Showing 126001 words to 129000 words out of 152911 words
garin ranar da kuka tafi aka kawo kayan aiki,zanen gidan ma sai da na zaba tace ana gamawa zata siya min mota Kuma ta bani jari million biyu,Cele tace taci ubanta baza ta karasa ba duk ta kwashe mana ladan komai sai dai naji tayi wlh bata Isa ba sai dai na karasa maka gidan nan Kuma motar ni zan siya maka na kaiku Makkah da su Umma haka naji har su Bilkisu ta canja musu kayan daki,wai shi Nawwar komai bata yake ne Yar iskar yarinyar nan uban mene a local government dinta Wanda mu Babu sai wadaka take yi,Abba yace ai Rabi har local government ce da ita a gidan ubanwa zata mallaki local government,Cele a ranta tace wlh na gane me yasa Nawwar yake mata komai Yar bariki ce Rabi sun gama sanin kan tsiya,Nima zan dage bari na Saba na samu Ahsan na Maida shi cikakken Sallamammen Sullutu,Cele bata San shi Nawwar dama can yana da saki hannunsa a bude yake wasu banza ma taimaka musu yake bare iyayen Rabi,Su Star duk shine ya musu komai.
Abba Bai San mene local government ba,yana ta murna yana ji a Kan farin cikinsa har kokawa ake yi, na gane gaskiya mutum kawai yace Allah ya bashi masu Albarka na gari ko mace ko Namiji,Shiga muka yi ciki Uwa tana zaune tana gyara tabarmarta data ganmu sai murna nace lallai su Uwa an saduda an San darajar Kai,to kin San darajar kanki mana tunda kema macece bazan ce kin San darajar mata ba tunda harda ke kina cikin matan,mace bata son a haifo mata kinji kunya Uwa kin dinga cin arzikin mu kenan,Har da jefar da Rabi to gashi tana muku gini tana saki cikin suturar da ku kuka kasa kuka jefar da ita,Cele ta dafa kirjinta tace Wai Uwa ni Zaki ce Zaki jefar an haife ni sai Kaka aka bawa ni ya rikeni rukon da ko Wanda ya haife ni bazai min ba,Uwa wallahi gori sai in bamu hadu ba,Uwa tayi mukus tace Dan Allah kuyi hakuri ku yafe mana gashi yanzu Rabi har abinci tasa an kawo mana ba abinda bata kawo ba,Cele tace a'a duk dai Rabi muna tare Amma bata fada min ba uhmm to nima zanyi nawa bari komai yayi settling,Ahsan ya gaida su,suka amsa da fara'a suna jansa a jiki,mun Dade a gidan sannan nace zamu koma gidan Umma tayi mana girki Abba da Uwa har bakin mota suka rako mu suna ta kallo,Ina fadawa Ahsan Rabi ce du tayi ni banyi komai ba ta kwashe ladan,dariya yayi yace karki damu zamuyi musu namu na daban ai abin alkhairi baya karewa a duniya ni San me za muyi sai lokacin Cele hankalinta ya kwanta,Yace ga Kaka ma,Cele tace wannan kafata kafarsa rayuwa sai da Kaka,bazan iya barin Kaka na tafi wata Uwa duniya ba,Ahsan yace duk yanda kike so,amma fa bazan zauna a kasar nan ba sai dai kasar mu,na yarda dai zamu na zuwa hutu mu Dade amma ni bazan siya Miki gida a Nan arewa ba bai min ba can garin su Miracle yafi min weather tayi ga ba mutane da yawa in munzo zamu zauna can,Cele tace dole dai ka siyawa kaka gida a Nan Kaduna ko ka rushe nasa ka gina masa sabo Idan yana so yayi aure ban sani ba kar na shiga hakkinsa,Ahsan dariya yayi yace ya samu me dafa masa me ma kuke cewa abinda tsoho ke sha?nace kunu,yace na'am me dafa masa kunu,nace damawa ake cewa ba dafawa ba.
