Showing 60001 words to 63000 words out of 141466 words

Chapter 21 - ZUCIYA kowa da irin tasa Complete Hausa Novel

unknown   

13 Oct 2024

15904

tayi ai aikinta ne ba nawa ba."

Matsowa ya farayi ita kuma tana matsawa baya, tsoro takeyi sai dai itakam bazata taba yadda ta gyara musu falo ba wato ta gyara suzo su zauna suyi soyayyarsu a ciki?
Jin tazo jikin bango yasa ta tsaya tare da kallansa a tsorace, Ashraf ya kalleta sannan yace " Maimaita kalamanki."
Kasa tai da kanta ba tare data maida ba, ya saki wani murmushi yace " in aka tambayi iyayenki matsayina a gunki me zasuce? Ahh i am really curious."
Zaro ido tai cikin mamaki tace " ban gane ba."
Yace " Menene matsayina a gunki?"
Gabanta ne ya fad'i da sauri tace " Yayana mana."
Yace " Good."
Menene matsayinmu a gun iyayena da 'yan uwana?
Tace " Wanda ya taimakeni."
Yace " Bravo!, to menene kuma matsayina a gun 'yan kauyenku da mahaifinki?"
Baki ta shiga motsawa tana san magana sai dai bazata iya fad'a ba.
Ya juya ya fara tafiya sannan yace " in kina san 'yancinki kimin biyayya sai in baki takardarki cikin sa lama ki auri wanda ranki yakeso."
Cikin takaici tace " in naki fa?"
Yace " Well! Wannan kuma ya rage naki kinsan dai ba'a aure kan aure ko? Haka nan zakiyi ta zama har ila masha Allah."
Yana kainan yai hanyar dinning.
Tabishi da kallan takaici, ba ma zaka zauna dani ba sai dai haka zan ta zama har ila masha Allahu, lalai ma Ya Ashraf.....

Cikin takaici ta shiga gyaran gida ranta inyayi dubu to fa ya b'aci, takaici duk ya turnuketa, ko inama wannan matar tasa taje? tai maganar ranta a b'ace.
Hotunsu ta kalla dake manne a falo sunyi masifar kyau kamar me, taja tsaki sannan tace " Aikin kawai ko kyau ma."

Lol nikam ai dariya ce ta kamani na kara kallan hoton wanda yaune rana ta farko danaji an kushe wannan hoton.....Su Nafi ko me yasa akaga munin hoton da ni kaina na bash A1?????


*THE INNOCENT TEAM*[7/4, 11:51 PM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
  Kowa da irin tasa

   ©Ayusher Mohd.....

38

    Tsayawa yai cak cikin tsananin mamakin Nafi yarinyar da a iya saninsa sanda ya d'aukota ko dukanta zakai bazatai magana ba illa ma inka gama ta b'uya a wani gun tai kukanta yau kuma itace........
  Katsemai tunani Anisa tai da zanzaro ashar, tace " Lalai yau za'ayi kan babban b*********, ni kika rikema hannu?"
 Nafi ta sake mata hannunta batare da ta tanka mata ba sai neman giftata datai zata wuce.
 Cikin zafin rai Anisa tasa hannu iya karfinta ta hankad'a Nafi, saura kiris ta kifa taji an tareta tare da rungumeta, nan suka karasa kasa su biyu, basai ta tambaya ba tasan waye ko ince zuciyarta ta isar da sakon waye zuwaga gab'obinta.

   Aneesa mamaki ya kamata ta saki baki dalala tana kallan wannan al'amarin shikam Ashraf suna karasa faduwa, ya mike tare da sake Nafi sannan ya kalli Aneesa cikin fad'a yace " kinada hankali kuwa? Yanda kika hankad'ota inta fad'a kan wani abu fa??"

   Aneesa kam cikin mamakin kalamansa tace " Ya Ashraf kana nufin tare mata kai ko me?"
 Ya kalli Nafi cikin b'acin rai yace " wa zan tare wa? Ina miki fad'a akan zakiyi b'arna wata rana in har baki kula da abinda kikeyi ba kina min wani zancen banza."

Aneesa tace " Naji na d'au laifina amma inaso inji me yasa ka tareta kai ka fad'i ita kuma ta fad'i a jikinka?"

  Kansa ya shafa da hannu cikin takaici ya kalli Nafi yace " malama kama hanya ki fita, sannan in sakeji kin raina na gaba dake wlh inbakiyi wasa ba sai jikinki ya gaya miki."

