Showing 3001 words to 6000 words out of 62773 words

Chapter 2 - GIDAN GANDU

09 Oct 2024

4437

ba,dan haka babu inda zamuje,in labiru kuke zance ma,dazu wasu samari suka kawomana kara wai sun nemeshi sun rasa a baking rafi lolacin da suke shan rake dazu,dan haka ku tattara naku ya naku kubar nan wajen tun wuri"
Cikin sanyin jiki na rashin sa'a suka bar wajen,wanda dama shi bashari baiyi magana ba,inda wajen tsara yan matane da bleaching toh ya rufe kofah,amma harkar yan sanda kam,matsoraci ne shi sosai na bugawa a taro.
Fitowa sukayi daga police station suka tari acaba wanda zai kaisu asibitin da aka kwantar da hanifan,nan ma saida akayi ja inja da mai adaidaita sahu kafin ya daukesu,suna cikin tafiyane bashari yagyara zama yafara magana wacce baiyi ba tun sanda aka shiga police station din,
"AI baba umaru in fada maka,mutanennen basuda imani,cewa muka cemusu anyiwa fah yarinya fyade amma ji yanda suke wani nuna halin ko inkula,hmmm abin duka babu sanda"
"Dallah can yimin shiru da fuska kaman ta sabuwar fatalwa,waiku adole yan gayu,duk kun shafa mai kun mele fuska kaman wanda aka bi da dutsin guga,zaka ce wani abin duka babu sanda in anbaka sandan uban me zaka iya idan an baka sandan,akwai abinda ka iya ne banda shegen zuwa wajen yan mata,duk wani dan kudinku anan yake karewa da kuma sayen tsukakkun wanduna"
"Kai baba umaru ku bakwa gane zamani,idan ta ganka baki babu wanka ai babu rabin zance,ai idan ta ga fuskarka fara tas ga kuma wandonka irin sabin gwanjonnan yanzu zakaga ana love wallhi in ba kaiba sai rijiya"
"Kai bashari zaman mu lafiya kayimin shiru anan wajen tammmm"
Shiru kuwa yayi da bakinsa bai sake cewa komaiba har suka iso asibitin da aka basu gadon.
A wajen cashier suka hadu dasu inna larai a tsaye suna jiran layinsu ya iso saboda ganin likata(kasar tamu kenan allah yah ya fiddamu cikin wannan hali).
Kudin wajennasu bai isa ba ,saida baba umaru yaciro guntun sanjinsa kafin aka bawa mai karbar kudin.
Bayan sun samu an basu gadone,baba umaru yah kalli kawu shehu yana mayar masa yanda sukayi da yan sanda a police station dazu,tun bai karisa jin mai ya faruba ya fara masifa saboda tsabar ransa ya baci,
"Hmm dama nasan za'a rina,wai an saci zanin mahaukaciya,duk sun bata yayannan basuda aiki sai jawo magana acikin gari,kowa acikin su bayason laifin dansa toh yanzu wa gari ya waya ,gatanan ina tatura yarinya kwadayi anyi mata aika aika tabar mutane da wahala"
Inna larai ce ta goge idanunta da yacika da hawaye ta dubi kawu shehu cike da masifa tafara magana,
"Kai shehu ya isheka haka,kawai zaka samu mutane da shegiyar masifa,zaka ce wani mun b'ata y'ay'a ,aikai suka iyo kaidin na allah ko kanace bamusan mai kake aikatawa,dama wanda yayi ai sai anyi masa,kuma dama kyan d'a yagaji ubansa,kai suka iyo,dan haka kadaina wani jingina laifin akaina eheee"
Kunyace takama kawu shehu ganin yanda inna larai tafere baki ta masa wankin babban bargo da masifa kaman d'anta gashi dakin Da'aka kwantar dasu da mutane.
Sallama baba umaru yayi musu ganin yanda abin yafara zama na tone tone maimakon zaman jinya,fatan samun lafiya yayi musu yai hanyar gida na fatan allah ya kyauta aransa.
