Showing 54001 words to 57000 words out of 62773 words
tana masa wani kallon nasan mai yake faruwa.
Bayyi mata magana ba sai tsayawa da yayi. Yana kallomta.
Sameemah ceh da haushi yakamata ganjn zasu fara fadannasu a gaban yara tace,
"Wai kekam inna larai meyasa kike hakane,ke har kina da karfin gwiwar dazaki yi wata magana akan laifin wani,hakan ma mijinki,nagan daman kin san yana aikatawa ba wai baki sanj ba,kawai yanzunne akka kamashi hannu dumu dumu,kaman yanda kema yasan halin dakike aikatawa.
KO kin manta lokacin da kike bin manyan anguwa akan zaki dawo dakinki lokacin da shima ya ganki da malam mai gani har hanji na anguwar kan tudu ya sakeki idan kuma............"
"Ke kinga dakata haka yah isa haka naji ,banason wani tone tone,shegiyar yarinyah kai,sai kace kedin allah da annabi kike bi yanda yakamata,naji zan barshi ya shiga amma ba dai ya tabamin kayan amfani ba sai yah tsarkake tukunna"
Shidai wucewa yauyi ya barta a wajen tana ta sababi kaman aikota.
Can wajen isha ne bayan anyi magriba,baba umaru ya aika a kiramasa dukkan yan matan gidan.
Har bakin turakarsa suka je kowa ta samu wajen zama ta zauna.
Gyaran muryah ya fara tareda godiyah ga Allah tukunna.
Nasan kunyi Mamakin tara ku danayi ,badan komai bane saidan na gargadeku sannan na baku umarni,a gaskiyah na gaji da ganin masu hira a kofar gida,kaman ku su sameerah,sannan kuma da jawo magana wato irin su sameemah.
Saurayi zainab ya bada uzirin cewa bai gama giniba,ga kuma wani aiki daya samu yana bukatar zuwa service,dan haka ina mai baku umarni kowa a cikinku ta fitar da miji,dan duk tareda za'ayi auren babu wadda zata sake zama na gaji haka sai na jj da masu tasowa.
I'd an kuma baku fitarba toh in lokacin yayi koma waye zan aura ma yarinyah,zabi yarage gana ku.
Ku ta shi Ku tafi na sallame ku.
*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
Kasuwar Rimi Kano
Tel:📞 *07038339244*
❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤
Kar ku manta da
#comment
#share
#like
#follow.
____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤
Wattpad username:SAKHNA03
❤33❤
Kowa tashi yayi yah nufi harkar gabansa masu surutu sunayi,ita kuwa sameemah hakan bai dameta ba dan duk cikin zancensa babu wanda ta saka a mizanin gaskiyha bare har yah dameta,ai zancene ma ace wai itah ce zatayi aure.
Da haka zancen yah wuce kowa yah cigaba da abinda yake gabansa.
Harkar aikinta kuwa sai abinda ya cigaba,dan koh wata bata cikaba amma suanan ta ya zagaya inda mutum baya tsammani a fadin garin.
Da dare suna kwance dakin shiru kowa yana harkarsa sameemah kamma aiki takeyi a cikin system na wajen aikinta,sameerah ce tah shigo dauke da leda a hannunta sai wani daga kai takeyi,dagargajewa tayu a tsakar dakin tana fito da duk abinda yake cikin ledar.
Da biyu takeyin abinda take dan kawai su salma su gani,
"Kai koh a tarihi ban taba ganin yanda masoyi yake kulada masoyiyar sa kaman umaruje ba,gaskiyah na yarsa ba kyau ne da kwallaiyah yake sa mace tayi farin jini ba,idan itah mai sa'a ce shikenan,saboda bakin jini har ana binsa gida amma ba'a sameshi ba har yah tako har wajena yah zabi sarauniyarsa"
Haka tah cigaba da surutunta da zarar bunu, amma babu wanda yah tanka mata,dan gwara ma salma taja tsuka amma sameemah kam koh daga idonta daga kan system din batayi ba,
"Salma bisimillah ga kayan dadi,wanda ba'a ci a gida fah"
"Ke sameerah iskancin ya isheki haka kodan kinga mu zuba miki idone iye,ta bamaci a gidan kedin ci kikeyi,banza sabun shiga kawai a cikin hakrkar"
Dari yah sameerah ta sheke da itah dan dama so take wani yah tanka mata a cikinsu,
"Sabun shigar shiyasa naga daga shigata da kamo babban kifi dan gidan manya saboda na cika mace"
"Wacce macen kika cika,koh kinace babu wanda yasan asirin da kukayi masa ne keda uwarki,kuka karkatar da hankalinsa daga kan sameemah zuwa naki,ai kowa ma yaga kallon dayake miki yasan ba a hankalinsa yake ba,idan har kina ji da ke macece ai saiki kallameshi tah kissa ba ta asiri ba"
Bakin cikine yah kama sameerah jin abinda salma take fada mata,bata san lokacin da ta kaimata raruma suka fara fada ba,cikin kankanin lokaci duk suka tumurmjshe naman kajin a da lemon a kasa.