Baso ne a zaune ya hakimce sanye cikin Shadda milk yayi kyau matuka hancin nan dodar ka rantse bai taba Shaye Shaye ba, Omaira ce ta shigo dauke da Sallama a bakinta Baso ya kalleta da mamaki dama itace shi kyawunta ya masa yawa,Harara ya balla mata ya mata Kiran kare cwa cwa cwa da Dan bakinsa,Omaira ta bata rai ta zauna itama tace Cwa cwa cwa ta Kara da fito fiii fiit...,Baso ya kalleta da sauri tare da furta ke yane? tace Yane Kuwa,bana son yawaa tashi na ganki kinyi ko baki min ba,Omaira ta kalle shi duk kyawunta ya Rainata mata wayo ta mike a fusace ta juya tace San kowa kin Wanda ya rasa ka kiyayeni nima Yar kwaya ce,Baso yace Allah? Wacce kike sha a ciki? ai ni irinki nake nema dama yana wani karkada kafafu kamar Dan sarki dama haka yake shi gadarar masifa kamar Dan wani,magana ma Dalla Dalla yake yinta da raini yana bin mutum da wani kallon baka Isa ba sabo da bashi da kunya shi Shaye Shaye ya gama kangarar da shi,Omaira wayarta taci gaba da latsawa tana chating da saurayinta na WhatsApp,Baso ma wayarsa ya jawo ya amsa Kira sannan yaci gaba da latsawa,sunfi minti talatin a haka,Wise ce ta shigo tace ah Bason Salma dare dare wlh, amsawa Wise yayi yace sai barawo ta gidana shike nan wai sun gaisa ta wuce,Omaira ta dinga mamaki a haka gaisuwa ce,mikewa yayi ya fito da kudi sababbi dubu ashirin ya zubewa Omaira a cinyarta yace Kya sha ko Ermo ce tunda Yar kwaya ce,Omaira tace ni nace ka bani kudink.....kafin ta karasa ma yayi nisa ya fice,dama shi suke Jira zasu tafi,Nawwar yace yaya to? Baso yace yayi dai dai take Dani babban Kai ce nafi son wacce zata yi maganina,Nawwar ya kama dariya ba a gane Ina Baso ya nufa Sam,yace kyau ya masa yawa yanzu yace yafi son wacce zata gara shi,Yace Anya kuwa Baso ya Daina Shan kwayar nan ko dai har yanzu bata sake shi bane.
Masu sharhi ku dinga sharhi na gode aci gaba tam🤣
AsmaBaffa
[8/30, 10:20 PM] AsmaBaffa: 🌼'YAR AIKIN KARUWAI 2 🌼
MATAFIYA
BOOK 2
96-100
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA GA
ZAINAB USMAN
*MISKI 3in1 Alfirdaus*🌹 Albishirinku💃 original miski daga *Egypt* miskin da koda yaushe Kuna yabawa dashi yana dauke 1.*Musk oil* ana shafawa agaba bayan gama al'ada inda hali za'a iya ringa sawa Koda yaushe yana maganin infection yana gyara gaban mace sosai 🙈ko yaushe gurin yakasance cikin kamshi 😇bayaga haka sunnah ne amfani da miski
2.*Musk cream* Ana shafawa ajiki gaba daya musamman wajan cinyoyi yana sa jikin mace koyaushe yakasance cikin kamshi kuma yana gyara fata, yasa tayi laushi
3.*Turaren tsarki* wannan turaren karshe ne 🔥 🔥 ba lallai se bayan gama period ba koda yaushe zaki iya rinka tsarki dashi yana gyara gurinnan🙈 sosai, kuma ana shafawa a hammata yana kawar da da wari karku bari abaku labari 🙍♀️👱♀️
Masu bukata ku ne wannan number
09065959708
Page naki ne
AIDA MAMAN TASNIM
Bayan su Baso sun tafi Omaira ta shigo tace Aunty kinga abinda Omar ya bani,karba nayi nace inye yarinya anyi goshi sai ki ajiye abinki,ajiye min to Tarawa zanyi na siyawa Abba waya Me tsada nace to Allah ya taimaka,dariya tayi tana furta tunda Umma kin siya mata sai na siyawa Abba nace to kin kyauta ai,nace Uwa Kuma ko rakani Kashi ai Kya siya mata na tsokani Omaira,Omaira tace Allah ya kiyaye ko ficikata ai ni da Uwa haihata haihata ba irin zagin da bata yiwa Umma ba a gabanmu a'a wlh Abba ma dai Dan Mahaifi ne muna Kuma da ilimi dai dai gwargwado if not ai da Shima baza mu kula shi ba,Abba ko sandal din Makaranta bai taba siya mu da shi ba,Nace to ba sai kuyi hakuri ba yanzu ni da aka jefar dani fa Kuma yasan an jefar dani kuyi hakuri rayuwa ce ba gashi ya wuce ba sai labari yanzu ai mu zamu nemi Lada a wajensu ko a Daina tashin zance Raina baci yake Idan na tuna,Omaira tace Chansa Aunty hakuri ai kamata yayi sunanki Hakuri,Nace ke kika sani dai jibi zamu koma gidana kuje da Hamra da me aiki kuyi gyara duk a gyare yake ayi masa na musamman,Omaira tace to zamuje sai mu tafi da wasu kayanki ko? Nace ae haka za ayi.
