Showing 108001 words to 111000 words out of 129540 words

Chapter 37 - ABDUL JALAL Hausa Novel

08 Oct 2024

6672

yagaya masa wannan maganar ya kyale,
Ya juya ya koma cikin Asibiti, yaje ya tarar da Still Jalila tana kuka, tana surutai akan Ummi, Halima nata bata hakuri, bebi takanta ba, ya kwashi wayoyinsa ya kwasa ya fice daga dakin.
Ana idar da sallar magariba Abba yazo, yaji dadin ganin Jalila, ta farfado ta fara samun sauki, sedai tarame sosai, ta danyi duhu, shima Abban haka ta dinga masa kuka, tana surutai, ita ummi,
Abba ya shiga yi mata nasiha me ratsa jiki
"Jalila ki karbi kaddararki a duk yadda tazo miki, nima inata kokarin inga munsamu inda take amma abun ya gagara, inkika mika al amuranki ga Allah komai zezo da sauki, jikina yana bani har yanzu tana raye, kuma zata dawo, karki cutar da kanki da wannan kukan da kikeyi, "
Abba ya kalleta sannan ya kira sunanta" Jalila"
"Na am Abba"
Ya cigaba da cewa "nidin nan ma misaline a gurinki, ba uwa ba uba, ba danuwana, gashi bamu da wasu dangi nakusa kona nesa, nasan bazaki rasa sanin tarihinmu ba nida mahifinki a gurin umminkiba, mu biyune kawai a gurin iyayenmu, kuma suma ba yan garin nan bane, gudun hijira sukayo, a yanzu haka bani da kowa, daga Allah seku ya'yana, ku nake kallo inji dadi, lokacin da nake kan ganiyar bukatar kulawar dangina, Allah ya karbesu gaba daya, amma hakan be hanani rayuwa ba, dukda har yanzu inata fafutuka ko Allah zesa insamu wani daga cikin danginmu,
Dan haka ki kwantar da hankalinki, kinada Allah kuma ni mahaifine a gurinki, duk rintsi duk wuya, babu abunda zesa in juya miki baya, ko Ummi na nan kobata nan, ina kaunarki yata ce ke jinin dan uwana, kicigaba da addu'a ki kwantar da hankalinki, kinji yarinyar kirki, zuciyata na shiga kunci idan naga hawayen marainiyar nan kuma amanar Aliyu, bana son zubar hawayenki, kiyi hakuri duk lokacin da kike kuka ji nake kaman naci amanane, "
Sosai nasihar Abba ta ratsa zuciyar Jalila, wanda yasa jikinta yin sanyi matuka ga kuma tausayinsa daya kamata
"insha Allah, Abba zan cigaba da addu'a in tana raye Allah yasa tana hannu nagari, inta rasu kuma Allah ya.......... Kawai seta fashe da kuka
Sosai tausayinta ya kama Abba, Halima dake gefe ma kuka take, Jawwad ma ji yayi kaman ya tayata
Abba yace" tana rayema Insha Allah, kuma zamu gano inda take "
Gyada masa kai tayi, Jawwad yace
"Abba Maama tazo dazu ta dubata"
"yayi kyau" shine kawai abunda Abba ya fada, ya tashi ya tafi, bayan tafiyar Abba, Jawwad ma barin dakin yayi, yaje office din doctor Salis, bayan sun gaisa, Jawwad yake tambayarsa yaushe ze sallami Jalila
"se ta dan kara hutawa, nan da ko kwana biyune, tana bukatar kulawa, saboda abunda ze iya biyo baya, amma nan da kwana biyu ze sallameta Insha Allah" daga haka sukayi sallama ya fito, Jawwad koda ya fito bekoma gurin Jalila ba ya tafi gida, seda akayi sallar isha'i sannan ya dauki Nana ya kaita Asibiti, daya kaita ma a gate ya tsaya ta sauka ya juya, Nana tayi murna ganin Jikin Jalila da sauki, hira Nana take tayi mata amma tayi shiru, zuciyarta duk babu dadi, dakewa kawai takeyi,
"Nana ina yaya Jawwad"?
"Ai yana ajiyeni ya juya, inaga ko wani gurin zashi" Jalila ta dan jinjina kai,
? ?
Jalal kwance a dakinsa ya kurawa ceiling ido, dagani yayi zurfi sosai cikin tunani, dan lumshe ido yayi, tareda yin Ajiyar zuciya, kirjinsa yamasa nauyi matuka, ya mike zaune ya dafe kansa da hannunsa biyu, sallama tayi a palournsa, yai shiru be amsa ba, ta karaso da tray a hannunta ta nemi guri ta zauna a kusa da shi, hannunta biyu ta saka ta cire masa tagumin
"Yaya Jalal meyake damunka tagumi fa babu kyau" dan kurawa Ilham ido yayi ya dauke kansa
"Yaya kayimin magana mana, naganka wani iri"
"Me kikazo yimin nan?"
"Fruit na kawo maka, kuma naga kwana biyu baka zama a gida, kwana uku banganka ba, duk na damu, ko cikin gida baka lekamu"
