Showing 135001 words to 138000 words out of 141466 words

Chapter 46 - ZUCIYA kowa da irin tasa Complete Hausa Novel

unknown   

13 Oct 2024

15897

kace zakasa a saki d'ana?"

Ashraf yace " zan biya kudin da ake binsa zai kuma yi bailing sa "

Tace " naji yaushe kakeso in fada?"

Murmushi ya mata yace " zan sanae dake lokacin."

Cikin damuwa tace " Yaushe to zaka sa a fito da Asim din?"

Yace " karki damu saboda ankusa a cikin satin nan ne insha Allah."

Nan ta fito tai gida.


Dady shima yazo, kuka sosai yai agaban Ashraf magana d'aya yake cewa "Ashraf ka yafemin, kalmar da kawai yake fada kenan."

Ashraf ya kalleshi yace " karka damu Dady ko ma menene na yafema."


Yau 'yan sanda suka isa company din da Kawu yake, shi kam a wannan lokacin nema yake ya tattara komai na company din ya gudu, bai taba tunanin za'a zagayo kansa da wuri haka ba.

Yana zaune a office suka iso, ID dinsu ogan ya fito dashi yace " u are under arrest."

Kawu ya daure yace " akan me kenan?"

Officer din yace " mun kama daya daga cikin yaran da ka sa su sa wuta a ginin sannan ya bamu tabbacin kaine ka sasu."

Kawu ya rikice yace " a ina? Karya yakemin, Ashraf ne ya zugashi."

Baiyi auni ba yaji ansa mai ankwa, nan fa hankalinsa ya tashi ya shiga sambatu yana cewa a kira masa Ruma, shifa bai san me ke faruwa ba.

Sudai sukai waje dashi.

A cell aka garkama shi, sannan aka umarci Ashraf dayazo.

Bayan ya zo ne nan ya basu wayarsa sukaji duk abinda ya faru a lokacin.

Hankalin kawu ya tashi, ya dinga musu hauka.

Nan aka shigar da kara kotu.


Kawu kam anga rayuwa, bai taba tunanin zama a cikin dan dakin nan ba duk tsawan rayuwarsa.

Duk yayi baki ya jemi, Ruma kawai yake kira, ya ma rasa inda zaisa kansa, yayi tunanin basu kudi su fitar dashi, sai dai inaa duk inda ya bula abin yaki yiwuwa.
Har ranar zama a kotu.



***********


Nafi sun fito daga masallaci a garin makka, suna tafe ita da Mumy, Mumy ta kalleta tace " gashi har mun kusa komawa banga ko waya kunyi da Ashraf ba."

Nafi tai kasa dakai tace " Nasan zai nemimu in har ya nutsu."

Mumy tai murmushi tace " Nafisa kina birgeni sosai, kinama mijinki uzuri ba kamar wasu matan na zamani ba."

Nafi ta kalli takaru yanda taga anbiyosu sun smkwashi kayan da suka baza akan titi da gudu kamar me suna zabga gudu, ta kalli Mumy tace " nikam Mumy wai haka duka takaru suke zama agarin nan sam ba daraja?"

Mumy tai murmushi tace " ba duka bane suke rayuwa haka, sai dai akasarinsu abinda suke kenan, sai dai addu'a."

Nafi sunzo tsallakawa wata ta taho da kayan saidawarta da gudu ta bangaje ta da karfi wanda sai da ta fadi.

Matar ta tsaya tana ba Nafi hakuri, Mumy ta kalleta tace " haba baiwar Allah kudinga abu da hankali mana."

Nafi ta dago dan yima matar magana, mai idanunta zai gani?"

Mahaifiyarta ce sanye da wata kodadiyar doguwar riga da hijab tana rike da kayan saidaiwa a hannunta tanayi tana waigawa, ganin an biyosu yasa ta juya zata tafi.

Cikin zafin nama Nafi ta kama hijabin ta.

Matarta kalleta tace " Malama kiyi hakuri nace."

Nafi ta kara kura mata ido, tace " Inna?"

Kallan mamaki matar ta mata tace " ban gane ba."