Mami ce ta Kira Auta da Salma part din Baffa yana zaune tace da Baffa gasu nan sun Daina zuwa school wajen kwana biyar kenan na gaji da fadan Idan basa son karatun su fada,wajen aikin ma Auta baya zuwa Office,Auta yace Kai Mami,karya nayi ai yace ni ban ce ba,Salma ce tace Malaman ne suke meeting zasu yi na sati daya shine suka bada hutu ta Kalli Auta suka hada Ido yace ae ai kuwa meeting suke shiga kullum sabo da yanda zasu inganta Makarantar,shugaban Makarantar yace cin hanci da rashawa yana gurbata masa dalibai dole ayi gyara,Baffa Yana ji yayi dariya kawai,Mami tace Auta to wannan karyar taku bata shiga ba ku canja wata,Salma tace da gaske Mami Kuma ma ba wani cikakkiyar lafiya ce Dani ba malaria har yanzu bata sake ni ba ko? ta furta ta Kalli Auta,Auta yace hakane Kam jiya ma da zazzabi ta yini,Mami ta harare su tace Kai Dalla ku rufe mana baki,Baffa ne ya dakatar da Mami yace dakata ki bisu a hankali Yara ne fa,Auta yace ei yarane mu,Baffa yace ku koma school kafin ku koma gidanku Karka bari na ganku a gida bakwa zuwa,Auta yace to zamu je ai gobe Monday Baffa kayi mata ya jiki Zazzabi tayi sosai,Baffa yace Allah ya sawwake,Salma tace Ameen harda labgabewa,Mami murmushi tayi kawai tace Allah ya shirye ku,Auta yace Ameen dai Mami ya rike Hannun Mami shi yasa nake sonki kece ta karfen,hannunta ta fisge tace dan Allah sakeni ni fitsararre,Salma dariya tayi ta juya ta fice tana fitowa tace Baffa ya gane shi dake Namiji ne,Auta ne ya fito yace My producer, dariya Salma tayi tace ta ya na zama producer? Yace Yara fa zamuyi producing to gaki da industry guda,Salma tace sarki ni me Industry ai Kaci uban Industry din duk ma'aikatan ciki ka tarwatsa su,Rada ta masa tace jiya round 2 kayi fa na sha wahala daurewa nayi saura kadan na gudu,hannu yasa ya sarkafo ta wuyanta ta baya suna tafiya a haka, Abdullah na yana ta uban kuka na rasa yanda zanyi da shi,Auta yace ga mutuniyar can ana fama suka yi dariya,Auta yace Allah sarki bari mu Kai mata dauki suka shugo,a tsaye suka sameni Ina ta aikin jijjiga shi yaki shuru,nace wannan yaro nayi zuciya na ajiye a saman bed nace sai kayi tayi tun safe kake kuka an rasa me aka maka haba,jiya duk bamuyi bacci ba Kai Kaki hutawa ka hana wani sakewa haba Abdullah don't make me loose,Sake daukan abina nayi nace taho kaji na tuna wahalata,Auta ne yace ko dai bashi da lafiya? Nace kaga magungunansa ni tunda Cele ta masa wanka na rasa Kansa wlh,Auta yace ko dai rauni ta masa ba a sani ba,bari a kaishi wajen likitan Yara,dakko shi mu tafi,Salma ta dauke shi suka tafi da Auta da Abdullah jariri yana ta tsaga kuka.