  Nafi kalamansa sunsa gwiwarta tai sanyi ranta kuma ya sosu sai dai ya ta iya? Mikewa tai jiki a sanyeye tai waje.
 Tana fita Ashraf ya kalli Aneesa cikin takaici yace " ke bakiji kunya ba??yarinya karama ita take nusar dake nan d'akin aurenki ne ba wai na wani ba? Akan me zatama gyara miki gun da yazamar miki dolenki?"

   Aneesa wacce idanunta suka ciciko tace " Yaya nikam inaji a jikina kamar ba auren soyayya mukai ba, kamar ni kad'ai ce nake sanka kai kuma sanda kakemin kawai na 'yan uwan taka ne."

  Idanu ya runtse sannan ya kalleta yace " a soyayyar danasan ina miki da, banaji yanzu ina miki ko rabinta sannan bana tsamannin zaki tambayeni dalili ganin ke kikafi kowa sannin abinda ya jawo hakan."
 Yana kai nan ya zari makullin mota yai waje.

  Aneesa ta fashe da wani irin kuka na bakin ciki itama ta fito tai b'angaren Ummanta tana kuka wiwi kamar wacce akama duka.


  *************

  A b'angaren Asim kuwa yana ganin su Ashraf sun tafi yai b'angaren mahaifinsa cikin tsananin tsoro da firgicin kalaman Ashraf.

   Yana isa ya kwankwasa tare da murd'a kofar ba tare da ya jira an bashi izini ba.
 Kawu wanda ke zaune gaban wani karamin akwati (kit) yana duba wasu takardu yanajin motsin mutum yai saurin rufe takardun tare da maidashi cikin kit d'in, yana kokarin tura kit d'in karkashin gado Asim ya fad'o d'akin tare da kallan mahaifin nasa.
 Shikam Kawu da sauri ya karasa turawa sannan ya had'e rai tare da cewa " Kai Asim bakada hankali ne zaka fad'omin d'aki ba sallama?"

  Asim ya karaso kusa da mahaifinsa tare da tsugunawa a gabansa yace " Abba ya zanyi?"
 Cikin mamaki yake kallansa yace " Da me fa?"
 Asim ya share zufa nan ya sanar dashi duk abinda ya faru sai dai ba fad'amai da sanin Umma a harkar ba.

  Kawu ya kalleshi cikin b'acin rai sannan yasa kafa iya karfinsa ya ture Asim, ya cigaba da magana cikin fad'a, Asim me yasa ne sam bakada hakuri? Banine nace kabar komai a hannuna ba?"

  Asim ya rusunnar dakai yace " Abba kayi hakuri wlh ni sam banasan ganin yaron ne."
 Tsaki kawu yaja sannan yace " zancen banza ma kakeyi, yanzu idan wad'anda ka tura sun kama Ashraf kenan 'yan sanda suka zo fa?"
 Kana tunanin bazasu sanar dasu kaika aikosu ba? Daganan sai me? Kamaka zasuyi a banza."
  Asim yai kasa dakai cikin dana sanin gaggawar daya aikata, kawu yacigaba " ni nace kabar komai a guna, akan me zamu halakar dashi bayan bamu gama sannin iya dukiyar dake karkashin sa ba?"

  Asim ya jinjina ma mahaifinsa kai sannan ya bashi hakuri, nan kawu ya sallameshi tare da zama akan gadonsa yai shiru yana tunani, can cikin wata irin murya yace.


" Yaya ya zakayi??? D'an da kakeji duk duniya baya shi gashi a tafin hanuna, ya auri 'yata sannan matar fa kake santa kamar ranka ta dawo karkashina." Wata irin dariya ya saki wanda ni kaina saida tsoro ya kamani, da sauri nabar d'akin ina mamakin dama haka mutumin nan yake??? Lalai wata zuciyar akwai hassada da mugunta a cikinta.

   Asim na fita yai murmushin farin ciki tare da kara kallan kofar d'akin yace " Kai!!!! Amma Abba karshen mugu ne."
 Ya sa dariya sannan yace " ko menene a  akwatin nan???"
 Kad'a kai yai ya nufi b'an garen Umma, ya shiga kenan ya zauna yana jiran ta fito daga b'andaki sai ga Aneesa ta shigo da kuka.
  Cikin kulawa ya mike ya rungumota yana tambayarta menene? Aneesa kam kuka take sosai, nan Umma ta fito ta samesu a haka.
 Itama zama tai suka cigaba da tambayar Aneesa abinda ya sata kuka, Aneesa cikin kuka tace " Umma Ba Ashraf bane ya fifita yarinyar nan a kaina."
 Cikin rashin fahimta Umma tace " Ban gane ba?"