"Inkingama ki tashi kibani guri"
"Haba yaya Jalal, in damu da kai har inzo inda kake amma ka koreni, please yaya Jalal kabani dama mana a rayuwa, wallahi I love you Yayana, please marry me, in ba kaiba rayuwata tana cikin hatsari ina bukatar kulawarka, bazan iya auren wani ba kaiba"
"Idan kika bari na kuma yi miki maganar ki barmun dakina, sena miki abunda baki taba zatoba, sha3 mahaukaciya kawai" daga haka ya tashi yabar palourn ya shige bedroom dinsa,
Mutuwar zaune tayi, gaba daya notin kanta ya kwance tarasa mezatayi, ita namiji yake wulakantawa haka, dole tanemi mafita, Jalal yafara kaita bango matuka, tana cikin nazarinne wayar Jalal daya bari a hannun kujera tafara ringing, amma setaga lambace ba suna, hannu ta kai ta daga wayar tasaka a kunnenta, da dagawarta taji muryar mace tafara magana
"Haba my Jalal, kwana na uku ban ganka ba, ban saka a idona ba duk na damu, gashi baka daga wayata ina ka shigane, I want surprise you"
Ran Ilham ne ya baci, dan haka cikin masifa tace "Ke dalla Malama dakata mahaukaciya, dabbar inace ke, to Wallahi bari kiji in gaya miki, ko ke kika kaso maita duniya bakisa ki auri Jalal ba, Jalal nawane ni kadai, inbiki kiyayeni ba wallahi se kinyi danasanin zuwanki duniya, gara tun wuri kisan inda dare yai miki, Jalal bashi da wata mata in ba niba, munafukar banza data wofi, maci amana"
Hannah tace
"Ke saurara Me kike da suna, karki kuskura kice zaki zageni, bani da lokacin ki, haduwarmu ta farko kin gayamin magana son ranki, na kyaleki, bani da lokacinki, kuma idan ina raye Wallahi karya kike kema ki auri Jalal muzuba nidake, dan halak ka fasa, sokuwa kawai"
Jin hargowar Ilham ne yasa JALAL fitowa daga bedroom dinsa, yana zuwa ya tarar da Ilham rike da wayarsa tanata bala'i da surutai, karasawa inda take yayi, yasa hannu ya karbe wayarsa, ya juya ya nufi dakinsa, mikewa Ilham tayi tabi bayan Jalal tana masifa, a kunnensa ya kara wayar
"Ya akayi?"
"haba Jalal, meyasa kanwarka mahaukaciya ce, toka gayamata idan a wancan lokacin mun hadu ta zageni na kyaleta ta kiyayeni(a zatonta Jalila ce Ilham) , kasan halina zan mata rashin mutunci, kuma ka gaggauta gaya mata, nida ita shege kafasa"
"meyasa ke baki gaya mata ba"?
"Hakama zaka ce? Shikenan Jalal, ina ta wahala akanka, amma wata tana cimin mutunci ko, shikenan zatasan wata zaga wallahi, kasani duk me shirin kawomin matsala tsakanina da kai, sena gwada masa ni a mata ta dabance"
"Look Hannah bana son shirme kaina kemin ciwo, kuje kuyi tayi, tunda daga ke har ita baku da hankali, banzaye kawai"
Hannah kuma Ilham ta faada a hankali ba Jalila ba, wace kuma hannah, inma rainamin hankali suke, zasuga tsiya, yana gama wayar ya ajiyeta, wannan jarababbun sun kara hargitsa masa lissafi ransa a matukar bace yake, ya balle rigarsa ya aje kan gado ya juyo, yaga still Ilham tana tsaye, tana huci
"Meye haka ina cire kaya kinzo kin sani gaba, malama ki wuce ki bani guri, bana son shirme ds hauka"
"Wallahi Yaya Jalal, bazaka tabbatar da nayi hauka ba se ranar dana fara yimaka haukan, ni kake cewa mahaukaciya ko?.......
Tinkarota yayi gadan2 ta juya da gudu ta fice, dan data bari ya karaso ta san sauran, amma shi a gurinsa yayine dan ya tsorata ta, saboda tun ranar da Jalila tace masa ragon namiji shike dukan mata, be kara dukan Ilham ba, sedai yayi mata tsawa, shiyasa tasamu damar kara yi masa shishshigi, tana juyawa ta tafi, ya dawo ya zauna yai shiru, sun kara dagula masa lissafi, ga maganganun Jalila sun tsaya masa a rai, daga baya yaga bashi da mafita, ya tashi ya dakko mutuniyar tasa, yaiwa kansa caji ya kwanta anan, yafara bacci.
Jalila ta fuskanci Jawwad fushi yake, a lokacin itama taga rashin dacewar abunda tayi amma ba yadda zatayi, itama bata san tayiba, tana cikin dimuwane, shikuma yasata gaba da jaraba, tana wannan tunanin bacci yai awon gaba da ita