Yana shiga gida inna RAMATU(matar baban SAMEEMAH ,uwar su sameerah )ta tari baba umaru da barka kaman ba itaba,da Mamakin sa yah kalleta saidai ya boye baice komaiba,ruwan sanyi ta kawo masa da shinkafa fara da mai da yaji da akayi da ranar.
Saida yah wanke hannun sa kafin yafara garwaya shinkafar dan dama da yunwa yadawo gidan ,kuma yayi arba da tsautsayin daya faru,dawowa tayi ta samu waje ta zauna tana gyara zaman dan kwalinta,
"Ah dama nace baban su ATIKA,(haka take cemasa),kaman dakai aka tafi da hanifa asibiti koh?"
"Eh dani ne ya akayi?"
"Meyafaru ne acandin?"
"Shiyasa kika tareni da fara'a harda ruwan sanyi da kawo abinci a kwano mai murfi dan kiji labarin abinda yafaru koh?"
"Haba baban atika ya zaka ce haka kuma naga dan ka fadamin ba laifi bane koh"
"A gunki kenan ba,toh bazan fada ba,waiku mai yake damunku ne bakuda aiki sai kowa buri yake yaga wani abu yasamu dan uwansa yadora agaba koh,haka kuke daga ku har y'ay'anku kamar an garwaya an raba"
"Kaga baban atika nifah ba cewa nayi kafara min wani zance na banza da wofi ba,kawai tunda bazaka fada ba shikenan,dadinta ma da su sule kaje,zan tambayesu su fadamin,kuma dama dazu na kara kudi an dad'o maggi na ashirin saika bani kudina na fasa yafewa"
Kade zaninta tayi tana cika kaamar kububuwa ta bar wajen,dan tsabar takaici daya shak'i baba umaru jijjiga kai kawai yayi yana rufe kwanon abincin,dan ji yayi duk abincin ma ya fita a ransa.
(Allah ya shirya matan mu a yanzu,musamman ma kauye koh babban gida wannan matsalar tafi yawa a irin wannan muhallen).
A kofar su larai kuwa kowa yah watse yakama harkar sa sai matan dasuke karkashin inna karima su kadaine a kofar ana maida abinda yafaru ana yada shewa,Hansai ceh matar dan baba umaru na farko manjo wanda yatafi cirani bayan ya saci kudin sarkin noman anguwar tasu ana nemansa,wanda yanzu y'ay'anta biyar kenan,duk suna gidan suma ana fama dasu.
"Hmm ke kiji sai mukaji abu yafaru kuma?"
Itama wata a gefensu ce ta cafe tareda cewa,
"Naga dama ita ke likawa labirun,yanzu gashinan ai yayi mata aika aika,maganinta"
Wata a can gefece tana bawa danta nono ta kalli MAIRO wanda ita ta gama magsna yanzu,
"Ke mairo yanzu kece mai cewa wani wai allah yakara dan anyiwa Y'arsa fyade?,ai gwara ita dole akayimata naga ke yar ki HAFSA,amai muka ga tanayi akaje aka dawo kuwa ashe cikine da ita,kuka shirya ke da ita da asuba kikaje aka zubar mata ,harda cewa wai shawara ce take damunta"
Kunya ce ta ishi wanda aka kira da mairon wanda tafara masifa cikin borin kunya itama ta fara maidawa wanda tayi maganar da nata laifin,
"Naji dai ina Y'a tace kawai tayi,kuma hakan bazata sake faruwa ba,amma ba'a kama uwata da makocinsu ba a daki ina"
"Ke dan kutumar ubanki mairo mutsaya iyah kan gidannan banda sako gidan kowa,dan wallhi inta hakane kowa bazai ji dadi ba in toza'afara'za'afara"
"Hehe dama in baki yasan mai zaice bai san mai za'a mayar masaba,kan me uwa da wabi duk uban abinda za'a fada a fada ba tsoro nakeba,abin kunyane kowa gaba yabashi anan wajen ba baya ba,dan babu wanda abin kunya bai lullubeshi ba anan wajen,dan haka kawai ayi sha'ani wai na birni ya cuci na kauye".