  Asim yace " Malama dalla daina mana kuka ki fad'a mana menene ke faruwa."
 Hawayenta ta share ta shiga sanar da su duk abinda ya faru tun daga farko har karshe."
  Umma ta mike cikin fad'a tace " Lalai za'ayi tashin hankali a gidan nan."
 Asim ya mike tare da cewa " akwai meeting dole ne yau ayi taron gaggawa na gida dan kuwa Ashraf yayi kadan ya wulakanta mana ke."
 A zuciye yai waje......

  *****************


   Nafi kam tana fita daga b'angaren Ashraf ta nufi nasu b'angaren taje shiga taji ance " Yaya Feena."
 Juyowa tai tare da kirkiro fara'a tace " My Amrah kece da kanki?"
 Amrah tai murmushi tace " yaushe kuka dawo?"
 Nafi tad'an jujuya kai sannan tace " ni kadai na dawo."
 Amrah tad'an yi hucci kad'an kamar babba, Nafi tai dariya tace " Yaya Amrah ya akai ne?"
 Tace " Mumy ce tace " in mun dawo daga makaranta muzo gun yaya Little ta mana wanka sannan ta d'auko mana kaya."
  Nafi ta d'an canza fuska kad'an tace "Amrah naji haushi fa! Wato ni bazan iya muku abinda Little zata muku ba ko me?"
  Amrah ta matso kusa da ita tace " Yahkuri Yaya Feenah wlh ba haka nake nufi ba."
 Nafi ta kama hannunta sannan tace " naji muje mu taho da Afrah." 
 Nan suka fara tafiya hannayensu rike da juna.


    ***************

A can kauye kuwa Datti yana cikin tsananin farin ciki da walwala, a 'yan shekarun nan dabobbinsa sun kara bunkasa sosai yazamo kaf kauyen garin ba wanda ya kaishi yawan dabobbi, shi kadai yake rayuwarsa cikin farin ciki ba wanda zai kashema kud'i bare har arzikinsa ya ragu.

   Sam bai damu da halin da Nafi take ciki ba bare kuma matarsa da d'ansa da suka gudu.
  Duk sanda aka tambayeshi gidan Nafi sai yace sai dai a tambayi Dan Litti dan kuwa shi bazai iya gane wa ba, hakan yasa duk 'yan garin sun d'auka da gaske yaje gidan 'yar tasa.
  Sanda Dan Litti yai wata 5 a garin kachako yad'an tara kud'insa ya shiga garin kano neman Ashaf sai dai duk yanda ya nemesu ya kasa samunsu kasancewar garin da girma sannan baisan wani kwatance ba sai Ashaf mijin Nafi, wannan yasa duk inda ya tambaya sai dai amai dariya gani suke kamar shirme yake ko kansa ne ya tab'u.

  Bayan kud'in hannunsa sun karene ya koma garin kachako ya cigaba da achabar sa har ya d'an samu wasu kud'i, ya sanar da uban gidansa akan zaije kauyensu ya dawo.
  Mamaki ne ya kamashi ganin kowa ya ganshi sai ya tambayeshi wai 'yar gidab Datti a wani irin gida akai kaita? Wasu ma cewa suke zasuzo ya kaisu.

   Datti yanajin labarin D'an litti ya dawo ya taho takanas ya tareshi suka keb'e, Datti ya kalleshi yace " ya kaje gidan?"
 Dan Litti ya girgiza kai alamar a'a, Datti yace " ka taimaken duk wanda ya tambayeka gidan Nafi kace musu munje ka taimaka min."
  Mamaki ya kama d'an Litti yace " What u say?"
 Datti yai tsaki yace " malam ni banasan wannan yaren arnan naka kamin hausa."
 D'an Litti yai saurin rufe baki dan yace ya daina turancin shima.
  Nan Datti ya lalaba Dan Litti akan yai karya wai sunje gidan Nafi.
 Shikam d'an litti ko sati baiyi ba ya koma garin kachako ya cigaba da kasuwancinsa, ganin yayi abokai acan ga uban gidansa na sansa sannan can yafi kawo masa kud'i.