Yana kwance akan cinyarta, tana shafa sumarsa, tafara magana cikin sigar rarrashi, da daddadar muryarta me cike da iyayi da shagwaba
"AbdulJalal dina, kadena shan giya kaji, banason abunda kakeyi, bana son ganinka a irin wannan yanayin raina bayamin dadi, sonake kazama mutumin kirki kaman kowa, mutane sudena kyamarka,"
Murmushi yayi,
"To Babyna, nima bana son abunda nakeyi, zuciyata bataso bansan meyasa nakasa denawa ba, amma ki dinga yimin addu'a zan dena, amma nima kidena yimin wulakanci a gaban mutane banaso"
"Kullum ina yimaka, addu a, idan naga kana rashin kyautawa, gaba daya rainane yake baci, shiyasa nakema ka haka, amma nima na dena, amma promise me kaima zaka dena"
Murmushi ya kumayi "Allah yayi miki albarka My queen u mean a lot to me, Insha Allah ze wuce kaman banyiba, yayinda mutane ke guduna da kyamar halayena, lokacin kuke kaunata ke da yayanki, can't forget your sacrifice "same to me, u mean a lot to me, ABDUL JALAL, fuskarta ta sunkuyo zata sumbaci goshinsa, "
"Jalal ka tashi rana tayi haske fa, nasan ko salla bakayiba, se wani Murmushi kake a cikin bacci, wai me kake ganine a baccin"?
Se yanzu Jalal ya gane mafarki yakeyi, Kallon Jawwad, Jalal yayi yayi tsaki
Jawwad yace "Ya dai?"
Ajiyar zuciya Jalal yayi "Bakomai"
"Bakomai kake ta murmushi a bacci haka, gayamin mafarkin me kake?"
"Kaga ni ka rabu dani"
"Anyway kaje kayi salla, takwas da rabi fa" Jalal bekuma cewa komai ba ya mike yaje yai wanka, yai alwala yai salla
Ilham ta boye damuwarta tayi breakfast, bayan tagama breakfast ta mike ta nufi gidansu Nana, bakowa a palourn gidan, dan haka ta wuce dakinsu Nana, taje ta tarar da Nana tana wanka, amma bataga Jalila ba, neman guri tayi ta zauna, ta jira Nana ta fito, Nana ta kalleta
"Lafiya kuwa da safiyan nan? Naga kwana biyu ma bana ganinki, ko kun jone da Yaya Jalal ne no more matsala, shiyasa kika yadani"
"Nana ba wannan ba ina yar uwarki?"
"aini dama a kule nake dake Ilham, kwanan Jalila uku a Asibiti se jiya ta farfado, amma kokice tana ina, ta sha jiki kaman zata mutu" Ilham a ranta tace " A a tana asibiti to wace ce mukayi waya jiya,? cikin ko in kula Ilham tace
"Niban saniba, bansan bata da lafiya ba, Allah ya sawwake"
"Ah haba zakicemin baki saniba, bayan yaya Jalal ya jejje Asibiti dubata"
Ji Ilham tayi kaman Nana ta soka mata kibiya, "yaje dubata fa kikace"
"wallahi kuwa, kullum se yaje, nima yabani mamaki, amma kinsan kobeje dan kowaba yaje dan Yaya Jawwad"
Jinjina kai Ilham tayi, ta Mike "na tafi se anjima"
"daga zuwanki zaki tafi"
"eh naga kaman fita zakiyi"
"A a ba inda zani Asibiti ne se anjima zani"
Bata kuma bi takan, Nana ba, Daga haka tai waje, zuciyarta fal takaici, wai kullum se yaje asibiti tunda aka kwantar da ita, "ko uban me yake zuwa yi, ta tabbatar ko uwarsa a aka kwantar baze je dubata kullum ba, tokuma wace ta kirashi, jiya? Karfa inje ina can ina hauka, aikin gama ya gama ina gefe, kai da sake wallahi, dole in tada balli" daga nan tai gida kaman mahukaciya.