Hawaye ne ya fara zubo ma Nafi tace " Inna nice fa Nafi."

Idanu matar ta zaro cikin tsananin kidima tace " Nafi?"

Mumy kam ta fahimci me ke faruwa ganin an biyosu yasa tace " mu wuce d'aki kwayi magana."

Nan suka karasa hotel dinsu.

Nafi hannunta na cikin na mahaifiyarta kuka kawai takeyi, ita kanta matar kuka take.

Nafi ta daure tace " rayuwar da kikeso kenan ki ka barni a kauye ni kadai?"

Inna ta share tata kwallar tace " Nafi ki yafemin wlh nayi dana sani sosai na barinki."

Nafi cikin kuka tace " menene abin birgewa anan?sannan ina kanina Mudan?"

Uwar ta share kwallarta tace " Mudan tun daya girma ya bi abokai suka shiga hidimar duniya, har abu yake sha, nayi fadan har na gaji, nayi dana sani har ba iyaka, rannan Aka zo min da labarin hadarin mota da sukai."

Hankalin Nafi ya tashi kwarai tace " meyasa baki koma ba bayan rasuwarsa?"

Tace " da wani idan zan koma? Bayan kayan Datti dana sata na bar iyayena sannan na barki, na kuma yi sanadiyar mutuwar dana, nikuwa mai zan koma inyi?"

Kuka sosai takeyi wanda hankalin Nafi ya kara tashi, nan suka shiga yin kuka sosai.

Mumy ta tausaya musu, nan taba mahaifiyar Nafi shawara akan ta dawo nan da zama tunda sun kusa tafiya kuma International ne zata biya kudi au wuce da ita.

Godiya sosai Inna ta dinga yi haka ma Nafi.


*************


Anyi zama a kotu inda Lawyer din Ashraf ya dinga fito da shaidu na garari ciki kuwa harda Auwal Max, Umma, Dady, Alhaji Uba sannan ga wasikar mahaifinsa ga kuma yaran da aka kama yasa wuta.

Ga maganar Kawu wanda Ashraf ya dauka, hankalin Lawyer din Kawu ya tashi ganin ba wata mafita, nan fa kowa ya san abinda kawu yai ma Abbas da d'ansa.

Kotu ta umarci dole ne ayima Dady da Mumy hukunci sannan Umma ma.

Kawu an yanke mai hukuncin daurin rai da rai, saboda ya kashe Abbas sannan ya nemi kashe Ashraf banda dukiyar maraya dayake amfani da ita.

Dady kuma an yanke mai hukuncin shekara 10 saboda shima dashi aka hada baki gunyin kisa, sannan shima yaci kudin maraya.

Mumy kuna an yanke mata hukunci kala biyu, ko ta je gidan yari ta zauna na shekara 2 saboda karyar da tai akan gadon maraya duk da kuwa danta ne, ko kuma ta biya kudi million 30.


Umma kuma an yanke mata hukuncin biyan kudi dubu 200 saboda kin fadar gaskiya datai.


Auwal Max ma an mai hukuncin zaman gidan yari na shekara 8 saboda yayi laifin taimako gunyin kisa.

An sanar da Mumy bata kasar sai dai ana sa ran nan da kwana 3 zata dawo.
Alkali yace tana dawowa a killaceta.

Da wannan zaman kotu ya tashi.


Littke tayi kuka kamar ranta zai fita jin wannan sabon al'amari, hankalinta ya tashi, labari kuwa ya bazu a gari ko ina ka zaka abinda ake fada kenan.

Su Ferry ma Nabil yazo ya basu labari, hankalin kowa ya tashi na mamakin wannan al'amarin, anyi bikin jibiya waccan satin.



Shikam kawu maganarsa daya shifa Ashraf ya cuceshi akuma kiramai Rumarsa.


