Showing 57001 words to 60000 words out of 141466 words

Chapter 20 - ZUCIYA kowa da irin tasa Complete Hausa Novel

unknown   

13 Oct 2024

15931

Ya karasa gun aikinsu nan ya tadda 'yan team d'insa sun dad'e da zuwa, nan ya zauns suka fara abinda ya kawo su.


Su Nafi ansha kwalliya, suna fitowa Habib na yin parking, tundaga nesa Little ta hangoshi ta saki wani lalausan murmushi na farinciki, Nafi ta kalleta sannn ta kalli inda take kallo ganin Ya Habib yasa tai murmushi itama tace " Little a dinga kokarin dannewa irin wannan nuna soyayya kirikiri haka??"

Little ta harareta sannan tace " haka nace miki?"
Nafi ta d'an rangwad'a kai tace " Little kenan."

Juyowa yai shima ya hangosu, nan ya tsaya tare da kurawa Nafi ido, gaskiya yarinyar nan type d'insa ce ba karya, har suka iso gun yana kallanta, Nafi ta d'an had'e fuska tare da kawar dakai ge.

Little ta matsa gunsa tace " Ya Habib daga ina haka?"

Idanunsa nakan Nafi yace " wlh wucewa nazo yi shine na shigo."

Little ta kalli Nafi dan taga yanda yake kallanta, sai dai bata kawo wani abu ba tace" Nafi tayi kyau ko yaya?"

Habib yai murmushi yace " Sosai ma kuwa."

Nafi ta matsa daga saitinsa sannan tace " inafa wani kyau dan kowa yaganki yasan kece kikai kyau."

Ta fad'a tare da cewa " Ya Habib ko ba haka ba?"
Ya kalli Little kunya tad'an kamashi yai wani murmushin burin kunya yace " dama ai Princess daban ce."

Little ta saki murmushin farin ciki.

Little ta kaleshi cikin kauna tace " Ya Habib yaushe zaka tafi?" yace " zuwa la'assar dan inasan ganin Ashraf."

Kai little ta d'aga tace "Allah yasa mu dawo mu sameka."

Yace Ameen tare da satar kallan Nafi.

Nan sukamai sallama suka shiga motar Little sukai gaba.


Su Umma kam da Asim suna zaune a falo suna jiran good news tunda sunga fitarsa daga gidan da motar mercedes wanda hakan yasa Asim ya sanar dasu sunan motar da number ta, sai dai jin shiru har shad'aya ba labari yasa Asim ya kira, sun sanar dashi har yanzu motar bata wuce ba, nan suka kara jinkirtawa zuwa azahar, nan ma akace motar bata wuce ba, cikin takaici Asim ya kira wani ma'aikacinsu na company ya tambayeshi Ashraf yazo? Ga mamakinsa jiyai ance tun d'azu yana nan.

Haushi da takaici suka turnukeshi ya kirasu ya hau su da fad'a sannan yace " su tafi daga gun kafin ma a zargi wani abun.?"






*THE INNOCENT TEAM*Copied By
YAYA HAYAT
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
Cool novel, makeup and kitchen2⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen3⃣)


WHATSAPP NO:
+2347039625239
[7/2, 5:42 AM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
_ĸowa da ιrιn тaѕa_

*Wannan Shafin Sadaukarwa ce gareku Haske Writers Association*

*©na Ayυѕнer Mυнd*
ayushermohd.blogspot.com


*Wattpad As_AyusherMohd*


{ *36*}


Little ta kai bakin gate wayarta ta fara kuka, Nafi ta zaro wayar daga cikin jakarta ganin Sunan Big Bro yasa Nafi tai saurin mika mata, Little ta amsa tare da gaidashi.

Nafi duk ta tattara hankalinta kan Little tanasan taji me yake cewa sai dai batajin komai sai amsar da Little ta bashi "Yaya har mun fito fa?" tai maganar tare da had'e fuska, Nafi sai ji tai tace " Yaya dan Allah ka....." da alama katseta akai wanda ta karasa maganar da cewa " To Yaya."