Bayan su Jalal sun gama breakfast, Jawwad ya tafi asibiti be takurawa Jalal seyaje ba dan ko shine baze komaba sabida abunda baby tayi masa.
Doctor salis ya shigo yai mata allura ta cannula, bayan yagama ne ya kalleta
"Baby ya jikin" banza tayi masa
"ya kikayi shiru?"
"nace maka ba sunana Baby ba"
"Amma yayanki yake gaya miki"
"to ba Yayana kace ba, ko kai yaya nane? "
"am sorry, Jalila ya jiki"
"da sauki Alhamdilillah"
"Masha Allah, Allah yakara miki lafiya, jinake ciwon nan kaman ya dawo jikina, duk na damu wallahi"
Dan ya mutsa fuska tayi
"dan Allah ni ka sallameni yau"
"Amma meyasa?"
"To zaman me nake bayan na warke, ni kawai ka sallameni nagaji da zaman asibitin nan, gara in? koma gida"
"Dan Allah kiyi hakuri nasan in kika tafi ba lallai inkuma ganinki ba"
"wani mugun kallo Jalila tayi masa, to in zauna in maka mene? Ni gaskiya nagaji gida nakeson komawa, kobaka sallameniba sena tafi, ko in Abba yazo in gaya masa mekace"
"A a yi hakuri, zan sallameki yau Insha Allah tunda kin warware"
"da dai yafi maka"
A ransa yace lallai haka wannan yarinyar take da tsiwa, lallai Jalal yayi gaskiya, amma shidai a hakan yana sonta don komai nata yana birgeshi, ana haka Jawwad yazo suka gaisa da doctor salis, ya gayawa Jawwad yau ze sallami Jalila, tace ita tagaji da zaman Asibitin, Jawwad yai murna sosai yace "indai ba wani matsala ai gara a sallamemu,"
Bayan fitar doctor Salis, Jawwad ya nemi guri zauna, ko kula Jalila beyiba,
"Yaya Jawwad, ina kwana?"
"lafiya kalau" shine abunda Jawwad yace,
Daga nan bekuma cewa komai ba, wayarsa ce ta fara ringing ya dakko ya daga
"Salamu alaikum"
"Wa alaikum salam, My Jawwad barka da safiya,"
Muryar ya dauka, ya gane me maganar, dan haka yayi murmushi
"Hanan kin tashi lafiya" seda Jalila ta waigo ta kalleshi
"Lafiya kalau, yame Jiki, Abdallah yacemin batada lafiya, da sauki jikin nata? Ko kuwa? "
"Kwantar da hankalinki, Hanan taji sauki, muna sa ran Insha Allah yau za a sallameta"
"Me yasameta ne"?
"Ta samu stroke ne, amma yanzu ta farfado tana lafiya"
"Allah sarki na kira wayarta ne bata shiga, itakam baby me yayi zafi haka, har tasamu stroke? in kana kusa da ita bani muyi magana"
Wayar a hansfree take Jalila tana jin komai
Ya kalli Jalila sannan yace
"Bacci take in ta tashi zan gaya mata"
"to shikenan"
"kayi saving lambata, mu dingayin waya"
"to shikenan, karki damu" sukayi sallama da Hanan
Ya mike ze fita Jalila ta kira sunansa, tsayawa yai ya waigo yana kallonta
Idonta taf hawaye "Yaya Jawwad fushi kake dani ko? Dan Allah kayi hakuri, bazan, kuma ba" takarasa maganan hawaye na gangarowa daga idonta, ita dai zubda hawaye baya mata wahala
Dawowa yai yazo gefen gadon ya zauna
"Baby sam banji dadin abunda kikayiwa Jalal ba, haba baby, gaba yake dake fa, indai zakiyi masa haka nima zaki iya yimin kenan"
Girgiza kai tayi "A a Yaya dan Allah kayi hakuri, nima ba a son raina na fada ba, raina ne a bace, shikuma yafaramin masifa, amma kayi hakuri"
"Bani zaki bawa hakuri ba, inkina so in hakura, Jalal zaki bawa hakuri"
Da sauri ta dago ta kalli Jawwad