   Wannan Kenan....


   To be continue ......


  *THE INNOCENT TEAM*

( _Dan Allah kuyi hakurin jina dakukai shiru wlh Wayatace tad'an same matsala sai do akai resetting d'in d'inta Tukunna.....Thanks 4 ur Love._ )
[7/5, 6:20 AM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
  _Kowa da irin tasa_
  
*Na Ayusher Muhd*

  39


    Nafi ta shiryasu tsaf sun zauna a falo sunata hirar su, labarin makaranta kawai suke bata itakam kai kawai take d'agawa amma sam hankalinta ba'a gunsu yake ba, abubuwan da suka faru a d'akine suke dawo mata.

   Ta zarfafa cikin tunani sam bataji shigowar Little ba, sai jitai an dafa ta, ta d'an xabura kad'an sannan tace " Amrah me kika ce?"
 Little ta zagayo ta gabanta tare da harararta tace " Feenah wato baki mayi tunani na ba ko?"
  Nafi ta kalleta sannan tai murmushi tace " My Little tuba nake wlh sam hankalina yayi wani gun ne."

  Little ta zauna kusa da ita tare da cewa " Alamin yau ai karamar hauka yaso min."
  Nafi ta d'an tabe baki tace " Name kuma?"
 Little ta girgiza kai cikin takaici tace " wai shi a dole ke da Ya Ashraf akwai wani abu a tsakaninku."

  Nafi ta zaro ido tace " kamar ya kenan?"
 Little ta d'aga kafad'a tace " ohon masa, shi wai yanda kukeyi keda yaya sam bayaso, hankalinsa bai kwanta da yanayin yanda kuke ma juna ba."

  Nafi tasa dariya sannan tace " lalai da alama baisan Ya Ashraf ba shiyasa, me zaiyi dani?"
 Little ta d'an harareta tace " kijiki ke kuma, wai ashe yaje gunsa kafin ki fita yana gaidashi amma yaya wai da kyar ya amsa mai."
  Nafi tad'an turo baki kad'an tace " wannan kuma ai yanayinsa ne ba wani abu ba."

  Little tace " Na fad'amai amma kamar zigashi nake, sam ya hanani zama agun kamun nan shidai wai sai na fad'amai ko kina sansa."

  Tsaki Nafi taja tace " daga had'uwa sai soyayya sai kace wata taxi?"
 Little ta kwashe da dariya tace " Love at first sight yake so ku zama."
 Nafi ta had'e fuska tace " lalai wayaga."
 Dariya sukai a tare.

    Bayan sallar sukaji kararrawar tarawa, Little cikin mamaki tace " Meeting kuma?"
 Nafi tace " Ai nikam kafin ki dawo nayi bacci."
 Mikewa Little tai tace " Bazaki ba?"
 Nafi ta jawo pillow ta kishingid'a sannan tace " Family Meeting."
  Little ta harareta sannan ta mike tai waje.

    Nafi ta gyara kwanciyarta tare da kalan wayar da Alamin ya bata, kai ta girgiza alamar a'a dan zuciyarta na raya mata ta kunna wayar.

   A can falo kuwa kowa ya hallara, Ashraf ne ya shigo daga karshe, ya ja kujera ya zauna.
 Kawu ne ya fara sallama nan ya tambayi dalilin taron?

  Asim ne ya mik'e sannan yace " Abba in anci abinci zan sanar da kowa."

  Anci ansha kafin Asim ya mike yace " A gaskiya Abba bazan juri ganin abinda Ashraf yakema kanwata ba, yau cin mutuncin har yakai ya fifita wata kucakar 'yar kauye akan matarsa."

  Wani murmushi Ashraf ya saki, Mumy kam kallan Ashraf tai cikin damuwa, ganin abinda yai yasa ta fara tsoron karfa ya b'allo wata maganar dan tasanshi sarai.

  Kawu ne ya katseta da cewa " Ban fahimceka ba, Fad'an tsakanin Ashraf ne da Matarsa?"
  Asim yace " Eh."
 Kawu ya kalli Ashraf yace " Ashraf ya akai?"
  Kallan Asim yai ba tare da ya d'auke idansa ba yace " Asim za'a tambaya ai kawu ni me na sani banda sani da akai nazo nan."
 Kalaman sun ba kowa haushi sai dai ya zasuyi? Kawu ya kalli Anisa yace " ke me ya faru?"