Tana kashewa ta kashe motar tare da kallan Nafi ranta duk a b'ace, Nafi ta kalleta tace " ya akai?"

Little tace " wai Yaya ne yace kije ki gyaramai b'angarensa."
Nafi ta kalli Little da mamaki tace " Ni kuma?"
Little ta d'aga kai alamar eh, Nafi ta canza fuska sannan tace " Matarsa fa? Ita bata iya gyaran bane ko me yake nufi?"

Little tai karamin tsaki tace " wannan uwar san jikin me zatayi? Banda chatting."

Nafi ta d'aure fuskarta tamau sannan tace " Mu tafi kinji?"

Little ta kalleta cikin mamaki tace " Me kike nufi?"
" Mu tafi inda zamu."
Little kam tayi mamakin Nafi dan bata taba tunanin zata iya ture maganar Ya Ashraf ba ganin yanda take girmama shi.

Little ta kalleta tace " Feena....!"
Nafi tai murmushi tace " Mu tafi kinji, wato matarsa bazata gyara musu muhallinsu ba shine ni zanje in gyara musu, sannan ba kunya su shiga suna farin ciki, sannan gobe ma aa kara kirana in gyara, to ba da ni ba."

Little ta jinjina kai alamar ta gamsu da zancen Nafi sai dai tana jiye mata b'acin ran Ashraf, iya kuluwa Nafi ta kulu wato ita da bai damu da ita ba shine yake neman sata gyara musu b'angaren su a lokacin da suke shirin fita, ta d'anyi kwafa kadan a ranta tace " ni d'azu kamar zan zauce jin wani abu zai sameshi ni kuma wato wannan ne sakayyar da zaimin.

Bata sake magana ba har suka ita gidan su Yusra sai dai kana kallanta kasan ranta a b'ace yake.

A bakin gate Al_Amin wanda ke zaune yana ganinsu ya saki wata fara'a tare da mikewa ya nufo su, sam Nafi bata kula ma da shi ba, har ya iso inda suke Little ta mai murmushi sannan suka kalli Nafi wanda sam hankalinta baya gunsu sai ma ci gaba da tafiya da takeyi.
Hannu Little tasa ta rikota wanda hakan ne yasa Nafi ta juyo ta kalleta, ganin Alamin a tsaye yasa ta mai kallan mamaki.
Rausayar da kai yai cikin salon soyayyarsa yace " I am disappionted Feena."
Nafi ta kakaro murmushi sannan tace " Sry wlh ban kula ba, sam hankalina na wani gurin."

Ya d'an shagwab'e kadan yace " in har damuwarki ba akan wani namiji bane na hakura in kuma har akan namiji ne ba ni ba banaji zan hakura."

Little ta saketa tai gaba ta barsu ganin Alamin ba kunya agabanta yake wannan sakalcin.
Nafi ta juya kai gefe sannan tace " just 4get, ya kaje gida jiya?"

Alamin ya kura mata idanunsa wanda ya kashesu kai kace a haka idanunsa suke, Jitai bazata iya kallansa ba hakan yasa tai kasa da kanta, ya kara matsowa sannan yace " Feena jiya na baki waya amma sam ko kunnata ma bakiyi ba, sannan yanzu kin wuceni ko kallona bakiyi ba, Feena please kar ki wahalar da zuciyar dake tsananin kaunarki."

Nafi ta d'ago jiki a sanyaye, ganin yanda har yanzu kallan nan yake mata yasa tad'an kalli gefe sannan tace " Ba haka bane, jiya bayan na shiga gida bacci nai da wuri, yau kuma sam ban ganka ba."

Alamin yai kasa dakai sannan yace " Ko dai....."
Katseshi tai da cewa " Alamin me yasa kake da yawan complain ne? Na fada ma uzuri na why not kai believe da abinda nacema meyas kake neman tursasani akan fadar abinda na shine ba?"

Tana kai nan ta juya ta nufi hanyar da zata sada ta da ciki, da sauri Alamin yasha gabanta tare da rike kunnuwansa biyu yace " Sry Feenah please!!"