Ganin abin zai bacine yasa inna karima korar kowa daga dakinnata ,kowa yayi hanyar kofarsa yana maida nasa zancen.
A wajen su sameemah kuwa lokacin da suka dawo daga gidan alhaji Sama'ila har sunyi hanyar gidan kungiyar tasu,ta bada umarnin a nufi hanyar gidan karagiya inda aka kai labiru dazu da safe,mashin din suka k'uza suna sakin hayaki a duk layin dasuka wuce kafin suka yanka cikin gari inda zai kaisu inda yake.
A zaune suka sameshi yana rarraba ido fuskarsa ta kumbura suntum saboda dukan dayasha,mamakine kwance akan fuskarsa daya ga sameemah a wajen,
"Yayah labiru kayi Mamakin ganina ne,nice dai y'ar kanwar taka"
"Amma mai kike a wajennan,ko dagskene da ake cewa kece shugabar yan dabar garinnan?"
"Kwarai kuwa gashi ka tabbatar da kanka,kafin mukai ga nan,ajiye wannan wasan a gefe muyi abinda yatara mu,miyasa ka aikata abinda nake zarginka dashi"
"Makike zargina dashi iyee,kaika jimin yarinyar nan"
Murtuke fuska sameemah tayi kaman ba itace take dariya yanzu ba,wani irin wawan mari ta sauke masa akan fuskar sa saida dungura jini yana fita ta hancinsa,komawa yayi ya gyara zamansa da Mamakin irin naushin daya fito daga hannun nata kamar wani babban majiyin karfine ya dakeshi,
"Yanzu zaka bani amsa koh kuwa,mai ka aikatawa karamar yarinya dazu da safe?"
Karkarwa jikinsa yafara yana rarraba ido ganin abun dagaske ne ba wasaba,
"Iyyeee na'am wai nnnni .........din"
"Oh tambaya kake,kai burgu ku dan taba lafiyarsa na dan minti talatin da alama bayason lafiyar tasa"
"Ahah su tsaya,kiyi hakuri wayyo,dama kullum tana wajena,ina yin hakuri shine har jiya nakasa toh yau dana ganta shine,na saya mata shayi da biredi bayan ta shanye najata shagon ilu dama bai bude ba,na biya bukata ta,shine kawai"
"Mesunan abinda ka aikata kenan?"
Saida yayi dan shiru ganin zata sake zabga masa wani marin yasashi saurin cewa,
"Fyade,fyade sunansa"
"Kowa yaji laifinsa ko baijiba?"
"Eh munji shugaba"
Suka amsa dukkansu a tare,
"Kai arnen dawa dakkomun abinda nasaka kamin dazu nasan yanzu yayi yanda nakeso,cikin sauri kuwa yabar wajen ,bai dade ba sai gashi da wani kwano abinda yake cikinsa yana turiri,
"Kai burgu kucire masa wando yanzunnan"
Aikuwa kaman jira suke cikin kankanin lokaci suka sutale masa wando,tun baisan mai zai faru ba yafara ihu yana rokonta,
"Shshshsshdh,katsaya da ihun tukunna bari nayi maka wani gargadi,idan ka kuskura nayi maka hukunci kaje gida aka tambayeka mai ya faru ka kira sunana.......,hmmm,saina rabaka gabadaya da abinda kayi amfani ka aikata laifin"
Tun bata gama masa gargadin ba,ta juye soyayyan mangyadan da aka dauko daga wuta akan gaban labirun,cikin kankanin lokaci kuwa fatar wajen tafara sutalewa tun daga kasan cibiyarsa har zuwa rabin cinyoyinsa.
Su kansu yarannata saida suka girgiza da hukuncin da sameemah tah aikata,
"Kuje kujefashi a bayan layin unguwarsu inda yan gidan zasu ganshi,uwarsa saitayi jinyarsa tunda ita ke daure masa kan macijin yake wasa da wutsiyar"
Tabbbnnnnnnn,lallai sameemah!!
Mucigaba dai mutane Nah🤣🤣😂🤣

❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤

Kar ku manta da

#comment
#share
#like
#follow.

____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤


Wattpad username:SAKHNA03


❤04❤

Ihu yake yana jijjiga kai tun yanayi da karfi har yazamo baya iyacewa komai sai nishi dayake saukewa kaman mai nakuda tazo gargara dan wahala.
Burgune yakalli sameemah wanda har yanzu fuskar sa bata dawo dadai ba da laifin daya ga shugabar tasu ta aikata,
"Amma shugaba wannan hukuncin dakika masa baiyyi tsauri ba kuwa?"
"Toh ka rama masa mana,saina san kaji babu dadi da abinda na yanke,kai wai yaushe kuka fara ma wannan challenge dinnna wa,ne,banason wani iyayi da nuna tausayi na karyar banza a fuskarku,dan tsabar munafurci har kune masu cemin kuna tausayi,da Y'ar gidanku ya farde,ai bansan sanda zakuyi masa aika aika ba saidai naji anakirana a police station naje na fitar da ku,aikin banza kawai inzaku kaishi inda na sakaku ku kaishi in kuma bazaku jeba ku fadamin saina kaishi da kaina"
Sunkuyar dakai sukayi dukkansu suna bata hakuri a tare.
Dalewa tayi kan mashindin burgu saida ta burka yafara kara kafin tace,
"Zanje gida na dawo,ku tabbatar kun shirya shagalin kafin na taho,bayan kun gama cika aikin"
"Bakomai Shugaba bakida matsala"
Fisgar mashin din tayi ta bule kura kafin tayi cikin gari da mungun gudu.
Bayan ta bacewa ganinsune burgu yajuyo yah kalli su arnan dawa tareda cewa,
"Kai dauko buhu musakashi muyi saurin gama aikinnan,dan komawa wajen shagalinnan,kunsan idan harta gama abinda take tariga mu,zuwa toh wallahi bazamuci wannan ganimar ba,nikuwa yanda yawuna yatsinke da wannan gashsshun kajin inban samu na yaga ba akwai matsala"
"Hakane ogah burgu nima tawajennawa haka take yakamata mu hanzarta"
Daukar labiru sukayi wanda yake ta yada kai dan wuya suka zefashi a wani katon buhu,bayan sun dorashi a mashindin arnen dawa suka dau hanya sai anguwar su labirun,wanda sannan yamma tayi,bayan layin ya dauke sawun mutane. Saida suka samu wani rami gefen kwatar gidan kafin suka jefah shi suka tafi.
Parker mash in din tayi a kofar gidan ta shiga tana fed'uwa tareda yin wakar koroso,larai tasamu a tsakar gidan wato matar yayansu manjo wanda yatafi cirani ,wanke hatsin tuwo take a kwaryah,saboda neman magana sai kuwa tace,
"Mutum bashi da aiki sai halayyar maza hakanma a mazan tantirai,allah dai yah shiryah"
Tsayawa sameemah tayi daga shiga dakinnasu na yan mata,kafin ta jiyo ta kalli kulu din,
"Kehh mekikace yanzunnan,kuma Sannan kifadamin dawa kike?"
"Aikin banza Inna fadi da wanda nake ma uwar me za'ayi,karkarinta dai borin koro kunya ko za'a dakeni ne yanda akeyiwa yan dabar iyee"
Jijjiga kai sameemah tayi kafin tayi wani bolll da kwaryar hatsin a kasa.
Ihu larai tafara tana kururuwa tareda durawa sameemah ashar duk wanda yazo cikon bakinta.
"Yar bantan uba ni zaki zubarwa hatsi ko uwarki ceh ta sayamin dazaki zubarmin?"
Shiru ta hadiye wani yawu mukut,ganin yanda sameemah ta saita y'ar wuk'a a makogaranta,
"Kika sake saka uwata a zancenki saina maida y'ay'an ki marayu kuma na maida manjo gwauron karfi da yaji,ki kuma sake ki gani zaki ga ko karya nake ko a'a,banza karya mai bin mazan wasu kawai"