Aka kaishi wajen likitan ya duba shi sosai yace ai rauni aka masa a kirji,kashin hakarkarinsa ne ya goce,gyara aka masa ya bada magunguna yace ni zan sha ba yaron ba,kafin su zo gida yaro tuni yayi bacci suka dawo Auta yace Cele tayi aika aika ke ya za ayi ki bata shi ta wani yiwa jariri wanka me ta iya ita Idan ba masifa ba,Nace wlh na shiga wanka sai gani nayi ta masa wanka ta shirya shi ni bana bata ta masa wanka,Auta yace to kashin kirji ta goce masa,nace Kai bala'i karfi ta sa masa,Auta yace ki kula to,yayiwa Salma rada yace zan fita Madam sai dare zan dawo,Salma da rada itama tace abincin fa? Karki yi zan siyo mana kayan Dadi Wanda zamu samu Madara ingantacciya a jikinmu,Uhm tace a dawo lafiya Karka dade zan kulle maka kofa indai ka wuce 9pm,Yace an gama my Queen,My princess,my Paradise,har da wani rusunawa a gaban Salma kamar yana gaban Gwamna Allah ya tsare min ke,Allah ya ja zamaninki shugabar mata, Allah ya Kara Miki lafiya da yawan rai,macen kwarai sa maza ladabin dole Me hamshakiyar Industry a sarrafa man ja a sarrafa man gyara,ga Madara me inganci ga ...Salma ce ta ture shi tana dariya tace please jeka wai dan kar aji sirrin su, nace Kai Auta ko kunyata,ficewa yayi ko a jikinsa.
Salma na kalla nace Salma me Industry Yan iska,Salma ta fuske tace Dan Allah karki biyewa Auta kin San halinsa da wasa kinga Abdullah sai baccinsa yake ta canja zancen,Nace ke yar bariki ni Zaki wa wayo,dariya tayi tace Aunty Kenan,na jawo zumata ta tsumi na fara sha,Salma tace kaga manya dan San min, nace bazan bayarba ku nemi taku a sirri,please Aunty nace to badan halinki ba sabo da Auta na bata guda a Yar roba,ta karbe tace na gode, Mami ce ta shugo Salma da sauri ta cillata kasan gado tayi wani sakato kamar doluwa,Mami kuwa Abdullah ta dauka ta goya shi ta fice,sannan Salma ta dakko tata tayi sauri ta shanye harda girgijewa da ruwa,na kalleta Ina dariya nace irinku Salma sai kuyi kisa baza a gane ba Kun iya funafunci,tace to sai ka zauna kana talla sai kace ciwon Nononki Mami zo ki kalla kin gani kuzo ku gani,Auta ka gani,Dariya nayi nace jibi I yanzu dai ni Kam Ina gidana Antena sai baza ayi ba,Salma tace ku dai kuna son Antenar nan Abar da ba Dadi ba Kun damu mutane,Nayi dariya nace sai nan gaba Zaki bayani,Wise ce ta shugo ta ta tsinci zancen tace ba a zagin Antena a gaban mu mun San darajarta,Salma ta kama dariya,Wise ta hau iskanci kala tana karkada duwawu tace inama Star zasu zo kiji kirarin Antena,muna ta iya shege Salma tana jin mu,Auta ne daga fita har ya Kira ta daga tana wani kashe murya ana karkashe Ido kamar tana gabansa muka bita da kallo,kamar zata narke tana wani shagwaba tace Baby kaje ne? Auta wai Ina bakin gate na fita da mota har nayi missing naki,dariya ta kama Salma daga fita gate har an Kira waya,sai lokacin yaci gaba da driving yace karki kashe raka ni a haka tace to muje ka tuka mu a hankali,wai a haka ta wayar take raka shi hhhh muna dariya wannan iskanci na su Salma,Yar school din da Salma suke zuwa ta Iya yaren Igbo tsinta tsinta sabo da cudanyya da su,su Auta kuwa dukkansu suna jin yaren har su Baffa Idan suka juya sai ka rantse sune ma Igbo din,Idan zata fadi wata maganar sai ta jefo da Igbo,nace Dan Allah ba Dadi yaren nan wlh bana son ma na iya Ina jin Nawwar yana yinsa wani haushi,Su Wise suna jin yaren sabo da sun Dade a garin nice kawai ban ji bana so Kuma na iya amma sai ji nake yi.