Nafi ta kalleshi bata cemai komai ba sai kokarin canza hanya tai gaba da takeyi, bai san sanda ya riko hannunta ba, Nafi ta watsa mai wani mugun kallo sannan ta fizge hannunta tai gaba.

Kai ya dafe cikin tsananin tsoron abinda ya aikata, me zata d'aukeshi?

Nafi tana shiga ciki aka nuna mata d'akin da su Little suke nan ta shiga ta taddasu ana ta hira, duk yanda sukaso su jata da hira taki aminta a karshe ma kwanciya tai batasan sanda bacci yai gaba da ita ba.

Can cikin bacci taji Little na tashin ta, ta bud'e ido a hankali, Little ta kalleta tace " Feena ya zamuyi?"
Nafi ta mata kallan da me fa?
Little tace " Ran Yaya ya b'aci yana waje yana jiranki."

Idanu ta zaro gabanta ya yanke ya fad'i ta mike zaune da sauri tace " Da gaske?"
Little tace " wlh, yace ki fita yanzun nan, in kuwa kika bari ya shigo sai ranki ya b'aci."

Nafi ta mike tare da d'aukan mayafinta tai waje.
Little tace " inzo muje?"
Kai Nafi ta girgiza mata alamar a'a sannan tai gaba.

Nafi tana fita ta shiga neman motarsa dan itakam bata ganta ba, horn taji an mata wanda yasa ta juya ta kalli inda taji horn d'in, nan ta karasa gun jikinta duk ya mutu ga bacci ga tsoron me zai biyo baya, tana zuwa jikin motar ya zuge glass d'in motar sannan ya mata alama da hannu akan ta shiga.

Nafi ta bud'e motar ta shiga tare da rufe kofar.
Bai mata magana ba sai jan motar da yai, sai da sukai nisa ya juyo ya kalleta rai a b'ace yace " wato ni ban isa dake ba ko? Maganar saurayin ki ta fi tawa ko?"

Cikin mamaki ta kalleshi ta daure tace " ban gane ba."

Wani irin burki dayaja sai da numfashinta yai gaba na wucin gadi.
Nafi a tsorace ta kalleshi, ransa a b'ace yace " ban bada sallahu ki gyaramin part d'ina ba?"

Nafi ta kalleshi tace " ka fada amma gani nai ni meye nawa na shiga part din mai mata?"

Ashraf mamaki ya kamashi yaushe 'yar nan tai baki haka?
Yace " to ita kinsan ba 'yar wahala bace dan nace ki taimaka mata shine zaki tafi gidan saurayinki?"

Wani mugun kishi ne ya taso ma Nafi, ita ba 'yar wahala bace?"
Kallan mamaki take mai, yacigaba da cewa " sannan ke harkin isa in saki abu ki kama hanya kiyi tafiyar ki??"

Nafi batasan sanda ta saki wani murmushin takaici ba, ta goge kwaIlar data taho mata, tace " Yaya ba sai ka fadamin magana akan matarka ba, nafi kowa sanin ita ba 'yar wahaka bace, ni da ka d'aukoni daga riga mai shan madara da nono kullum, mai kiwon dabobbi nice 'yar wahala."

Jikinsa ne yai sanyi, a zahiri shi gidan saurayin ne bayasan taje ya kuma rasa dalilinsa na rashin san hakan, shi yasa yasata aiki bawai wulakantata yakesanyi ba.

Nafi ta share kwallarta sannan ta cigaba da cewa " Yaya ka maidani garinmu inda nake, na fi kowa sanin banda matsayi a gunka dama sauran mutanen gidan, Little ce kadai mai sona dama can ni haka Allah ya halliceni da bakin jini, ubana ma ba sona yake ba, uwata ta d'auki kanina ta tafi dashi ni da bataso ta barni a riga, ban taba samun wani wanda yake sona tsakani da Allah ba in har ka cire little, gwara ka..........

Jitai an jawota an rungume ta, kalamanta ne suka tsaya cak, bama su kadai ba duk wata gaba ta jikinta jitai ta daina aiki, shi kanshi sai daya rungumeta hankalinshi ya dawo jikinsa, me ya aikata? Sai dai ya kasa zare jikinsa..........



