Showing 69001 words to 72000 words out of 141466 words

Chapter 24 - ZUCIYA kowa da irin tasa Complete Hausa Novel

unknown   

13 Oct 2024

15930

bane yasa ya kalleta, itama cikin nata salon dan da saninta ta d'auko wayar tanasan tabbatar da abinda zuciyarta ke so, kallansa tai cikin shakka sannan ta kalli wayar, ta canzama Alamin suna daga My Number zuwa My Alamin, ganin sunan daya fito kan wayar yasa ransa ya sake b'aci dama gashi bai gama warewa ba a zuciye ya fizgi motar sukai waje.

  Nafi kam bata d'auki wayar ba sai tai kamar irin tsoron Ashraf takeyi,sunyi nisa akan titi ba wanda ya kula wani, Nafi ganin haka yasa ta d'aure tace " yaya baka tsaida magana ba akan tafiya..."
 Bata karasa ba taji yace " gobe ki shirya ko driver din mumy ne ya kaiki."

  She really feel disappointed ganin yanda ya bata amsa ba wani damuwa ko kulawa, wata zuciyar tace " dan kawai ya sake miki fuska yau kin dauka sanki yake? Stop dreaming Feenah."

  Kanta ta juya ta kurama titi ido, a cikim ginin Ado bayaro mall yai parking sannan ya fito, a hankali itama ta fito tare da kallan garin, hadari ne ya fara had'uwa.
 Ta juyo ta kalleshi taga yayi gaba, tsayawa tai cak ranta inyayi dubu ya b'aci ta bi bayansa da kallo ba tare da ta je inda yake ba, sai dayai nisa sannan ya juyo mamaki ya kamashi ganin bata taho ba tana tsaye a jikin mota sai idanu da ta kafeshi dashi.

  Shima tsayawa yai yana kallanta me takeyi acan?"
  Nafi ta juya tare da kifa kanta a saman mota ji take kamar tai kuka ko zataji dadi wannan dizgi har ina? Suzo tare amma ba magana sai kawai yai gaba ya barta, so yake ya nunama kowa bashida hadi da ita ko me?

  Jitai ance " in bazaki jeba shiga mota in maidake gida ko ki hau adaidaita ki tafi, kina tunanin banda abinyi ne?"

  Ta juyo ta kalleshi yana tsaye ya had'e fuska sosai, d'azu ta tuno sanda ya sakar mata fuska wannan wani irin mutum ne?"
  Ran Ashraf ya kara b'aci ganin wayar a hannunta, ta d'aure tace " yaya kasan ban taba zuwa ba amma kana ajiyeni kai gaba kabar ni, ya kakeso inyi?"
  Ranshi ya sake b'aci yace " bakida kafa ne ko kuwa jaririya ce ke?"

  Nafi ma cikin b'acin rai tace " duk da ni ba d'aya daga cikin abinda ka lissafa bace amma ai nima inasan kulawa, taya zamu taho tare ace kana can gaba ni kuma ina can baya?"
 Ashraf ya kalleta zaiyi magana yaji tace " so kake ka nunama kowa bakada alaka dani?na sani kafi karfin ajina balle har ka jera dani sai dai na rasa me yasa nakeji zafin hakan aduk lokacin da kamin, nasan da hakan har kasan zuciya ta to why nakejin zafi?"
 Ta fad'a tare da juyawa tana neman maida kwallarta, jikinsa ne yai sanyi sam matsalarshi kenan bayasan yaga ya sa mace kuka, kallanta yai sannan yace " zaki iya tahowa yanzu?"

  Kallansa tai sannan ta fara takawa a hankali, Yana gaba kad'an tana binshi a baya, har suka isa cikin shop right  nan ya nuna mata babban cart ita kuma ta jawo suka fara zagawa, ita take nunamai abin bukatar makaranta inta sa d'aya sai ya kara biyu a ciki su zama uku, haka suka sai kaya sosai, ita har tsoro take nawa za ace musu in akazo gun biyan kud'i?

  Bai bari taji ba ana fad'an nawa ne yai saurin mika Atm card dinsa nam aka cira sannan akasa wani ya kai musu mota.

  Suna fitowa sukaga gari ya turnuke sosai, nan sukai sauri suka shiga mota, ko fita daga mall din basuyi ba aka fara yayyafi, kafin kace me? Ruwa ya tsuge sosai ruwa mai karfin gaske wanda ko gaban mutum baka gani.