Cele kuwa Sai dare Ahsan yace ta taso su tafi hotel,ta fara fushi zata masa gardama Umma ta kirata bedroom tace mene kike fushi? tace to Mami a gidan ma na dawo bazai kwana shi Daya ba kafin mu tare a gidanmu kina ji wai garin su Miracle zamu koma shi baya son nan,to shine me wallahi baki da hankali baki San ma auren ba ai Yanzu sai yanda aka yi dake kuma dole kibi abinda yake so duk inda yake son zama dole ki bishi nufinki shi zai Miki biyayya baki da hankali baki San maza ba musamman Larabawa taurin Kai ne da su wlh ba a canja musu ra'ayi ki godewa Allah ma da yace zai siya Miki gida a Nan Zaku na zuwa a kan lokaci,shi yasa Rabi ta fiki hankali sai abinda mijinta yake so,Idan Zaki nutsu ma ki nutsu kije ki bi Mijinki,Zata yi magana Umma tace zan tsinka Miki Mari wlh tafi ki bani waje shashasha Allah ya Miki gata kina iskanci bar gidan nan ko inci ubanki,Cele tasan Umma ma akwai fada ta juya ta fito tayi murmushi tace tashi mu tafi,Ahsan yaji Dadi hannu ta rike masa ta jawo shi tace muje Idan na gama rakaka wajen dangi Allah bazan sake zuwa gidan wasu ba muyi ta kwana tare tunda abin haka ne Kowa yace sai an bi miji,Ahsan bai San Cele zuciya tayi ba ya mata kiss a goshi tare da rungumeta a gaban su Rahma suka ce Uncle Ahsan sai gobe,Cele tace wai Uncle sai da safen ku suka tafi sai Hotel dinsu driver ya sauke su suka shiga,ya birge Cele tace a takaice dai na zama yar Hotel kowa Yana aurensa a gidan Miji ni kuwa Ina hotel duk Wanda ya zargeni yayi tunanin karuwa ce ni Allah ya Isa nasan Hausawa da sa Ido da zargin banza,mutum baida tabbas yana ganin Abu ya masa mummunan zato duk Wanda ya zargeni Allah ya Isa bazan yafe ba,sai Kallona sukeyi mutane sun zaci bakon balarabe na samu me shigo da kaya Nigeria da ace a garin su Miracle ne wa zai kalleka ma,Ahsan ya shiga wanka ya bar Cele tana ta masifa,fitowa yayi ya ja hannunta suka shige toilet din tare, towel din da ta daura tana Jira ya fito a wanka ta shiga ita shi ya janye
Cele ta matsa jikinsa da sauri tace haka kawai ka kalleni ta fisge nasa towel din suna dariya tace nayi zuciya Nima na zama Rabi sarkin zuciya tunda dai Babu me kawo min agaji sai dai ace ka tafi wajen Miji baka da uzuri sai na Antena to ai bazan mutu ba ayi ta cin uban local government zan daure har na Saba,yanzu na Daina musu kawai na hakura tunda abin hakane,Ahsan in tana surutunta wani ba fahimta yake ba sai dai ya tsinci wani dariya yake,Cele ta zaga ta bayansa kamar zata hau bishiya tace haka naga Salma tana yi ta dafa kafadun Ahsan ta dora kafa a kaurinsa ta kama zata hau kamar wani Katanga,ta sulmiye ta dawo kasa ta dire ta sake gwadawa tana