Feduwar da sameemah tayi ne yasa su tsaywa sai a sannan suka ga irin ta'adin da sukayi da abincin.
Karnukan ne suka shigo da gudu,dan yanzu harda wani karami ma a cikinsu wanda sameemah tah samoshi a hanya yana halin jinyah,yanzu watansa daya kenan har koma kaman ba shi ba.
Dan dama itah haka halinta yake,yawancin abubuwan da suke karkashinta taimakone yake hadata dasu,shiyasa koda kudi babu wanda yah isa ya sayi yardarta a wake abinda yake nata.
Hannu tah mika tareda nuna musu naman dakaye kasa a babbaje. Sukuwa dama jira sukeyi kare da nama,ai babu batun jira.
Sororo sameerah ta tsayah tana kallon sameemah wanda tah bawa karnukanta naman da saida tah hada da bada jikinta kafin ta samu duk dan tazo tayi burga a gabansu,dan kallon yamda yake mata mutane suke gani,amma har yanzu bata wani mallkaki zuciyarsa yanda take so Ba,kawai idan tayi magana ne yaka aiwatarwa amma dan shi a karan kansa baya yi mata abu dan racayinsa kawai,
"Me kika aikata haka sameemah, nama nawa dana shigo dashi kika bawa karnukanki suke cinyewa"
"Yanzu yah tashi daga naki ai,tunda kin gama dashi ta hanyar zubar dashi a kasa,kinga yah zama na karnuka tunda dama abincin kasa su ake bawa,dan karna wahalar dake ne kawai na basu,menene lafina a ciki Toh?"
Har ta bude baki zatayi magana sameemah tasaka hannunta a baki shshshs da alamar tayu mata shiru .
"Banason dog on surutu aiki nakeyi,kuma nariga na fadamiki dalili,idan har kika sake cewa takk kuma a kan maganar toh umarni zan basu suna gamawa da naman su koma kan naki naman,in kuma kin musa ki gwada"
Ga kwadayi yana cin sameerah ga kuma haushin yanda ta samu naman amma bata ciba,ga kuma takaicin bata da ikon yin komai akan abinda sameemah tayi mata,,dan haka hadiye wani yawu kawai tayi tah fice a dakin,duk da tana ganin salma tana mata dariyar mugunta amma bata,kulata ba.
Dakin inna ramatu ta shiga ta sameta tana ta nade kayan wanki akan gado,daga ido tayi ta kalli sameerah din wanda sai kumbura takeyi dan bakin ciki,
"Ke kuma miye kika tsaya min a kai kaman kububuwa"
"Ummah da na fasa amma yamzu ina so a zartar da aikin kawai,sona ke yanzu duk wani aiki da zai rikitah kwalwalwar sameemah tah haukace to ayi mata,umma idan da dama ma tah daina yin komai a rayuwarta tazama tamkar mutun mutumi"
"Hmm kindawo hankalinki kenan,lokacin danake nuna miki gabar ai yamma kike dosa,dama na fada muku matukar tana numfashi sannan babu wani abu na dauri da akayi mata toh babu wanda zai yi rayuwar farin ciki kaff a cikin gidannan"
"Ummah harda salma ma inaso ayi mata wani abu"
"Keee rabani da taba salma uwarta maba a zaune takeba,sannan itah ba itah ce mataalarki ba a halin yanzu,su kansu mutanen gidan indai akan sameemah ne toh suna cikin tashin hankali idam asirin kanta yah karye,ke kina tunanin iyah ni kadaice kawai mai hannu a cikin aikin? Hmm akwai abinda yafaru wanda iyah mu muka sani kawai,yamzudai a bar wannan zancen tunda kince kin amince shikenan dama tun farko kece kika yimin gardama.
