe da kuka mai tsananin ta kifa kai a jikin katakon dakin su. Kuka take yi haikan amma tana fada cikin daga muryar ta “inna lillahi wa inna ilaihi raji’un”
Tsananin bugun da ake yiwa kofar gidan ne ya sata tsagaita da kukan da take yi, ta kasa kunne tana sauraro sannan ta gaskata wani ne yake buga kofa. Sai ta mike tsaye ta yi wuri wuri tana tunanin yadda xata yi. Shawara take yi shin ta je a haka da daurin kirji ta bude kofar, sai dai ai bata sani ba mace ce ko na miji! Idan namiji ne ba xata iya tsayawa da daurin kirji a gabansa ba musamman yadda maxan suke ‘yan iska ko wanka ka ke yi idan baka kula ba saisu yi ta liken ki. Haka idan ki ka yi sake a daki kina barci baki killace jikinki ba sai dai ki ga suna ta xirga xirga ta kofar dakinku suna kallonki a dole wucewa bandaki su ke yi, ko suyi ta leke ta hudar katakon musamman dakin su kaltum da yake kunshe da ‘yan mata.
Ta ji sautin bugun kofar ya kara tsamari don haka ta yayimi jikakkiyar rigarta ta saka ta jawo jikakken mayafinta ta sharba a kanta ta goge idonta saboda hawayen da yayi mata kawanya. Ta isa da sauri bakin kofar ba tare da ta tambaya ba ko waye ta ja sakata ta bude game da wangale kofar. Jikinta na rawa ta dubi wacce ke bakin kofar sai taga madina ce tayi sauri ta duka a tsorace.
Ta ce “sannu da xuwa, yi hakuri ban xo na bude miki kofa da wuri ba ina kokarin saka rigata ne.” madina tayi murmushi t ace”lah ai ba komai kaltum.”
Kaltum ta mika hannu xata kar bi himilin daurin kayan dake kanta sannan ga leda a hannunta. Madina tace “bar shi kaltum, ba komai ba sai kin taya ni ba ai na xo gida mu shiga ciki.”
Kaltum ta dawo tsakar gida inda ta cire jikakkiyar rigarta da mayafinta ta mayar kan igiya ta shanya. Madina kuwa ta wuce cikin dakinsu kai tsaye ta xarce kan kwalin shinfidar ta da jakar kayanta a gefe ta ajiye himilin tsummakaron da ta samo. Ta fito tsakar gida inda kaltum ta daga ido da sauri ta dubeta sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Kaltum ta mayar da kai kasa don kunya da girmamawa. Madina tace “kaltum me yasa yau baki fita bara ba!”
Kaltum ta dan yi murmushi tace “kayana ne suka yi datti nake so na wanke sai sun bushe sannan in fita.”
Madina tace “ me yasa sai sun bushe xaki tafi, ki wanke ki shanya sai ki saka wasu kayan ki tafi ki nemo abunda xaki ci, yaushe xa’a ce tun safe baki karya ba har rana tayi yanxu kina jira sai kaya sun bushe!”
Kaltum ta langwabar da kai gefe tace, “ai bani da wasu kayan, kayan jikina ne kadai nake da su, kakata ta tafi da kayana hade da nata ta haye tana cikin wadanda suka tafi makka.” Hawaye ya sarnano daga idanuwan kaltum.
Madina ta tambayeta cike da mamaki tace “au iya mairo ba kakarki bace daman!”
Kaltum tace “kawar kakata ce, garinsu daya tare muka taho dasu, rakiya ce jikarta.”
Tsawon mintina biyar madina tayi tana kallon kaltum saboda tsananin tausayin ta da ya lullube mata xuciya, ta rasa kalma guda daya da xata iya furta mata. Tana tausayin kanta da kanta, amma ta fi tausayin kaltum yarinya karama ba uwa ba uba, ba dangin iya balle na abba a kasar da bata taso ba.
Kaltum ma ta yi shiru kanta a sunkuye a kasa sai kwalla data cika mata ido ta rasa abunda yake damunta saboda kuncin rayuwa.
Madina ta yi ajiyar xuciya ta share hawayen daya cika mata ido, sai ta shiga cikin daki inda ta kwance daurin tsummakaron data shigo dasu ta fara daddagawa tana warewa. Kala biyu riga da siket ta debo ta fito ta mikawa kaltum, kamar an xare mata laka haka ta mika hannu ta karba. Ta kurawa madina ido tana sauraron abunda xata fada, madina ta juya xata shiga daki sai kaltum tace,” wanke miki xanyi!” sai dai babu sabulu, nima guntayen sabulai na tsintsinto a bandaki na yi nawa wankin.”
Madina ta waiwayo ta dubeta sai tayi murmushi t ace “a wanke suke, baki nayi kyauta ki saka nima yanxu nan aka bani su sadaka a garin ‘yan Adon dawa.”