Kwalo ido tasake yi kafin ta ce cikin mamaki ,
"Dama kinsani?,dan allah karki fadawa manjo wallahi yankani zaiyi"
"Banza karamar y'ar iska ashema tsoronsa kike ji,shine ni harkika samu damar shiga harka ta ko?"
"Ahah kiyi hakuri bazan sake ba"
"Kima kara mana kiga aiki da cikawa,mtswww"
Wucewa tayi ta bar kulu tana d'ebe hatsin dake kasa har Sannan jikinta rawa yake saboda kashedin da sameemah tayi mata.
Bakowa a dakin sai salma tana ta danne danne a irin wayar zamaninnan ,daga ganinta kaga irin matan nanne masu ji da kansu duk da cewa kyakykyawace dan inka dauke sameemah duk matan gidan ta fisu kyau,hakanne yasa take harka da manyan alhazan ds yan gidan basayi.
Itah ceh y'ar larai ta fari wato yayar su hanifah,kwanan ta dawo daga bikin kawarta wanda akayi a abuja sune manyan kawaye.
Sameemah koh kallonta batayiba balle ta yimata sallama,kayan jikinta ta cire kafin ta fito daga dakin daga ita sai towel a jikinta.
Fitowartane yayi dadai da shigowar SULEH MAYEH (yayan labiru) gidan abokin manjo wanda tun bayan tafiyar manjo cirani bai daina shigowa ana gaisawa ba.
Lashe baki ya hau yi yana kare jikin sameemah da kallo,dawani gashin bakinsa buzubuzu ga idonnan yasha kwalli dakyar kake ganin kwayarsa dan rinewar idon ,saboda shan sholi.
'Yawwa yau na taki sa'a gaskiya tunda idona yai arba da wannan d'anyar kazar yau,kai rabbana yayi hallitta a wajennan,kaiiii dolema naje nasamu tsohonnan wato baba umaru,na mika yan kudina a bani ke mushiga daga ciki tunda naga ke baka d'ebi romo ka wuce"
Koh kallon inda suleh maye yake bata kallah saima neman ruwa da take wanda zata watsa a jikinta saboda zafin da'ake.
Wani dan yarone yazo wucewa ta kirashi,
"Kai zo nan,jeka kofar uwarka ka d'ebo min ruwa kace injini neh"
Da saurin jikinsa kaman zai kifah da kasa ya karba yayi kofar tasu da gudu dan cika umarnin nata.
Suleh ne yadameta da magana,dan shi a ganinsa tana jinsa,wani shegen kallo ta juya ta watsa masa kafin tace,
"Kai kasan allah duk da nasan ba saninsa kai ba,toh ka tattara yan kafafunka kabani waje,koh kuma yanzu nayi maka wani naushi da saina bajeka anan wajen saidai a zo a daukeka,kaga tsohuwa sai tayi jinyar majinyata biyu"
Karbar ruwan tayi da yaron ya kawo mata ta shige bandaki tana jan tsuka.
Saida ta gama shirinta tsaf kafin ta nufi gidan kungiyartasu,lokacin ana shirin kiran magriba,wasu masallacin kam ma sun shiga amma itah koh a jikinta kaman ma an ce an yafemata sallahr.
Lokacin da ta isa su burgu sun gyara wajen tsaf kaman ba shiba,a kijerar da aka tanada ta hakimce tana wani shan kamshi ,kayan ganimar aka bajemata a gabanta.
Kajine sun sha suya mai kyau jajaye sai turiri suke,gakuma lemo masu sanyi dakuma duulah mesaka mutum ya jishi a sama,wata kururuwa su burgu suka buga dan dadin ganin irin abunda aka kawo.
Hannu tasa ta yagi cinya guda d'aya tasaka a baki kafin kuma kowa yafara yagar nasa rabon,kid'a akasa mai irin buga sautinan kowa yana rausaya wa yana cika bakinsa da d'i,
