Showing 3001 words to 6000 words out of 152911 words

Chapter 2 - Yar Aikin Karuwai 2

22 Oct 2024

4704

hotel,nace shine wlh Ina mamaki da murna na dirgo daga saman bed Muka rungume juna sosai Yana dariya yace amma lokacin gaskiya matata Yar kauyis ce,dariya nayi nace ba wani yace kinyi wani daurin dankwali kin zamge kai me kunya bakya iya kallona fa,nace ai daga nan sai bariki,yanzu ai matar tawa ba kunya gareta ba,nace duk ta gudu ai gashi ka sake lalatani,gashina yake shafawa yace Yar amana ta ya daukeni yace zauna muyi kallo,baki na turo Ina shagwaba Ina Masa magana da Ido dariya yayi yace na gane ke Yar nan zalamarki yanzu tayi yawa,Murmushi nayi Ina sake rungume shi na tura shi saman bed yana min wani kallo me rudani,Hannu nasa tare da cire Yar guntuwar rigar da na saka daga ni sai pant sai bra,Muka Fara zuba kauna yau nice ke Jan ragamar komai ko da Muka tsunduma cikin harka Ina samansa Ina twerking yau sai da na gogewa Nawwar hadda,yaji Dadi fiye da kullum sai lallabani yake Yana nan da ni.

Mairo tun a ranar da Suka Isa kasa me tsarki wacce ta musu Hanya ta kaisu gidanta Wanda su wajen goma ne a gidan gidan nasu duk kazanta ko Ina ba a gyarawa ga Makkah suna da kuda,a cikin gidan duk Inda ka bi sai kudaje buuuu buuuu suna tashi ba kyan gani,Mairo tace kuda haka sai kace Muna gaban me balangun da bai Fara gashi ba,ku Kuwa ku samawa kanku lafiya ku dinga gyarawa ji yanda Muka wuce hadaddun wurare amma sai a nan Muka yada zango ,Agent din ta bata rai tace Zaki ma Yi bayani sai nan gaba tukun gaki da ciki Wai watansa nawa ne ma? Mairo tace wata bakwai kenan,gashi nan fa ya girma Amma kamar tumbi Allah ya taimakeki ,sauran takarin ne Suka Zo dukkansu dattijai dasu suka dakumi Sadiya Suka hau Yi Mata kiss a kumatu Salamu Alayki muaaah muahhh,kowacce haka Suka dakumi Mairo itama Suka rungumeta suna marhababik marhababik muah muuaaah....suna magana suna jefo larabci,Mairo tace zanyi fitsari,muje Kinga wagga hammam can wai toilet,ta fara takawa a hankali agent Hajiya Marwa tana furta shuwayya shuwayya....Mairo dai ta shiga toilet to ba Dan laifi an wanke.

Bayan sun huta na sati daya nan kuma Hajiya Marwa tace to akwai Sana'a iri iri ba Zama a nan Kuna gani kullum sai mun fita a garin nan neman kudi,dakin Marwa inda aka sauke su kaya ne zukumi zukumi irin na Yar hajja duk gumama iri iri ba masaka tsinke,a cikin gumamar Wanda mu anan akafi sani da gwanjo amma na larabawa ciki Suka zabi suturun sakawa,ita Mairo kudin Sana'ar ma aro aka Bata tsabar talauci, ta fara yin fura da nono amma da Yogourt suke amfani suna kaiwa gidajen masu Ibada Wanda Suka Zo Ibada Saudiyya ko dakin ka'aba ba a kaisu ba sabo da gudun kame dole sai lokacin da aikin Hajji yazo sannan kowa Yana da yanci lokacin zasu iya su sauke farali har Umrah amma duk da Haka Hajiya Marwa tace zata kaisu suyi Umrah kafin lokacin aikin hajji.