Hmmmm nace su kawu sai ai zaman yari lafiya.....lol😂


*#ASHRAFEENAH TEAM*

💞

_Barkanmu da shan ruwa, Allah ya bamu ladan ibadar amin_
*ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com


*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡



*87*



Little tayi kuka kamar ranta zai fita, Anisa ma haka, haka suka rungume juna itada Little a kotu suna kuka, Ashraf daga gefe yana zaune yana kallansu, shikansa abinda yake tausayi da tsoro kenan bayasan Little tasan abinda ke faruwa sai dai ba yanda zaiyi.

Habib wanda ke zaune kusa dashi idanunsa sun kada sunyi jaa kamar goro, yasa hannu ya buga kafadar Ashraf baice komai ba ya mike zai fita, hannu Ashraf yasa yamaidashi ya zauna sannan a hankali yace " ina zaka?"

Duk yanda Habib yaso ya b'oye hawayensa kasawa yai tun balle daya kalli Little yaga yanda take wani irin kuka, a hankali hawayensa suka ziraro ya kalli Ashraf kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa.

Ashraf ya mai murmushi yace "karkace komai Buddy nasan abinda ke ranka, so stop feeling guilty, ba laifinka bane haka fatanmu dai Allah ya yafe mana kurakuranmu."

Rungumeshi Habib yai alokacin hawaye ya fara zubomai sosai, cikin takaici da tsantsan tausayi yace "Ashraf na na......."

Kasa karasawa yai dan kukan yamai karfi, Ashraf ya bubuga bayansa a hankalu yace " karka damu abokina in har zuciyarka ta karye haka, Little fa?"

A hankali Habib ya d'ago ya kalleta sannan ya kalli Ashraf.

Murmushi Ashraf ya sakar mai sannan yace " kalli Dady ka gani shikanshi murmushi yakema."

Nan Habib ya kalli mahaifinsa wanda za'ai waje dasu, da sauri ya dauke kansa yace " ni ai bansanshi ba."

Ashraf ya hade fuska yace " ka tashi kaje kamai sallama, ko kamanta mahaifinka ne?"

Habib ya kalli Ashraf yace " Haba Ashraf kisa fa?"

Sosai Ashraf ya tamke fuska yace " ka tashi ko kuwa?"

Jiki a sanyaye Habib ya mike ya karasa gun mahaifinsa.

Yana matsowa Dady ya kama hannunsa yace " Habib kayi hakuri."

Habib ya kalleshi cikin takaici yace " Dady ban taba tunanin haka halayenka b'oyayyu suke ba."

Dady ya daure yace " Ni kaina bansan me ya sameni ba, sa dai fatana kada kasa wannan abun a ranka harya xamemaka wani abun, sannan duk da abinda ke tsakanina da mahaifin Little bazai hanani yimaka sha'awar auranta ba."

Habib ya dago cikin mamaki yace " Kanaso kace in auri Little bayan abinda kukama mahaifin Ashraf?ai ba Little ba banaji ma zan iya auran wata a duniya."

Yana kainan yai waje da sauri, Dady ya bishi da kallo hawaye suka zubomai.

Nan akai gaba dashi, kawu kam ba wanda yaje gunsa haka aka fita dasu aka sasu a mota Sai gidan yari.


Anisa kam tana isa gida ta rufe kanta a d'aki banda kuka ba abinda takeyi, tayaya mahaifinta zai kashe mahaifin Ashraf? Itakam ba wani uzuri da zatama mahaifinta ace d'an uwanka?duk da ba uwarsu d'aya ba ai jini jini ne, itakam bataji zata iya ko da cutar da Little ne bari har akai ga kisa.

Duk yanda Umma ke buga mata d'aki taki bud'ewa, a yanzu kam ta tabbatar da aurenta da Ashraf ya kare haka kuma tasan rayuwarta tazo karshe ba tantama.


Ganin taki bud'ewa yasa Umma ta koma falo ta baza tagumi tana kallan tsakar falon, lalai ba shakka duniya abin tsoro ce, itakam komai da yake faruwa jinsa take kamar a wani mumunan mafarki ne da takeyi.



Little kam zazzabi ne mai zafi ya rufeta wanda sai dayakaita ga kwana a asibiti.