  Little kam fatanta Allah yasa ba Nafi ake nufi ba.
 Anisa ce cikin sanyin murya tace " yarinyar nan 'yar kauye ce ta nemi kawomin raini dan na sata aiki shine na mata fad'a akan ni ba sa'arta bace shikuma shine ya shigar mata ya wulakantani a gabanta."

  Mumy ta kalli Ashraf, Kawu ne yace " Ashraf me yasa ka wulakanta matarka akan tana nunama yarinya karama 'yar kauye laifinta?"

  Ashraf ya kalli Anisa sannan ya kalli Kawu yace " wannan kuma itace takeda amsar tambayar, me yasa nabi bayan yarinyar? "

   Mumy ta kalleshi tace " Ashraf me yasa kai haka?"
 Bai amsamata ba sai juya kai dayai, ya sani sarai dama yarda zatai da duk abinda akace mata yayi.
 
  Anisa ta kalleshi cikin sakalcin magana tace " Yaya kaine fa kamin fad'a akanta."

  Ashraf ya mike tsaye cikin takaici yace " fad'a? Ai banaji wanda na miki yau sunanshi fad'a, sannan Umma ki maida 'yarki kusa dake dan banaji tasan me ake nufi da aure, da kuma darajarsa."

  Yana kainan yai waje abinsa.
 Cikin zafin rai Asim ya mike ya sha gabansa yace " ce maka akai mun gama magana?"

Ashraf ya kalleshi yace " Me ya rage?takardar kanwarka? Ko 'yan daban daka turo d'azu?"

  Asim ya kalli Ashraf cikin wani irin yanayi, Ashraf ya bubugamai kafad'a sannan yai gaba.

  Bakin ciki ne ya cikama Asim ciki a zuciye yai wani irin ihu.

  

    An gama taro kowa zuciyarsa ba dadi, Little ta shigo d'aki.
A kwance ta hango Nafi rike da Qur'ani a hannunta.
Ta shiga ta zauna kusa da kafarta.
 Nafi takai aya sannan ta kalleta tace " kun gama?

  Little tace " A kanki ma akai taron."
 A tsorace Nafi tace " ni kuma? Me nai? Nashina."

  Little tai d'an yake nan ta zayyane mata abinda ya faru......


 Asuba ta gari

  *[truncated by WhatsApp]
[7/5, 7:48 PM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_

© *na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com


*HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡

*40*

Nafi ta mike a zabure tace " Haka suka ce? Wow! Lalai na jinjina ma matar Yaya." ta fad'a tare da tafa hannunta.

Little tai dan dariya tace " hmm dan ma Ya Ashraf suka samu? "
Nafi ta koma ta zauna tare da jan tsaki tace " Ni fa gani nake Yaya nada zafi amma baya iya wani abun kuzo mu gani. "
Little tai murmushi tace " Nafi bakisan halin Yaya bane, yanada masifar zuciya da taurin kai abu d'aya ne yake hanashi yin komai a gidan nan. "

Da mamaki Nafi ta kalli Little tace " me kenan? "

"Mumy. " Little ta fad'a fuskarta d'auke da damuwa, sannan tacigaba "Nafi yau zan fad'a miki tarihin gidan nan. "

Da jin haka Nafi ta gyara zama cikin zukud'in san taji meke faruwa.

*TUNA BAYA.*

" Kakan Ashraf wato Sale ya kasance mutumin wani kauye ne dake garin Kila a karkashin jahar Jigawa, ya taso cikin wahala kasancewar mahaifinsa bashida hali sannan shi kad'ai ne namiji kuma babba agun mahaifinsa.

Wahala kam na rayuwa ya shata, dan mahaifinsa ba cikaken lafiya gareshi ba, duk wani arzikin gona iin ya samu akan kannensa da iyayensa yake tafiya, hatta kayan da yake sawa sun jeme saboda tsabar wahala.

Sam bai taba tunanin aure ba ganin nauyin dake gabansa sun mai yawa, har Allah ya kawo kanwar mahaifiyarsa ita da 'yarta sukazo hutu gidan.
Tunda Sale ya ganta yaji ya kamu da santa sai dai ganin ita daga birni take yasa ya kunshe abinda ke ransa.

Fanna wanda take 'yar kanwa ce ga mahaifiyar Sale a garin maiduguri suke, yarinya ce wacce ba

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login