Su kuwa Wanda Suka je ta kamfani maza masu ilimi sunfi yawa su already dama suna da aikin da zasu yi,wasu ana kaisu kamfanin wani balaraben suna aiki wasu kuma gidan gonar wani,shima idan aka Kai mutum Kawai suna wajen aiki sai sun dade suke samu su saci hanya su fito a haka suke samu suyi aikin hajji kafin su samu yancin fita,Yan unguwar su Sadiya da aka musu hanyar aiki Suka tafi ta kamfani Suma suna da yawa ciki akwai Nazifi ,Shamsu,Isa duk makwaftan Sadiya ne Suma Babar su Sadiya ta musu hanyar kamfanin,Nazifi shi gidan gona aka kaishi inda aikinsu tsike Apple su shiryata kwali kwali,Shamsu kuwa shi bangaren kula da shanu aka kaishi sai Isa Wanda wani kamfani aka kaishi Wanda suke sarrafa Alkama a maidata flour suna ta aikinsu hankali kwance su Kam sun bi ta tsari sai dai wasu aikin nasu da wahala Kuma ga kudin kadan ake bar musu suna biyan Agent kudi Wanda a tafiya 1.5million aka ce zasu bada amma suna zuwa garin Suka ce 5million zasu biya dole,bangaren Mairo ma haka aka maida kudin sabo da zalunci irin na Agent da suke yi Babu tausayi ba Imani kana aiki amma kullum a biyan kudi kake.

Dake a can ne ba wahala washe gari aka daura auren Mami da Mahmood Balaraben Yemen Wanda ke da shagon Jallabiyya a Madina ana daurawa Amarya ta tare a gidan balarabe shi ya dakko abarsa a mota,Dake su suna da gata a kasar har motoci suke siya,gasu su dake larabawa ne business ya Kai wasu Saudiyya, wasu Kuma suna wasu kasashen sakamakon gomnatin kasashen su Ambassador dake me hankali ne yasan me yake sai yaje kasar da yake jakadanci ya samowa Yan kasarsa aiki na kirki me kyau a bashi vacancy,duk me son aiki sai yaje a bashi form a kasarsa ya cike da takardun da ake bukata sai a zabo su a kaisu wasu kasashen daban daban haka har Yan Bangladesh haka Ambassadors dinsu keyi amma Banda na kasar mu Nigeria Kai ka Isa ya Nemo muku aiki tunaninsa kullum ya danne kudaden talakawa ga inda zai amfanar da Yan kasarsa amma ya kasa, sai dai a kyale talakawa suna shiga kasashe ta gurbatacciyar Hanya Wanda ba a San inda Suka nufa ba suna zuwa suna bata sunan kasar a banza Kuma ga inda aikin jakada yake,kasashen kirki gasu nan suna samowa Yan kasarsu job opportunities daban daban aiki me kyau bana wulankaci ba a wasu kasashen suna tura yan kasarsu marasa aikin yi.

Mahmood dama burinsa ya auri baka duk da cewa Mami Fara ce amma ba irin nasu bane,dama shi baya son baka ko da Yar Africa ce to ace tana da haske shi ta masa, gida irin na larabawa komai yaji a gidan ba abinda babu a Hawa na hudu Mami take sauran duk gidajen larabawa ne Dake dogon building ne sosai, Mami bata Jin larabci sai turanci,shi Kuma Yana Jin turanci, Alwala Suka yi tare da gabatar da Nafeela sukayi adduoi duk da shima balarabe ne Kawai amma baida wani ilimin addini sosai,Kayan ci da sha ya kawo irin nasu na larabawa,Mami Iya gasashen Naman ta iya ci da Madara,Yana bata a baki yana Mika Mata wata tare da furta laban Hajji,Mami tace ta koshi sannan ya kyaleta,wanka ta shiga,daya bedroom din ya koma yayi wankansa a can sai ganinsa tayi ya dawo sanye cikin kayan bacci masu kyau Yana kamshi dama ga larabawa gwanayen turare gashinsa yaji gyara sai sheki yake.