  Nan Ashraf ya gangara gefen titi yai parking, sunyi shiru sai kallan yanda ruwa yake sauka kawai sukeyi, Nafi batai auni ba taji muryar Ashraf cikin sanyi yace " karki sake cemin nafi karfinki wai ko na tafi saboda bazan iya jera wa dake ba."

  Kallansa tai cikin wani irin yanayi mai wuyan fassarawa ya juyo shima ya kalleta, ganin yanda take kallansa yasa yaji wani abu na ratsamai jiki, kansa ya d'auke da sauri, ya had'e rai sosai, Nafi ta matso sannan tace " Yaya ni..."
 Wayarta ce ta sake katseta ya juyo ya kalleta tare da kallan wayar, number d'azu ce, ta kalleshi cikin tsoro kafada ya d'aga mata sannan ya mata alama akan ta amsa wayarta.

  Jiki a sanyaye Nafi ta d'aga tare da sallama, Alamin yai ajiyar zuciya yace " At last kin d'au wayata."
 Nafi idanunta nakan Ashraf tace " sry d'azun ma wani abu nakeyi."
 Ashraf kam wayarsa ce a hannunsa yana dannawa sai dai hankalinsa na kan wayar da take.
  Alamin ya saki murmushi sannan yace " Feenah plz ki daina jamin rai wlh zuciyata zata iya kamuwa da ciwo in har baki tausaya kin amince da ita ba."

  Har yanzu idanta nakan Ashraf sai dai jin kalaman Alamin sun sa ta d'an sassauta murya kamar mai rad'a tace " Alamin ya kake so inyi wai?"

  Yace " ki amince dani na zama saurayinki ni kadai."
  Tace " bangane ka zama saurayina kai kadai ba??"

  Ashraf ne ya juyo ya buga mata wani mugun kallo wanda batasan sanda ta sauke wayar ba daga kunnenta hannubya bata akan ta bashi wayar ba musu kuwa ta mikamai ya sa hannu ya amsa tare da kashe wayar gaba d'aya, mamaki ya kamata a ranta tace ko kishin ne??
 Jitai yace " ku mata wani sa'in me yasa bakuda tunani ne?"

  Nafi ta zaro ido cikin mamaki tace name fa?

  Ya kalli wayar yace " ke kina ganin burgewa ne saurayi yaba budurwa waya ba wata magana mai karfi a kasa?"
  Nafi ta turo baki batare da ta amsa ba, yace darajarta take ragewa agunsa alama kuke nunawa na abin hannunsa kuke so.

  Nafi cikin takaici tace " ai ba ni nace ya bani ba sannan magana mai karfi ai za'ayita in na gama makaranta."

  Dariya taga yayi sannan taji yace " kin manta me nace miki kenan ko? Randa zakizo garin nan."
 Kallan mamaki tamai yace " cewa nai sai na yarda da yaron sannan zan baki takardarki."

  Kallan sa tai sai dai zuciyarta taji ba dadi haryanzu wato yana tunanin bata takarda ko??????

*THE INNOCENT TEAM*
[7/12, 12:06 AM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
       _ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
    ayushermohd.blogspot.com


*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡

  *45*

  Ranta yakai koluluwa gun b'aci Ashraf bai tsamani ba kawai yaga ta bud'e motar ta fita, ga ruwa ake sosai, da sauri shima ya bud'e kofa ya fita, tafiya kawai take tsabar ruwa batama san ina take sa kafarta ba, Ashraf ya hanzarta ya riko hannunta.

   Kallansa tai sannan ta fizge hannunta da karfe ta nemi ci gaba da tafiya, hannayensa biyu yasa ya rike kafad'arta ya juyo da ita saitinsa yace " Nafisa!!" ya fad'a tare da jijiga mata kafad'a, Nafi ta shiga neman kwace jikinta ganin yanda ruwa ke dukansu gashi da alama taurin kai take nemanyi yasa kawai ya d'agata cak yai mota da ita ahakan ma saj wutsul wutsul take, ya bud'e mota ya sata sannan ya zaga  da sauri ya shiga tare da sama motar lock.