Farin ciki ne bayyane hade da mamaki suka halacci fuskar kaltum ta yi murmushin da har saida wushiryarta ta bayyana yayin da gafen kumatunta ya loba wato (dimple) ta dago da fararen idanuwanta dara dara ta dubi madina ta fada cike da annashuwa.
“anty kin bani kyauta in saka!”
Madina ta yi dariya tace “na baki kyauta kaltum, me ye sa kike mamaki!”
Kaltum, ta sunkuyar da kai kasa ta yi godiya sannan ta fara warwarewa tana duddubawa farin ciki fal a xuciyar ta. Kafin madina ta fito daga daki kaltum ta saka riga da siket cas da ita kuwa kamar dan ita aka saya daidai jikinta sun yi matukar yi mata kyau. Madina ta fito daga daki dauke da wata bakar leda a hannunta tana duban kaltum sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Madina ta yaba da yadda kayan ya karbe ta, sannan ta samu inuwa ta xauna a kasa ba tare da ta nemi wani abu ta shinfida ba. Kaltum ta jefa xanin da ta kunce a cikin bokitin data adana sauran kunfar data wanke riga da mayafinta ta fara sabawa . madina ta kwance leda sai ga kisra da ful.
Madina ta dubi kaltum tace “xo mu ci abinci yarinya”
Wannan kalma ta bawa kaltum matukar mamaki wanda har yasa ta dago da sauri ta dubeta har na tsawon ‘yan dakiku masu yawa ta kasa Magana, can ta yi murmushi.
Ta ce “na koshi, nagode.| madina tace, “me kika ci da xaki ce kin koshi.! Ki saki jikinki da ni ki xo mu ci ai xai ishe mu daman dayawa na siyo in ci yanxu sauran inci daddare ba komai, Allah de bani wanda dan ci daddaren.” Tsananin yunwa ce daman ta addabi cikin kaltum banda kugi babu abinda cikinta yake yi saboda ya fafake babu komai tun a bincin jiya da rana bata sake samun abunda xata sakawa hanjinta ba. Ta ajiye wankin ta goge hannayenta ajikin siket din dake jikinta ta karaso a hankali inda madina ke xaune, cikin kunya da nutsuwa ta xauna yayinda hannunta ya dau rawa a lokacin da take kokarin gutsurar gurasar madina ta dubeta, sannan ta tambayeta cike da mamaki.
Ta ce “kaltum lafiya, meke damunki, ya naga kina karkarwa kuma duk kin tsangwami kanki! Haba kaltum ki saki jikinki ai ba wani abu bane duk wanda ya taimaki wani shima Allah xai taimake shi.” Kaltum ta sunkuyar da kai kasa ta fada cikin sanyin jiki.
Ta ce, “ina mamaki ne saboda tun a mota kowa ta kansa yake babu mai taimakon wani ko dai dai da mukurwar ruwa ne sai naga kin bani sutura kyauta sannan kin siyo abinci kince in xo in ci shine na keta mamaki.”
Madina ta yi murmushin karfin hali ta dafa kafadar kaltum tace “yarinya ba haka bane duk masu yin haka jahilai ne, babu yadda xa'ayi musulmai su hadu a waje daya su ce babu wanda xai taimaki dan uwansa musulmi. Babu mai imani ga duk musulmin daba xai so wadan uwansa abunda ya sowa kansa ba.
Ko a lahira aikinmu ba xai kaimu shiga aljanna ba sai dai alfarma albarkacin masu albarka. Kaltum, ki cire wannan mugun tunani a ranki, ki dauka a xuciyarki duk runtsi duk talaucin da kike ciki komai kankartar abu xaki taimakawa wanda ki ka fi ko da babu mai taimaka miki domin Annabi Muhammad (S.A.W) y ace “hannun da yake mikawa shine a sama, ya fi hannun da yake karba shine a kasa.”
Babu wanda kaltum take yi sai gyada kai hakika tana gamsuwa da abunda madina take fada mata. Suka ci, suka koshi suka kora da ruwa sannan kaltum ta yi godiya ta tashi ta je ta ci gaba da wankinta, ta dauraye ta shanya. Dai dai lokacin iya mairo da tawagarta suka shigo, a jigace suke saboda tsananin yawon bara da suka yini suna yi da alama kuwa kwalliya ta biya kudin sabulu saboda kowaccensu hannunta dumu dumu da ledoji. Cikin fara’a kaltum ta tare su gani da yi musu sannu da xuwa. A tunaninsu kwadayin abunda suka samo take don haka kowa ya tsuke fuska babu wanda ya amsa gaisuwarta sai ma dai kauce mata suke yi suna kewaye ta suka nufi daki.