Kallon Mami Kawai yake duk idonsa yayi ja har wani ruwa idon ke fitarwa sai da Mami ta tsorata,daure take da guntun towel ya kasa jira ta shirya,towel din ya fisge tare da yin jifa da shi, ya dauki Mami ya dorata saman bed,bakinta ya laluba ya fara kissing dinta a haukace Yana gurnani har wani shidewa yake,yanda yake bin Mami da tsotsar Boobs dinta kamar zai tsinke Mata su azaba Kawai take ji,shi kuwa ba ji ba gani,Har hakuri take bashi tana cewa please take it easy on me amma Ina sai gurnani yake Kamar zaki sai uban larabci yake ya manta Bata ji ashe masifa yake Mata Wai ya biya Sadakinsa tunda ya saka Mami a sako ya shigeta duk da tana da niima sai da taji zafi kasancewar ta dade rabonta da abin tunda Baffa ya dade bai kwanciya da ita,shi Kuma wannan balaraben Kamar mahaukaci haka yake abu,ba tsayawa Kawai aiki yake,tun Mami tana daurewa har ta gaza su dama yawancinsu Basu san su tsaya ba harijai ne,ya dade Yana Abu Daya sai larabci Kawai ke tashi a dakin Wai yabonta yake,Mami dai ta gaji ta fashe da kuka tana so ta gudu amma ba dama,tuni ta daina turanci shima ya daina sai larabcin dadi ita kuma ta koma Neman agaji da hausarta tana wayyo zai kashe ni,na shiga uku,ga mazaunan Mami sai Mari suke Sha duk sun Dade sunyi jajir, har da Kiran Nawwar ka ceceni 'ya'yana amma Ina ba kowa,sai da yaji wa Mami rauni sannan bayan ya kawo ya lura amma ko a jikinsa Kawai Alhmdllh yake furtawa yana Jin dadinsa,Mami tana ta kuka sai Kuma yazo ya lallasheta Yana labbata har ta gasa jikinta ya bata magunguna ta Sha ta kwanta sai baccin wahala.

Cikin dare Malam Balarabe sai ya sake dawowa Yana lalubar Mami,Mami da Hausa tace baza ta yarda ba Suka Fara kokawa sai masifa yake da larabci Wai ya biya sadaki,Mami dai taki yarda suna kokawa Kawai ya kifa Mata Mari ta dafe kumatu ya turata ta kwanta har tana bige kanta da karfen gado nan azaba ta sha babu romancing na kirki sai azaba nonuwan Mami sunyi jajir sabo da azaba ga mazaune sunyi ja Suma suna ta Shan mari,haka kamar ran Mami zai fita sabo da yanda yake binta ba sauki duk da ta Saba tayi haihuwa nawa amma wannan balaraben na daban ne Sam Kamar marar Kai haka yake,Yana aiki Mami tace wallahi sai ka sake ni bazan iya ba na Saba da tsohon mijina 30mnt ya kawo,shi yasa idan mace ta Saba da Namiji daya to da salonsa zata Saba idan harijine haka zata Saba,idan ma bai dadewa haka zata Saba,to da guda dayanta ta Saba,tace sai da Nawwar ya fada min wai yaran Zamanin nan Ina suke sanin Kan ta duniya ne gashi ya sani ya fada min naki ji,yayin da Mami take Shan azaba mu Kuwa Muna can Muna Shirin bikin Santana da Jamcy.