************


Mumy da kanta ta nemi mahaifiyar Nafi akan ta zauna da su sannan su tafi tare, Inna kam ta amince da hakan dan batada wani uzuri sai mamakin yanda 'yarta ta zama takeyi balle yanda taga Mumy na ji da ita.

Nafi ta ba Inna labarin duk abinda ya faru wanda yasata kuka kamar ranta zai fita dan kuwa tasan laifinta ne duk abinda ya faru ba shakka itace sila sai dai tayi farinciki na ganin yarta cikin wadata haka da farinciki.

Sun shirya tsaf Mumy ta biya kudin komawa da Inna.

Nan suka shirya suka baro kasa mai tsarki suka dawo gida Nigeria.

A ranar da zasu dawo Ashraf sam ya kasa zaune ya kasa tsaye dama tun washegari kafin su dawo ya dau Dan Litti suka shiga manya manyan company's na yin furnitures yasa kaf kayan bangarensa aka canza ma Nafi, sannan ya sai akwatuna saiti ya zubamata kaya kala kala, dinkakune, wadanda ba'a dinka ba, dogayen riguna da English wears.

Ya dauko masu gyara aka gyara bangaren sosai kana gani kasan amarya za'a kawo.

Kayan Anisa na sawa kuwa aika mata b'angaren mahaifiyarta yai, wanda hakan ba karamin tada musu hankalu yai ba, Anisa kam ko abinci bata iya ci kullum kuka kawai takeyi.

Yau tun safe ya shirya dan sunyi waya da wani abokinsa da suka tafi tare ya sanar dashi yanzu zasu taho.


Bayan ya kintsa tsaf Dan Litti sai tsokanarsa yakeyi wai wannan zumudi haka? Shi bai taba ganin Ashaf a cikin wannan yanayin ba.

Ashraf dariya kawai yakeyi, ganin akwai sauran lokaci sosai yasa kawai ya wuce police station nan yai bailing Asim bai tsaya ya ganshi ba yai gaba.

Asim yayi baki sosai kamar ba shi ba ya rame sosai, ya fito ya tari adaidaita yai gida kamar wani almajiri.


Airport ya wuce suka hau jirgi shida Dan Litti sukai Abuja.

Sun saita abin suna isa ba dadewa Jirginsu Nafi ya iso.

Tunda Jirgin ya fara alamun sauka Ashraf ya kafe jirgin da ido, har ya sauka sannan a hankali alhazai suka fara fitowa kallan mutane kawai yakeyi yanasan ganin matarsa.

Bayan sun sauko ne suka taho ahankali aka musu checking nan ya hango Nafi.

Wani irin sanyin dadi ne ya dinga ratsashi ba shakka bai taba tunanin akwai 'ya macen da zatasa yaji irin wannan yanayin ba amma yanzu ya bada kai bori ya hau.


Su Nafi suna fitowa daga gun daga nesa ta fara kalla kalle, nan idanunta suka hango mata abin begenta.

Tsaya wa tai cak tana kallansa idanunta suka ciciko da kwalla, shikansa kallanta kawai yakeyi, Mumy ganin haka yasa taja hannun Inna sukai gaba.

A hankali suka fara takowa idanunsu nakan juna, Ashraf sam bai kula da wani agabansa ba sai jiyai ya bige wani, ya d'ago ya kalleta dariya ta sakar mai shima yai dariya sannan ya cigaba da takowa, sai da suka zo daf da juna ya kai hannu da niyyar rungumota, ta matsa da sauri tare da cemai "yaya mutane."

Kallan mutanen gun yai sannan yadan sauke fuska alamar takaici, tai murmushin farinciki ya matso kusa da ita yace " ni fa gaskiya so nake na jiki a kusa dani."

Kallan mamaki tamai tace " yaushe yayana ya zama haka?ba kunya?"

Mutanen gun ya kara kalla cikin takaici yace " muje masaukin da nasa a kama mana sai yamma jirginmu zai tashi."

Nafi ta daga kai nan suka fara tafiya a jere, ganin tana jan yar karamar trolly dinta yasa yakai hannu ya amsa.

Mamaki abin ya bata sai dai bata musa ba ta sakar mai tana murmushi.