  Nafi ta juya kanta gefe, hannunta ya kamo yace " menene wai?kanki d'aya kuwa?"
  Ta kalleshi da idanunta da suka ciciko cikin wani irin murya ta kalleshi tare da cewa " yaya ni nace ka aureni?"
 Kallan mamaki ya mata, ta share hawayenta duk da tasan abanza dan kuwa hawayen sai ma kara zubowa takeyi, ta kalleshi sannan ta cigaba " Yaya ni bw mutum bace?dutse ce ni ko kuwa?"
 Kallanta kawai yake sam ya kasa magana, hawayen da takeyi da kalamanta sune kawai ke ratsa shi, ta kara share wasu kwallan sannan ta cigaba " ka tab'a ganin inda mace a ranar da aka daura mata aure miji yake mata zancen saki? Ka taba tunanin yanda wannan matar zataji duk da yarintar dake damunta a lokacin??"

   Ashraf jikinsa ya mutu sosai, Nafi ta sake goge kwallar sannan tace " ka bani takarda ta yanzu inaji shine kawai abinda ya kamata, a gun iyaye da mutanen garinmu ne kawai kake mijina waya san abinda ke tsakanin mu? Ni kaina mantawa nake da auren ka akaina, baka tunanin halin da zan fad'a idan na fara kula wani?ku kuwa ba zunubi na aikata ba in nai hakan?"

  Ashraf ya kara rike hannunta yace " Nafisa!"

  Hannunta ta kwace ta kalleshi cikin idanunta da suke zubo da kwalla tace " na gode sosai daka taimakeni, ka kula dani ka kuma sani a makaranta sai dai ina ganin lokaci yayi da nima nake bukatar zuciyata ta huta da kokwanton ni matar aurece ko bazawara ko kuwa budurwa?ka bani takardata gobe in koma mahaifata."

   Idanu Ashraf ya runtse sannan ya bud'esu a hankali ganin yanda take kuka bai san sanda ya jawota jikinsa ya rungumeta ba, kokarin kwacewa ta shigayi sai dai ya riketa sosai ganin ta kasa kwacewa yasa ta rikeshi itama tare da cigaba da kuka, jikinsu ya jike shakaf.

  Kuka take sosai wanda ke taba duk wani lungu da sako na jikinsa, kanta ta kwantar a wuyansa a lokacin da ta fara tsagaitawa da kukan, jin jikinta yai ya fara d'aukan zafi ya daure ya d'agata sannan ya riko hannunta ya shiga hura hannunta da bakinsa yana murzasu, kallansa kawai takeyi tanajin wani irin sabon kaunarsa na ratsata, Why?? Meyasa ita da takesan ta daina sanshi amma takejin haka.

   Ya kalleta yace " zazzabi ke neman kamaki, me yasa bazaki min magana ba kika shiga ruwa?"

  Ta kifta ido sannan tace " yaya ka tab'a tunanin ya nakeji inkamin zancen saki bayan ban tabbatar da matsayin aurena ba ma? "
 
  Ashraf ya kalli yanda jikinta yai sharaf sannan ya kalli idanunta cikin dan fada fada yace " ina miki zancen jikinki kinamin zancen abinda ba shiba?"

   Idanu ta kafeshi dashi, ya kalleta shima, kallan juna suka shigayi dukansu wani abu na ratsasu, Nafi ta daure ta d'auke idanta ta juyar da kanta jikin window, Ashraf ya sa hannu ya rikota tare da jawota kusa dashi.

  Idanun Nafi ne suka fifito ya kalleta yace " kalleni.!
 A hankali ta d'ago tana kallanshi ta maida kanta kasa, jikinta ne ya mutu ganin ya sa kanta akan kafadarsa yace " ki zauna a haka na yan mintina."

   Why? Tafad'a a hankali yai gyaran murya yace " zai taimakawa jikinki dake neman kamuwa da zazzabi."
  Tai murmushi batace komai ba, ya sake gyaran murya yace " ba kuma cewa nai kiyi hakan ba da wani."
  Tace " me yasa? Naga taimako ne."
 Ya harareta yace " ni ai haryanzu akwai aurena akanki."
Tad'an tab'e baki tace " auren da ni kaina ban tabatar ba."
 
Me kikeso ki tabbatar? Idanu ta rufe kamar mai bacci dan batada amsa.
Ya kalleta sannan yai murmushi.