Cele suna mota suna tafiya ruwa iska rana duk ta Kare a kansu duk sun fita a hayaccin Yan kwanakin duk sunyi zuru zuru sun rame, Amma a haka har nishadi suke yi suna wake wake da tafi sun kusa shiga Sudan suna bi ta Sahara duk sun Saba da juna duk da cewa wasu matan a ciki maza suna kawo musu hari,Samira ma Saura kadan Mustapha da Awwalu suyi Mata fyade Allah ya kiyaye Agent tace wallahi za a barsu a hanya shine suka samu lafiya Sabo da wasu ma fyade ake musu idan mazan ciki sunfi matan yawa.
Suna Shiga Sudan aka musu check in suka wuce kowa ka gani sai Murna tunaninsu ruwa ta sha,sai da Suka sauka a wata state ta Sudan sannan Agent tace to idan da me kudi sai ku Kama Sana'a har Allah ya kawo lokacin shigar mu Makkah,Cele tace na'am me Kika ce? Kinjini ai ku fito mu tafi Suka firfito da kayansu ta nunawa maza gidan da zasu zauna wani watsatsen gida shima a State din a Kauye suke sabo da wane mutum ba a shigar musu city haka Kawai,gidan maza dakin Dattijai daban dakin matasa daban,haka gidan da Suka je na wata ce wacce itace ogar Agent din da ta taho da su a gidanta aka sauki mata duk a daki daya aka gwamitse su,ga wasu matan da yawan gaske duk an kawo su sunfi wata a gidan suna ta Neman kudi a garin,Cele Allah yasa an iya Neman kudi,kwana uku suna fita suna ganin garin da hausawanmu da yawan gaske sai ta Fara danwaken Siyarwa ta fito da shi sai a warwashe a siye tas ga tsadar tsiya amma haka ake siyewa,kullum sai ta je ta gano lafiyar kaka tace ya dinga Fitowa inda ta kawo danwaken suna siyarwa tare,a cooler take Fitowa da shi dake komai sai da ta siyo dake Africa ne suna da abubuwa da yawa Wanda muma Muna da shi sai dai nasu Dake yankin Sahara ne Kai musu akeyi mutanenmu da Neman kudi, Su Samira sai mamakin kazar kazar din Cele suke Kamar ta San gari Sam a gidan ba a ganinta har wata state din take zuwa sabo da masifar neman kudi,Agent din gaba daya dariya Cele take basu daga zuwa gari sabo da Yar ta kife ce Kamar Yar kasar haka take abu, Hajiya Marwa Agent taga ta dawo da waken suya Kuma da kasko da kayan suyar awara komai dai ta hado,tace Allah de ya biya irinku muke so wallahi Yan ta kife ke ko hutawar ma bakiyi ba daga zuwa kwana goma ke tuni kinyi nisa a sana'a, kuma kina kallon garin Kika San me zakiyi Wanda Kika iya kina da basira,Cele tace gobe ma Sai awara naga har University ce a nan ga hausawanmu nan faca faca ko Ina gobe da Yamma sai awara danwake da safe, Cele washe gari ana gama siyar da danwake ta dawo gida ta yanka awararta ta soya a gida ta zuba a wani botiki ta Kai wajen makarantar duk da nisa Cele tana kaiwa sai kudinta cas ta dawo dauke da Madara ta gari da flavour da komai tana yin wanka tayi Sallah sai tazo tayi Albishir na siyarwa shima makarantar take kaiwa idan zata Kai Awara Mata har maza siye Albishir din nata akeyi,hausawanmu maza Yan makaranta sai son Cele suke kafin kace me Cele tayi suna kowa yace ya sunanta Kawai Cele duk da Cele aka Santa sai samari takeyi amma Ina kudi tazo nema kawai.
Alawar Madara ma yi take ta siyarwa sai Neman kudi takeyi sai da tayi nisa matan da Suka zo Su Samira Suka samu Rufaida Suka ce Cele koya Mana muma sana'ar, Cele da bala'inta tace dake ni na kawoku garin ni wa ya nuna min gari kowa yayi ta kansa ko Ina nake zuwa Kuma ai Kun sani, Yau Awarar Cele da yawa tayi abarta ga shegen tsada amma haka aka siyeta tas ta samu kudi sosai,Albishir ya Kare,Alawar Madara ma haka gidansu ta shigo da kudinta cas tana irgawa a gaban matan gidan sai da ta gama irgawa a gabansu tana wani gadara ta daga rigarta vest ce wacce tun a gida aka Mata aljihu me zip ta saka kudinta,Ogar Agent tace ke a waye kike Kamar kin taba zuwa wata kasar,Cele tace baki ga kalata bane jiki duk shayi tana gyara Riga,dariya sukayi,Cele tace ba time,wanka tayi ta canja doguwar rigar data siya a kasar duk kayansu dama sun wanke su tas, fita tayi ta samu restaurant ita da Kaka ta siya musu abinci me kyau Suka ci abinsu Cele kudinta take ci.