Boka yace baya bukatar kudinmu shidai burinsa kawai ki kwana a wajen sa toh duk wani abu da muke bukata zai tabbata,kinga koma menene sai ki tambayeshi kawai,saidai daga yanzu ki daina tuntubarta da fada,saboda kar ta gano mai yake faruwa"
"Toh shikenan ai gobe ma zan tafi,sai kicewa baba umaru na tafi kauyen kawunki saboda kinsan bayason fitarmu kwana a wani wajen,ai yamzu na tsani sameemah dinnan,dan idan muna zaune da umaruje har kirana yake da sunan fah"
"Yanzudai mungama magana ,kuma sannan ki fada masa yah turo a da maga ba tansa idan kuna hira,saboda da wurwuri ake dukan karfe kafin yayi sanyi"
Yau da safe kasancewar weekend ne babu zuwa wajen aiki,kowa yana gidansu,sallama akayiwa sameemah ana nemanta a waje,sai kace na miji babu alamar wani tambayar wani kafin ta fitah haka ta yafa gyalen abayar da take jikinta ta fita zuwa ganin mai sallamar.
Mamaki tayi da taga burgune da surayyah a bayan mashin dinsa suna kallnta fuskarsu dauke da murmushi,itama karisawa tayi kusansu saidai sabaninsu itah fuskarta babu alamar nuna wani reaction a ciki,
"Menene yah faru na ganku da ranar nana haka?"
"Shugaba alkhairi ne amma ga surayyah nan zaku shiga ciki tayi miki bayani,nizan je wani wajene idan na dawo zan maida ta gidan"
Kallon surayyah tayi tareda cewa,
"Ke Har yanzu kina yawon banzar koh baki dainaba,ba na gargadeki da bawa kowa lokacinki a araha ba,koh baki karanta takardar agreement din mu ba"
"Ahah shugaba wallahi na karanta,kuma ba na bin kowa yawo yanzu,kawai wannan din wanj abune daban kuma zanyi miki bayani"
Daga kai tayi kawai alamar taji kafin ta maida hankalinta kan burgu,
"Kai kumaa dama dazu nake shirin kiranka akN batun taron daza'ayi na senatoci ran Monday,ku tabbatar kun shiryah wajen kulada zirga zirgar mutane da cike hanya saboda kae a samu matsala"
"Shikenan zan samesu muyi maganar"
Sauka surayyah tayi daga kan mashin din tana kallon sameemah da idanuwanta so innocent kaman ba itah bace mai filllah rashin mutunci,itama sameemah kallonta tayi sau daya tareda zuyawa cikin gidan.
Ganin ta tafine yasa surayyah sake kallon burgu da alamar tambayar tabi ta kuma ta tsayah,
"Ki bi bayanta kawai kinga tayi mikk nisa,tunda Kika ga tayi haka tana nufin ki bi bayanta ne,saboda kimsan ba magana zatayimiki ba kaman sauran mutane"
Dahaka surayyah da dan gudu gudu saboda tayi mata dan nisa,tana yiwa kuma burgu bye bye wanda yah tada mashin din yana shirin barin wajen.
Tun daga shigarsu take ta kalle kallen cikin gidan,wanda yakeda kofofi da yawa a ciki,tana jin labarinsa amma wannan shine zuwanta na farko.
Wata kofah taga sun nufah sai gasu a dakin su sameemah,a bakin gado tah zauna yayinda sameemah ita,kuma tah fita waje sai gata da pure water a plate.
Ajiyewa tayi a gaban surayyah wanda ta hade jikinta waje dayah tana ta kalle kallen wajen ,
"Ke Kallon mai kike ne tunda zu,kincemin akwai abinda zaki fadamin kuma naga kinzo kinyi shiru baki ce komaiba"
"Ah Toh dama shugaba,ko na ce anty sameemah dama nida Ahmad(burgune )muke soyayya toh shine bamusan yanda abin zai faruba,sai muka yanke shawarar fadamiki tukunna duk yanda kika yanke akai"
"Nikuma nice mai yamke wa abinda yake cikin rayuwarku,ni babu ruwana da hakan saboda babu wanda nakeyiwa dole a cikin tsarina bare kuma saka shi dole sai yabi tsarina,saidia idan har ya yarda da cewa zai zauna dani toh wannan kuma daban"
"Eh dama ba haka bane anty sameemah,nice ma nace dole sai mun fadamiki,saboda iyayena sun amince da zamana a wajenki,duk da sunsan ba abune mai kyau ba nake niyyar yi amma kuma sun yarda dake ba niba,sannan tunda dukkanmu nidashi a karkashinki muke inaga ke yakamata ki shige mana gaba wajen hada kan iyayenmu da yimusu bayani,dan allah karkice a'a,ke kadai nake ganin zan samu goyon baya,wani abin a rayuwata rashin yar uwa mace da kuma rashin samun abokiyah ta gari mai hankali shiya fara saka raywata cikin hakan,saidai a yanzu ni ba ganinki na ke a iyah shugabata ba harda ma yar uwata,dan allah inaso ki daukeni a matsayin hakan"
Numfasawa sameemah tayi kafin tace,
"Shikenan inshaallah zanyi kokarin hakan tunda kin saka yardar ki a gareni"
"yawwa nagode anty sameemah Allah ya biyaki"
Daga haka suka bar zancen akan zata yi musu nata kokarin amma suma su sanar da iyayenna su akwai meeting dazasuyi da itah.