  Ganin ruwa ya fara d'aukewa yasa ya gyara mata kwanciya zuwa kujerarta duk da yasan ba Bacci take ba, sannan ya tada mota ya jata a hankali.

   Nafi kam juyawa tai tana murmushi lalai wannan rana ta shiga cikin tarihin rayuwarta ba wai cewa yai yana santa ba sai dai ta rasa dalilin farincikin nata.

  Sun isa gida sannan yai parking yasa hannu a wuyanta yaji dumin kadan ne sannan ya kalleta yace " mai baccin karya ki tashi ki shiga ciki ki dan zuba ruwan zafi a jikinki kisa kaya mai dan nauyi."

  Kai ta d'aga ba tare da ya juyo ba, sannan tai sumsum tai waje ya bita da murmushi.
 Yasa ankai mata kayanta sannan ya wuce b'angarensa yai wanka shima da ruwan zafi sannan yasa kaya ya kwanta akan gado tare da dora hannunsa akan goshinsa, meke damunshi? Me yasa yake abu kamar ba shi ba, me yasa yake yawan murmushi tare da yin abubuwan da bai saba ba in yana tare da yarinyar nan?

   Wata zuciyar tace badai kamuwa kafarayi da santa ba? Kai ya girgiza da sauri yace " No way, how can i...."

   Shiru yai yana tuno sanda ta kwanta ajikinsa tana kuka, murmushi ya saki tare da lumshe ido......

   Nafi kam haka taitayin komai cikin farin ciki har Little ta ke tambayarta yau meya same ta haka?Nafi kawai sai dai tai dariya..

  Washegari litinin da safe Ashraf ya shirya ya tafi gun aiki sabosa sunada Meeting yau ranace babba agunsa don project din da yai kusan wata 6 yana planning yau zaiyi presenting dinsa a gaban directors na company din.

  Karfe goma ne presentation din dan haka ya isa gun karfe 9 da kansa ya Shiga gyara gun har 10 tai, mamaki ne ya kashi ganin har 10 da rabi ba kowa a gun sai shi kad'ai nan ya fito ya fara dan zazagawa, wani member na team dinsa ya kira yace " ya dubamai ko ancanza lokaci ne."

  Yana nan a tsaye sai ga Mansir ya taho, ya karaso inda Ashraf yake yace " har an fara?"
  Ashraf yai kasa dakai cikin rashin jin dadi yace " ba wanda yazo shiyasa nake tunanin ko ancanza time ne."

  Kawubya d'an nuna rashin jin dadinsa a fili sannan ya d'aga waya ya kira Secretary dinsa, ko me ya cemai ya kashe tare da kallan Ashraf yace " Ashraf ance project dinka plagiarism ne."
 Cikin tsananin mamaki Ashraf yace " Ban gane ba?"
  Kawu yace haka aka sanar da directors din ciki kuwa harda members na team dinka sannan project din har anyi lunching dinsa ma a comapny din da muke rivals." yana kai nan yad'an bubuga kafadar Ashraf sannan ya juya ya tafi.

   Da kallo Ashraf ya bishi ya saki wani murmushin takaici a ransa yace " ko kuma ka d'auka ka basu ba? Kana tsoron hakan zai sa mutane suyi acknowledging dina."

  Ya runtse ido saboda wani takaici da ya kamashi, yai kwafa tare da zubar da takardun yai waje.

   Mota ya shiga ransa yakai kululuwar b'aci ya dage ya daki sityarin mota da hannunsa tare da kwantar da kanaa jikin kujera ya saki wani huccin takaici.

   Little ce ta kirashi sai data kusa katsewa ya d'aga sai dai muryar Nafi yaji tace " Yaya ina kwana?"
 Ya amsa a hankali, tace " driver din yazo zamu tafi gashi bakanan bare muyi sallama."
  Yace " da inzaki tafi makarantar sai kinyi sallama dani?"

  Mamaki ya kamata tace "Yaya gani nai...."
 Katse wayar yai sannan ya kasheta gaba d'aya ya runtse idansa da karfi zuciyarsa na kara tafasa.