*THE INNOCENT TEAM*
[7/2, 10:06 PM] YAYA HAYAT: *ZUCIYA*
_Kowa da irin tasa_

© *AYUSHER MUHD*

37

Sun dade a haka kafin Ashraf ya d'agota daga jikinsa, kansa ya maida yana kallan gefen titi, a zahiri kunyar kallanta ma yakeyi, Nafi kam anyi dif kamar kazar data fad'a ruwa, kallansa kawai takeyi, Ashraf ya juyo ya kalleta ganin har yanzu bata dawo daidai ba yasa yai saurin cewa " Ke wai yarinyar nan yaushe kika yi baki haka? Sai magana kike ba tsayawa?"

Nafi ta bud'e baki zatai magana sai shakuwa, jikake heee'i, kanta tai saurin sawa a cinyoyinta tana kokarin maida shakuwar, Ashraf yai saurin tada mota suka fara tafiya, shiru ne ya biyo baya Nafi ta d'ago a hankali ta kalleshi, ganin sun wuce hanyar gida yasa tace " Yaya ina zamu?"

Kallanta yai sannan ya maida kansa titi tare da cewa " Hotel."
A tsorace ta kalleshi sannan tasa hannu a kafafunta ta matse jikinta, ya juyo ya kalleta dariya ta kusa zuwa mai, yace " lalai yarinyar nan me kike tunani?"
Kallansa tai sannan a hankali tace " bakomai."
A ransa yace " lalai makarantar nan ta b'ata yarinyarnan, bayaji sanda tazo garin nan tama san me ake nufi da aure amma yanzu aga zancen hotek har tana wani matse cinyoyi? Shi me zaiyi da yarinya karama ma kamar wannan? In ma iskanci zaiyi?"

Nafi kam aranta abubuwa da dama take ayanawa, ne zai mata a hotel d'in? Tunowa tai da sanda ya rungumeta da sauri ta girgiza kai alamar a'a, Ashraf kam kallanta kawai yake saura kad'a ya bigi wata mota, da sauri yaja burki sannan ya kalleta yace " badai tunani kikeyi ni? Kamar ni Ashraf zanyi miki wani abu ba? Banaji kinkai wannan matsayin ko da kuwa iskancin na keyi."

Nafi wanda kalamanta suka b'ata mata rai tace " nima ai bance wani abu zakamin ba, sannan ko wani abun ne ai banaji nakai wannan matsayin."
Kallan mamaki ya mata, sannan ya had'e fuska tamau yace " Da alama raini yafara tasiri a tsakanin mu."
Juya kai tai batace komai ba sai d'an kunkuni datai, a zuciye ya fizgi motar, lalai yarinyar nan shi take ma kunkuni? Sun isa Hotel din ya karasa gun parking, kallanta yai sannan yasa hannu ya fizgota sam baisan da karfi ya jawota ba wanda hakan yasa ta fad'a kirjinsa, a hankali ta d'ago cikin tsoro, ya kalleta yace " me kika ce d'azu?"
D'an karamin bakinta ta turo gaba tace " ni me nace?"
Yai wani murmushi yace " bakima san me kika ceba ko rainin hankali? Da alama ma zagina kikai."
Idanu ta zaro cikin mamaki ta d'aga jikinta daga nashi tace " ni? Yaushe? Taya za'ai in zageka koda kuwa naman jikina kake yanka?"
Ya kura mata ido sannan yace " inkinaso in yadda baki zagen ba to ki fad'amin a ina kikaji zancen za'a tareni a hanyar zuwa office."

Kallan sa tai cikin tsoro, ya matso da fuskarsa kusa da nata yace " what? Bazaki iya fad'a ba?"