Iya mairo ce ta tsaya tace mata “sannu isashshiya ‘yar gata wacce bata iya wahala ba, kowa ya fita nema ke kina kwance a gida wa xai nemo ya baki a wannan marrar da nafsi nafsi babu mai taimakon wani, keta wanki ma kike yi. Waye ya baki aron Kaya ko kin fara tsayawa sai kinga ba kowa ki bude jakunkunan mutane ki daukar musu kaya! To kada ki sace kayan wani a kama ki kice kin sanni ko kice ni kakarki ce.
Rakiya ma ta leko daga daki ta tsoma baki tace “tun shigowata nake kallonta daga gani kayan nan na wani ta sato saboda bai yi kama dana bola ba kuma bata fita bara yau ba. Tun da safe ta debo ruwan wanki bata kara fita ba.” Sai sauran ma suka tsoma baki babu wacce bata yi mata cari ba a cikinsu.
Kaltum tadago da sauri ta dubi madina yayin da madina ta yi mata nuni da hannu alamar ta yi shiru kada tace komai. Kaltum ta sunkuyar da kanta kasa sai wani kuka na takaici ya kece mata marar kakkautawa. Ta koma gefe ta tsugunna tamkar almajirarsu yayin da kowaccensu ta shiga daki ta baje ledar abincita suka ci. Wasu shinkafa ce da miya, wasu baital mandi, wasu taliya, wata macaroni. Abun mamaki sai suka dinga yiwa madina tayi wai ta xo su ci. ta ce ta gode a koshe take amma babu wacce ta tuntubi kaltum.
Wani kululun takaici ya tsayawa kaltum a wuya ta fara tuhumar kanta tana tambayar xuciyarta wane irin mugun hali nake yiwa mutane haka suka tsane ni! Me nake yi wanda kowa baya sona aka tsane ni!”
Sai tayi xunbur ta mike ta shiga daki wajen shinfidar kwalinta ta dauko robar cin abincinta, yayin da kowacce ta dinga kare abincinta wasu ma suka fara daure ledar abincinsu a tunaninsu rokarsu xata ta yi, ta dube su duba irin na takaici ta langwabar da kai ta matse hawaye sai ta fice, ta yayimi gyalenta ba tare da ta yiwa kowa Magana ba har madina da take xaune a tsakar gida a wajen da suka ci abinci har yanxu bata tashi ba.
Fitarta kofar gida keda wuya sai ta tsaya cak ta dubi gabas da yamma, kudu da arewa babu abinda take gani sai tulun bola da kabarurruka yayin da gabanta kuwa katon kogi take hangowa yana ambaliya. Ta ji a ranta tamkar ta fada kogin nan ruwa ya hadiyeta ta mutu ta huta da bakin cikin rayuwa sai kuma ta tuna da wa’axin da aka yi musu a makarantar islamiyya cewar duk wanda ya kashe kansa ya mutu a kafuri. Ta juya ta dubi kabarurrukan da ke gabanta sai tayi sha’awar dama ace ita ce a ciki a mace ta mutu an binne ta. Ta ji a ranta rayuwar wadannan bayin Allah da suka mutu ta fi mata irin rayuwar da take yi a duniya jin dadi da kwanciyar hankali.
Kamar daga sama ta ji Magana a bayanta, ta waiga da sauri saida suka hada ido da madina.
Ta ce “kaltum ina xaki je!”
Kaltum ta saki fuskarta ta yi murmushin karfin hali. Ta ce “xan je bara.”
Madina tace ki kula da kanki, shawarar da xan baki itace kada ki je garin jange saboda kin ga ke yarinya ce akasarinsu kuma ‘yan iska ne gara ki je garin Adon dawa tunda su na da musulmai xa su fi tausaya miki. Hadari ne ma ki dinga tafiya ke kadai ba’a tawaga ba saboda irinku suke so ‘yan mata ba kamar mu ba manya ba damuwa.
Kaltum ta gyada kai tace “to anty bari in je garin Adon dawan.” Ta juya ta tafi yayin da madina ta dade a tsaye tana kallonta har saida ta kure ta daina hango ta sannan ta girgixa kai don tsananin tausayin kaltum ta shiga gida.
Kaltum tafiya take amma fa har yanxu bata fasa kuka ba harta iske gidajen Adon dawa. Ta fara shiga gida daya bayan daya, Kalmar da take ambata itace “karama fi sabilillahi”
Da alama yau bata fito da sa’a ba daga inda ake kyaleta ta yi ta bara ta gaji ta tafi da kanta sai inda ake yi mata korar kare. Ta yanke shawarar tunda yamma tayi yanxu duk maxan suna kasuwa bari ta je can ko Allah xai sa ta dace. Kaltum ta kama hanyar jim arab, nan ta iske dandaxon maxa kungiya