  Nafi kam mamaki ne ya kamata, cikin takaici ta shirya da taso in sukai waya yace ta bari ba yau ba sai dai yanda ya amsa mata yasa taji batasan zaman gidan ma sam a wannan lokacin, ta kalli Little ta mika mata wayar Alamin sannan tace " ki bashi wayarsa kicemai na koma skul inda rabon mu sake had'uwa to inkuma babu Allah ya hada fuskokinmu a aljanna."

  Little ta kalleta fuska a hade tace " wai dan Allah bazaki hakura da tafiyar nan ba?"
  Nafi ta girgiza kai cikin takaici tace " karki damu little kwana nawa ne?"
 Little ta harareta sannan tace " wani irin sako ne wannan haka kikeso in fad'ama al'amin din?"
 Tace "eh, bari naje nama Mumy sallama."

  Sunyi sallama da Mumy, sannam ta shiga mota ranta duk ba dadi suka tafi.....

  *ILYSM MY FANS*

[truncated by WhatsApp]*ZUCIYA*
       _ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
    ayushermohd.blogspot.com


*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡

  *46*

   Ashraf ya gyara zamansa a cikin mota sannan ya kira lawyer kuma abokin babansa, bayan sun gaisa ne yace " Uncle taimako nake san kamin."
 Yace "me kakeso Ashraf kasan saboda kai nake ta d'aga time din retire dina."

 Ashraf yai murmushi sannan yace " Nasani Uncle please so nake kaje Slc company kace ina tuhumarsu da satarmin project ka basu takardar shaidar sammaci a kotu."

  Lawyer yai murmushi yace " da alama yanzu ka shirya fito na fito da su."
 Ashraf yai dan kwafa yace " Uncle a duk sanda sukamin abu kalaman Abba daya rubutamin shi ke fad'omin sai dai inaji ajikina yanzu shima Abban bazaiso in barsu su kara b'ata ba."
  Lawyer yai dariya sannan yace " Hakane, dama ance Eye for eye, tooth for tooth."
 Sunyi sallama Ashraf ya bud'e mota ya fito, Asim ya gani ya nufoshi yana wata tafiyar kasaita.

  Ashraf yaja tsaki yace " The biggest fool is here."

  Asim ya karaso cikin isa sannan ya shiga tafama Ashraf, kallansa Ashraf yai yace " kai kuma me ke damunka?"
  Asim ya saki dariya sannan yace " Ashraf shi yasa nace maka ka kiyayeni ni ba sa'an yin ka bane."
  Kallan sa Ashraf yai yace " kana tunanin kaika aikata hakan?"
 Asim ya jinjina kai yace " sosai ma tunda ninasa aka sace project din."
 Kai Ashraf ya jijiga alamar tausayawa sannan ya matso yad'an bigi kafadar Asim da hannu yace " u are such a big fool, ka daiyi tunani dakyau amma ninasan kanka bashida wannan basirar, kaidai basirarka d'aya ka turo a kasheni."
Yana kai nan ya juya yai gaba.

  Asim yabishi da kallo cikin kuluwa yace " me? Yasan Abbanane yasani ko me?"kai ya jijiga alamar a'a sannan yace " ai ba yanda zaiyi ya zargi mijin mahaifiyarsa.

  Ashraf kam office ya koma ya cigaba da aikinsa, wanda akasa ya saci takardun a cikin members dinsa sai b'uya yake yi, sam Ashraf bai kulashi ba sai ma wani abu dake mai yawo a zuciya, wato kawu abin tsoro ne na gaske, ya tura d'ansa yayi abu yanzu in asiri ya tuno fa? Lalai mutumin nan wato akan abinda yakeso he can use anyone."
 Yaja tsakin takaici inya tuna uwarsa ma amfani yake da ita.

  Sai yamma ya tashi nan lawyer ya sanar dashi yace Slc ya sanar musu sai dai sunce a jira director ya shigo gobe dan shine yai proposing din project din.

  Gida Ashraf ya wuce, yana shiga yai parking sannan ya kira Little a waya, bayan ta d'aga ne yace " turomin kawarki."
 Little tace " wa kenan?"

  Ashraf ya had'e fuska yace " wace kawa zance ki turon bayan Nafisa."
 Da mamaki tace " naga kunyi sallama d'azu ta tafi ai."
Da sauri taji yace " bangane ba? Ina ta tafi?"
 Little tace "Skul ba ta kiraka ba?"
Katse wayar yai sannan yai wirgi da ita gefen

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login