Idanu ta kifta sannan ta had'iyi yawu, ya sa idanunsa cikin nata sannan yace " bazaki iya ba?"
Idanunta tai saurin maidawa kasa saboda wani abu dataji ya taho mata, komawa yai yazauna tare da d'aukan wayarsa yace " kijirani ina zuwa."
Yana kainan yai hanyar fita, batasan sanda tasa hannu ta riko rigarsa ba, yazo fita yaji an rikeshi, ya juyo ya kalleta sannan ya kalli rigarsa inda ta rike.

Nafi cikin tsoro tace " tsoro nakeyi Yaya."
Idanunsa ya kankance yana kallanta, ta cigaba " Tsoro nake kar na zama silar jawo gaba ko fad'a a tsakanin ku."
Ashraf yai karamai ajiyar zuciya sannan yace " Nafisa me kika sani? Me kika sani game dani da 'yan uwana? Mutane sun d'auka ganin fara'a a fuskar mutane shi yake nuna suna cikin farinciki sai dai abin sam ba haka yake ba, kowa da kike gani shi kadai yasan wace rayuwa yakeyi a cikin zuciyarsa."

Nafi tai shiru kanta na kasa bata kuma sakeshi ba, Ashraf ya sa hannu akan hab'arta ya d'agota yace " Asim ne?"

Kai ta d'aga mai tare da maida kanta kasa, Ashraf yace " sakini inje in dawo lokaci na tafiya."

A hankali ta saki rigarsa, ya fita.
Kallo ta bishi dashi jikinta duk ya gama sanyi.
Shikam Ashraf sam baiyi mamaki ba dan dama jikinsa ya bashi hakan, ya sani mutane dayawa ba sanshi suke ba a gidan amma kowa na kokarin b'oyewa banda Asim.
Yana shiga ya bada takardun dayazo badawa sannan ya fito.

Nafi kam abin duniya ya dameta, Ashraf ya bud'e ya shiga, ganin yanda take kallansa yasa ya d'aga mata gira yace " ya akai kuma?"

Nafi ta girgiza kai alamar ba komai sannan ya tada mota sukai gidan lawyer d'in babansa, nan ya ajiye wannan motar ya d'au tasa ta da sannan sukai gida.
B'angarensa suka nufa, yana gaba tana binsa a baya, sunje wuce wa ta b'angaren su Asim sai gashi.

Ashraf ya saki wani murmushin rainin hankali sannan ya cigaba da tafiya, ba wanda yama juna magana har Asim ya gifta Ashraf kad'an.
Yaji Ashraf yace " ASIM"
Ba Asim ba hatta Nafi wanda Asim d'in ke saitin ta ta tsorata da yanda Ashraf ya kirashi, Asim kam tsoro ne karara a fuskarsa, Ashraf ya tako a hankali yazo kusa dashi sannan ya sa hannu ya dafashi yace " ka tab'aji inda kura ta nemi kama zaki?"
Asim yamai kallan mamaki sai dai bai amsa ba, Ashraf yai murmushi sannan yace " Ita kanta kurar da take tsoron zaki kaga kuwa ta ina ta isa ta kama sarkin dabobbi?"
Ya kara matsowa kusa dashi sosai yasa bakinsa a saitin kunnensa yace " In har kurar tana neman halaka sarkinta to lalai sai tayi amfani da kwakwakwarta." Ya fad'a tare da nuna tasa kwakwalwar.
Sannan ya cigaba " in har batai amfani da nan ba to lalai ita zata fad'a cikin trap d'in datai na kama sarkinta."
Yana kai nan yasa hannu ya bubugamai kafad'a sannan yai gaba.

Nafi kam a tsorace tabi bayan Ashraf.
Shikam Asim anan suka barshi sai dayai kusan minti biyar a tsaye kamar abu kara motsi kafin ya juyo da niyyar kallan Ashraf sai dai sam baya gun.

Sun isa b'angaren sa, Ashraf ya kalli Nafi yace " D'akina nakeso ki gyaramin."
Ta kalli falon wanda duk yayi kaca kaca ko sanda yake shi kadai baya taba yanda falonsa yai haka bare yanzu.
Ta kalleshi tace " nifa d'akinka kawai zan gyara."
Yace "Falon fa?"
Tace " Wannan kuma matarka sai

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login