"Kai shugaba jar wuyah mufah tunda muna kungiyarki mun more fah,wace kungiyace zakaga ana siyan kayan dad'i ana cin wannan dad'in in ba kungiyar seemah jar wuyah ba.
Wani rausayah seemah jar wuyah tayi irin na wanda aka zigashi dinnan,
"Hmm aiku bari kawai saima idan an samu wata hanyar ta bud'e,harka tazo saidai kuji ana kungiyar seemah jar wuya sai ana cika form kafin a shiga"
"Heeeeeeehuuuuu sai seemah jar wuyah"
Dukkansu aka dauki ihu tareda shewa ganin irin kirarin da suka yi mata yah shigeta sosai.
Salame ceh a zaune ana ta tad'i itama a nasu gidan da yamma itada surukanta da kuma kishin balbali,
Hira akeyi wanda duk rabin hirar tasu gulmar gidan gandune, d'aya matarce wadda duk zancen da akeyi bata saka bakiba saida ga baya tace,
"Babar labiru wannan gulmar dakukeyi bata da amfani ko kadan,abinda yake faruwa a gidan abune daya zama tamkar ruwan dare a namu sauran gidajen musamman ma kauyukan mu da kuma iyaye masu san ransu wanda daka yiwa y'ay'an su fa'da gwara komai ka musu,addu'a yakamata mu dingayi ba wai mudinga yayata lafin y'an uwanmu bah"
"Kehh Wallahi kiyimin shiru banason wannan iyayin naki da kutufifi,zaki wani zo kina yimana wa'azi an fadamiki nasiha mukeso,toh muje masallaci mana...........,"
Wani yarone yah shigo da gudu yana kiran salame da karfi,
"Babar labiru babar labiru,wai kizo inji wasu a waje,wai buhu suka gani a bayan gidan can yana motsi,suna budewa sukaga labiru ne wai an konashi da wuta a cikin buhun"
"Kuntun ubah kai meka ce?,dagaske kake Kuwa,yau nashiga uku na lalace wane la'ananne a fadin garinnan ya yiwa labiruna haka wayyyooo na lalaceh"
Amma babar labiru kamata yayi kiyi addu'a ba ki dinga ihu ba"
"Dallah rufemin baki yar kan uwa shegiya wato bazaki barni da wannan wa'azinnaki ba koh,yanzu haka ma dake aka had'a baki inaga,dan dama duk bakin ciki kuke min dani da y'ay'ana"
Ganin fad'an na neman komawa kansune yasa kowa tayi kofarta ,ita kuwa ta rufa hijabinta batasan ko dadai ma tasaka ba,tayi waje har sannan bakinta bai yi shiru ba.
Saida su seemah suka kai wajen karfe dayan dare kafin kowa yayi tunanin hanyar tafiya gidan su,mashin din burgu ta dauka tayi gaba ,yana ta magana amma ko juyowa batayiba bare yasa ran zata dawo masa da mashin din.
Hanyar anguwar su sameemah ba kowa haka ta bi da wannan uban daren ga kuma duhun allah da annabi daya lullube sararin samaniyah,a wannan lokacin babu yanda za'ayi mace kamar kowacce ba irin sameemah ba tafito da irin wannan daren kuma a mashin ita kadai.
Tana cikin tafiyane taji alamun wani abu yah rike mata tayar mashin,tsayawa tayi cak da mashin din amma shiru bataga kowa ba,Murmushin gefen baki tayi da tagane mai hakan yake nufi,
"Tabbb gaskiya an rainani,yanzu harni wani zai rikemin tayar mashin,toh me akeso nayi ihu ko kuma zefar mashin din na barshi a wajen,kafin gobe wani yah lallab'o yasace koh?"
Tura mashin din tayi sai kuma taji tayar ta tafi,wani yunkuri tayi tasake tayar da mashin din kafin tace,
"Yadai fi muku,a saukake dan ni ba addu'a zanyiba dama tunda ba iya wa nayi ba,kuma ba ihu zanyiba tunda ba ganin ku nakeba,kunga bata lokacinku kueyi nima

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login