Can inda yabar Dan Litti ya karasa nan yaga Mumy, da sauri ya mikama Nafi jakarta shifa sam idanunsa sun rufe bai kula da ita ba.

Nafi tai saurin matsawa daga gun jakar tai kamar bata ganshi ba.

Mumy tai dariya tace " Ashraf jakar zata fadi."

Kallan Jakar yai ya harari Nafi wacce ta matsa dan yasan da saninta, da sauri ya waske yace " Mumy lallabani tai akan in rike mata wai ta gaji."

Nafi ta zaro ido tace " a ina kenan akai hakan?"

Harara ya buga mata nan aka kwashe da dariya dukansu harda Inna dan ta gane lalai wannan shine sirikin nata.

Ashraf ne ya kalleta ba shakka ba sai an tambaya ba akwai kama sosai tsakaninta na Nafisa.

Nan ya gaida Mumy ya gaidata sannan suka shiga taxi suka nufi hotel din da suka kama.

D'aki uku yasa aka kama d'aya shida matarsa, daya Dan Litti dayan kuwa Mumy.

Sanda zasu kama D'an Litti har tsokanarsa yai yace "amma dai Mumy da Nafi ka kamama d'aya ko."

Harara ya bugamai yace " to wa ya sani?"

Ana zuwa Mumy ta kama hannun Inna sukai d'akinsu dan tasan da alama Ashraf ba kara a harkarsa ta yau.

Shikam ko a jikinsa ya kalli Nafi yace muje.

Tsayawa tai tace " ina zamu? Yaya tarefa muke da mumy?"

Ya hade rai yace " to ko gabanta zamu in jawoki jikina?"

Idanu ta zaro tace " ba kace yau zamu koma ba?"

Yace " dan yau zamu koma sai aka ce a hanani jin dimin matata?"

Zatai magana taji ya ja hannunta ya turata d'akin ya rufe.



Ita dariya ma abin ya bata tace " yaya wai yaushe ka zama haka?sam ka manta da wata kalma a hausa wai kunya."

Rungumeta yai ya saki numfashi yace " Ahh lalai nayi missing matarnan tawa."

Jikimta tadan janye kadan tace " nifa yaya a gajiye nake sannan wanka nakesan yi."

Zama yai akan kujera tare da juya kai gefe.

Nafi ta dauke kai itama ta dau towel ta cire kayanta ta d'aura sannan ta matso kusa dashi ta manna mai light kiss a lab'ansa tace " is that okay?"

Juyawa tai zatai gaba da sauri yasa hannu ya kamota ta fada kan cinyarsa ya kalleta ido cikin ido yace " Are u kidding me?"

Zatai magana taji bakinta a cikin nasa, wani salo yake mata wanda yasa itama dole ta fara bashi murtani, nan fa ya rabata da towel dinta ya shiga sarrafata ta nayanda yakeso, sai numfashi yake fitarwa itakanta tasan yayi missing dinta........

Sai da suka gama tukunna ya jawota jikinsa ya rungume yace " I really Miss u Feenah."

Yanda taji ya fadi sunan sai da tsikar jikinta ta tashi, idanu ta kafeshi dashi, baki yasa ya hura mata iska a idanun yace " kallanfa?"

Bata dauke idanunta ba tace " yayan dan kara fada."

Ya kalleta yace "mene? I miss u?"

Kai ta girgiza tace "a'a d'ayan."

Kallan mamaki ya mata yace " to mene?"

Tace " d'ayan please."
Yace " wai Feenah?"

Kai ta daga da sauri tace "bantabajin dadin sunan ba a bakin wani ba kamar kai."


Idanu ya kanne yace " badai so kike kicemin haka kikesan indinga ce miki ba?"

Shiru tai sannan tana wasa da gashin kirjinsa tace "mene? Bazan iya ba?"

Yace " sosai, dan ni Baby nake san cemiki dan haryanzu u are a baby."

Baki ta turo tace " salan ka faracemin baby daga na haihu ka koma cemin Nafisa?"

Cikin mamaki yace " saboda kin haihu sai kawai na daina cemiki?"

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login