Dadine yakama surayyah har bata saN lokacin da ta rungume sameemah dan farinciki.
Tad'i suka dan fara yi bayan wannan zancen wanda kusam rabin maganar surayyah ce takeyi,dan itah bata iyha a zauna ana tadi ba irin na mata.
Sai wajen la'asar kafin burgu yazo yah dauketa suka tafi,wanda duk zamanta a dakim su salma basu kulata ba itama kuwa da ba baya bace a rashin mutunci sai abin yatafi a balance dan itahma kaman bata samu mutane a dakinba haka tayi.
Tun yinin ranar sameemah takejin faduwar gaba ga kuma wani nauyi da kirjinta yake yi mata wamda bata san daliliba,ta dawo daga raka surayyah zata shiga daki taji kamar alamar ana kiranta da karfi,bata wani bada reaction akan hakan ba duk da cewa zuwa sannan tah tabbbatar wani ne yake turomata wani abun,kasancewar ba wannan ne farko ba da ake mata,kuma tanada masaniyah akai.
*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
Kasuwar Rimi Kano
Tel:📞 *07038339244*
❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤
Kar ku manta da
#comment
#share
#like
#follow.
____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤
Wattpad username:SAKHNA03
❤34❤
"Haba manjo ka gyara hannun mana na gyara maka rigar,wallahi hadda ragwancinka ma yamzu kam tunda ciwon ya warke ai sai ka barni na ji da y'ay'anka ma"
"Wai ni kulu meyasa kika sanjane kullum cikin fada,nikam bana cemiki bazna kara shaye shaye ba,zan nemi sana'a na dungayi"
"Yah rage naka kuma,in kanaso ma ka cigaba"
Shiru yayi yana jinta shidai bukatarsa ta zubo masa wainar da takeyi ta rana yah ci tukunna komai ma sai ayi.
Hakan kuwa akayi tana zubowa yah yagyara hannun yanan dandanar miyar ganyen masar yana antayawa a bakinsa,koh maganarsa ba kaji,
"Hmm Gaskiyah nayi sa'a dana sameki dan naji ance sule har yanzu baya tashi.
~~~wani bakin tsuntsune yake ta bita mai kama da hankaka a wani waje mai surkukiyar gaske,dubawa tayi taga babu komai a jikinta sai wani farin yadi an yane jikinta daahi.
Ganin babu mafita ne yasata furmawa da gudu shikuwa ya bita a baya yana wata irin kara mai ratsa cikin kunnuwa.
Sun dad'e suna gudu har suka iso wani waje da hanyar bazata bulle ba sai wata babbar katanga wanda iyah ganin mutum baya iyah ganin keshenta.
*****
A can kuwa cikin sukukiyar daji da kuma tsohon dare,mutane biyu ne a zaune wanda saboda maita da kuma san abin duniyah basa da niyyar kwanciyha bacci irin na kowane san adam.
Sameerah ce ta kalli bokan da yake mata aiki tace,
"Toh yanzu kana ganin aikin zai yiwu kuwa?"
"Eh zai yiwu mana,yanzu haka tana can tana mafarki saboda munyi nasarar kama kuruwarta tun dazu,yamzu wancan tsuntsun da kike gani wanda muka tsireci da allurah uku bayan mun saka masa gashinta a cikin bakins kafin mu kasheshi,toh ruhinsa zai bayyana a cikin mafarkinta duk inda kuma yah ji mata ciwo toh bazai warkeba saidai ciwon ya cigaba da yaduwa irin na uwartah"
Leka kwaryar da take gaban bokan sameerah tayi dan ganin menene a ciki,idonta ne yayi tozali da video abinda yake afkuwa a cikin mafarkin sameemah,dadai inda bokan yasaka wani abu mai kaman katanga a gabanta saboda hana ta damar wucewa.