Share please
More Comments More typing..............................


=؊??=؊??=؊??=؊??=؊??
[9/23, 10:27 AM] +234 802 426 7634:
? ? _ABDUL? JALAL_

? ? ? _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
? ? (Daddy's girl)

? ? ? ? ? ? ? ?PAGE-? 48
PART 1

? _Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa,? ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

A har kullum ina jinjina da godiya ga masoya wannan novel nawa, comments dinku da addu oinku ina jin dainsu matuka, ina godiya kwarai dagaske,
Domin sharhi, gyara, kokuma shawara a nemeni ta what's app akan wannan lambar wayar
07063065680
Ina godiya matuka Allah yabar kauna

? ?? ? ? ? ?? _My first novel_


Jawwad ya dan daga mata gira
"Yes se kin bashi hakuri, sannan nima zan hakura", lallaima wai sena bashi hakuri, ajiyar zuciya tayi
"to yaya Jawwad, zan bashi hakuri Insha Allah"
"Yawwa baby, Allah yaba ki lafiya"
Jikinta a sanyaye, tace "Ameen"
Kamar yadda doctor yai mata alkawari, da yamma aka rubuta musu sallama, jikinta yayai kyau sedai rama, duk yadda doctor Salis yaso Jalila ta dan sakarmasa fuska ya samu kafa kansa taki, dan ita wannan shishshigin daya kemata haushi yake bata, shiyasa kome yace setayi masa shiru, ta hade rai, haka ya gaji ya hakura, suka shirya suka hada kayansu, Jawwad ya daukesu se gida, Abba yayi murna matuka da ganin an sallamo Jalila, Nana ma se murna take, Jalila ta dawo, saboda Jalila ba karamin alkhairi bace a gidan
Har yanzu Abba yana fushi da Maama akan Jalila, tayi mamakin tsawon lokacin daya dauka haka, yana fushi akan wannan yarinyar, yanzu takuma tabbatar da idan har batayi taka tsan2 ba aurenta ze iya mutuwa saboda ita, se yanzu taga gaskiyar maganar yaya mairo, su Nana ma ba bi takanta sukeba, duk saboda Jalila, lallai tayi kuskuren yadda da Jalila ta zauna mata a gida, gashi tafara hada mata husuma a gida, dole tasan abunyi.
? Kwana biyu da sallaman Jalila daga asibiti ta kara murmurewa, ta shiga sabgoginta, amma takan kebe ita kadai tayi kuka me isarta, gudun tayarwa da mutan gidan hankali, sannan tanata addu'a In Ummi na raye Allah ya bayyanata, tana cikin matukar damuwa amma, tayi iya kokarinta domin dannewa, kar a gane duk abunda take karfin haline kawai, Jalila ta lura Abba baya kula Maama, da tasaba kullum ta rakoshi in befita da wuriba, sucu Abinci ai wasa ai dariya, amma yanzu taga ko magana tayi se yayi mata banza, Jalila setaga hakan ba dadi, gidan ma ba dadi da suke zaune a haka, itako Nana ko a jikinta sabgoginta take.
? Yau Maama ta fita bata gida da yamma, har magariba bata dawo ba, dan haka bayan an idar da sallar maghariba, Jawwad yasamu damar kiran Nana a waya yace ta tura masa Jalila,
Ba musu Jalila ta tashi ta dau dan sirin gyale tasaka akanta, ta fita, part dinsa, da sallama ta shiga, taje ta tarar da shi yana aiki akan system dinshi, tana zuwa ya kashe system din, ya dago ya amsa sallamarta, karasawa tayi taje ta zauna a kasan carfet
"Yaya gani, Nana tace kana kirana"
"Eh Jalila, ya jikin naki"
"da sauki Alhamdilillah yaya"
"masha Allah haka akeso, dama kiranki nayi inji ya maganarmu ta rannan, kin bashi hakurin kuwa"?
Dan hade rai Jalila tayi
"To yaya ni ina zan ganshi, niban bashiba" ta fada tana dan zumbura baki
"To taso muje"
"Yaya ina zamu?"
"Zo muje seki gani" yafada yana tashi tsaye
Ba musu itama ta mike tabi bayansa, waje ya fita tana biye dashi, gidansu Jalal ya nufa, suna zuwa yai musu jagora zuwa part din Jalal, Jalila tayi mamaki duk

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login