Kowaccensu ta Kama Sana'a suna fama har Suka kwashe wata uku a Sudan Sannan akace su shirya lokacin shigar su Makkah yayi,masu kudi suzo a tafi dasu ta jirgi Wanda basu da kudi Kuma to fa ga mota a hakan ma har ruwa sai an haura ta komi,Cele tace Nawa ne kudin jirgin? Aka fada Mata ta cire nata da na kaka ta bayar, kwashe su aka kaisu can bayan gari waje ne kamar kurkur aka basu uniform ja Riga da wando Kamar yan gidan kaso kowa da number dinsa a jiki a nan ma Sai da Suka kwashe kwanaki sannan ranar da zasu tafi aka fara Kiran number har Cele da Kaka Suka Shige jirgi,na mota ma aka Kira wasu da yawa aka jera su a motoci,Suma kasar akwai kudin da suke karuwa da shi shi yasa suke yarda ana haka ma'aikatan wajen duk Yan kasar Sudan ne.

Cele a jirgi sai zare Ido akeyi da passport dinsu da visa duk an buga musu ta sudan, a hakanma Makkah ta wata state din aka shigar dasu maimakon ta Jiddah sabo da hanyar ta Barauniyar Hanya ce,Cele su a birnin Riyad aka sauke su Kawai aka musu check in duk kudin Aljihun su suke ci a hakan ma, suna fitowa Cele taga birni iya birni ta zazzagi kasar Sudan tas tace ga inda ake arziki tace Kasar da Annabawa sun zauna a cikinta ai ta musamman ce,ga cikamakin Annabawa anan kasar yake,mu Kuwa wanne Annabi ne ya biyo ta kasashenmu,sai masar itama a daban suke map ne ya cuce su ya watso su Africa amma a nan haka suke, akwai wacce aka hada su Cele zata musu jagora zuwa garin Makkah ta fito tace ga Taxi tana jiranmu kuzo muje Suka karasa,Balaraben yace su shiga inda aka Yi rashin sa'a sai kawai Cele ta Fara shiga motar ashe mazane Larabawa a ciki mutum biyu Kawai kafin Kaka ya shiga sunga an rufe motar an fisga a million anyi gaba da Cele ,Kaka ya Fadi ya fashe da kuka Yana shike Nan Jikata ta fada mugun Hannu mene amfanin zuwana Yana ta kuka,Matar da sauran maza da matan hausawa suna bashi baki cewar za a ganta Inshaallah,tace kaga dattijo tashi mu tafi wallahi a state dinnan basa barin baki sai wane da wane sai Wanda ya Isa shike Zama a nan sai ka jawo Mana a kamamu,Kaka Yana kuka yace tunda Naga motar nan baka wuluk glass dinta ma baki wuluk ba a ganin kowa nasan ba Alheri bace wata taxi Suka tare Suka shiga Suka nufi Garin Makkah,Kaka dai cewa yake gwara a kamani a maidani Najeria mene amfanina me Zan iyayi na Sana'a a kasar nan dama da jikata na dogara,wannan zuwa bai min ba shi yasa nace mubi ta Madina garin manzo aka ki ji idan Madina ne su suna kaunar mutane da bako gashi yanzu kun jawo min Ina Zan Sa kaina,sai dai nayi bara Kawai a kasar nan ba wata Sana'a da Zan iya ni bara zanyi na koma almajiri Kaka harda shanye Hannu ya sagale shi yace na koma nakasashe,wani abin idan ya fada dariya ma yake basu.

Cele kuwa tana fara musu ihu tana kururuwa Kawai suka dan hura Mata wani hayaki a Fuska shike nan jikinta ya mutu tana kallon kowa sannan kowa na kallonta duk abinda ake tana gani amma motsi baza ta iya ba ko yatsanta ta gagara motsawa,wani asibiti Suka wuce direct,suna yin waya matar Ahsan Maheerah ta fito sanye da kayan likitocinta tana zuwa da Allurarta cikin sirinji Kawai ta Bude mota Cele tana kallo ta Mata Allurar gaba Daya sai ta koma ganin duhu daga nan bata sake

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login