~~~,duk da gudun da tayi amma babu alamar gajiyah ko haki a cikin jikinta,saidai rashin ganin hanyar dazata cigaba da gudun yasa ta juyah tana kallon bakin tsunstun dayake nufowa wajen ta cikin saurin gudu da yafi na karfin tsuntsaye a gaske,saisa yazo daff da itah kafin tah mika hannunta tareda cewa,
"Tsaya Haka angama wasan. Yakai wannan *BAKIN RUHI*,(littafin marubuciyah oum hairan). Kayi kuskuren biyonin har wannan wajen,daga inda kake in jiyowa wani bangare na jikina a tareda kai,dan haka in umarninka daka tsaya a inda kake,idan kuma kayi gangancin matsowa toh mutuwar ma sai ta fimaka sauki"
Cak ya tsaya a wajen yana daddaga fuka fukansa kaamn yaga uban gidansa, masawa tayi inda yake tareda cewa,
"Yaron kirki ace dai kana jin magana"
Daga idonta tayi wanda yayi za kaman jini tana kallon sama,dadai wajen da su sameerah suke kallonta,gashin kanta ma yana dagawa a iska tamkar fatalwar data fito daga sabon kabari.
"Kinyi kuskure daga ke harshi din,a tunaninku bansan duk abinda kukeyimin bane?,nasani dukka kuma ba barku zanyiba ku tafi a banza,tunda yanzu har kun fara yin bakin asiri da kuma ruhin ba bayyi muku komai ba,duk da nakan dauki ruhi amma bana taba ruhin da baida laifi koda kuwa naso hakan,amma ku kunsaka kanku ciki saboda ku azzalumaine masu cutar wa.
Hhhhhhahhha kana nan yan iska kuna tunanin zaku iyah yimim wani abu a duniyar mafarkine wanda take itama duniyata ce?,kai daga nan inaso ka kayanka hannunka har sai jininka ya gama zubewa,ke kuma bazan yimiki komaiba kinci albarkacin yan uwantaka amma zaki karbi naki hukuncin koh ba yau ba kuwa,idan na barki da halin da kike shirin shiga ma ya isheki,sannan idan kin dawo ki gargadi uwarki abinda na fada miki
cewa karta kuskura ta sake shiga gonata,idan kuma wani ya ji a binda yafaru anan wajen toh sunanki matacciyah".
***
Abin bai kara bawa sameerah mamakiba saida taga yanda bokan yah dauki wuka ya yanka wuyahsa da itah,sannan jinin yana tafiyah direct zuwa cikin kwaryar wajen da sameemah take.
Ko motsi kasawa tayi har jinin bokan yah kare yah fadi a wajen,itah kuma kwaryar ta fashe,wani dogon numfashi sameerah taja kafin tah tashi ta furma da gudu zuwa cikin gari a kafarta duk da tsohon daren.
Tashi tayi daga baccin duk da har sannan gari bai wayeba dan koh assalatu ba ayiba,hankalinta kwance ta tashi ta debo ruwa ta sha kafin koma ta kwanta,saidai babu alamar bacci a idonta dan haka kallon rufin dakin kawai takeyi,idan ta tuna wanj abu sai tayi Murmushi wani kuma tah jijjiga kai.
Tana bude idonta sukayi tozali da sameerah wanda ta dawo da asuba tah zo daukar wani abu dakin,dan tunda ta dawo ba yanda ba'ayi da itha na amma daga ta doso dakinnan su sai jikinta yafara karkarwa saboda tsabar tsoro,sannan an tambayeta mai yah faru tace kuma babu komai,sai aka barshi da inaga gamo tayi a hanyarta ta dawowa,itama da taji mai suka ce sai ta amsa musu da cewar hakanne.
Toh yanzun ganin rana ta farayi amma sameemah bata fitoba ne yasakata shiga dakin da sanda domin daukar kayanata dan wancan din duk sun yage a hanyar dawowa daga jejin cikin hali na fitar hankali.
Saidai kashh rashin sa'a,tana shigowa itakuma sameemah tana tashi,karkarwa kafafunta suka farayi har sun gaza daukarta gabadayah,bajewa tayi a tsakar dakim har sannan idonta bai bar kan sameemah bah.
"Ke miye kike min kallo kaman kinga aljani"
"Bbbbbba bbbbbbu shhshshugabata dama kaya nazo dauka kuma banaso na tashaki a bacci,kiyafeni dan girman allah kiyimin rai"
"Hmm banace miki kar naji ba maganar nan a bakin kowa ba,toh ciki harda bakinki,gobema ki sake gigin yin shashancinki akai,dalla jita kaman kinsan allah ke,da kike hadani dashi nayimiki rai"
"Ahah na tuba kiyimin rai,in da san samu ma ki daukeni aiki a karkashinki koh kuma ki hadani da mai miki