Showing 24001 words to 27000 words out of 77913 words

Chapter 9 - 'Yar Mahaukaciya

10 Oct 2024

15870

haka kawai haduwar rana tsaka a zo da wanan zancen gashi daga an ganta bata shigen yayan hausa ga ido irin na kyanwa aje tsakar dare ta farka ta cinye mutun,? Gaba daya kowa tsoron Yar Mahaukaciya ya darsu a zuciyarsa


Mubasshir na rakube jikin garu yana kalon yanda da daya daya jama'ar suka fara fashewa suna tafiyarsu sai yan tsirirai su hajiya Marhaba da sauransu , muryar Idriss ta dawo da shi inda ya ce" Aba ka kontar da hankalinka ka cikata haka ni zan fitar da ita



Da hajiya da Mubasshir a tare suka kali Idriss jin furucin bakinsa


Elhaj Ilyass ya ce" Yawa yaron kirki fitar min da anoba daga gida


Yar Mahaukaciya da ta zamto tamkar mutun mutuni , a da da farko tayi tinanin zuwan wanan ranar , aman ganin irin yanda ta samu zama sai tinanin ya kau daga ranta, tabas ta saba da wulakanci, da cin zarafi aman bata taba zaton a wanan ranar haka zata faru da ita ba , furutin Idriss shi ya fi komai daga mata hankali bata san lokacin da wani karfi ya zo mata ba ta Mike daga yashen da take cikin karaji ta ce " Ya isa ,


Ta juyo da idanuwanta da sauran farin ya koma ja, tsakiyar kuwa yake haske haske cikin dakakiyar murya ta ce" *Idriss ba sai ka fitar da ni ba , zan FITA da kaina, ta juya wajen Hajiya ta tsuguna ta kama kafafuwanta ta ce" Ni ba mazinaciya bace , aman kuma ban san ba KO ni mayiya ce KO aljana ce, abu daya na sani nima mutun ce, sanan ni YAR MAHAUKACIYA CE, kiyi hakurin rashina , karki damu da inda zan kwana na saba da wahala, kar kiyi fushi da danki haka Allah ya so , na gode sosai da tarbiyar da kika bani harma kika nuna min nima inada daraja*

Tana gama fadar haka ta jawo hijabinta na makaranta dake rataye saman igiya ta juya cikin nutsuwa ta fito daga gidan su Idriss inda take yi masa kalon karshe






To jama'a ina Yar Mahaukaciya zata nufa? Muje zuwa😁😁😁😁
🇳🇪Belles écrivaines du Niger



*'YAR 👧🏻*

*MAHAUKACIYA👹*

*_Na SAJIDA_*




31

Tafe take bata san inda take jefa kafarta ba , gata dai da ganinta ka san yar banban gida ce KO yanayin jikinta da yanda take haske sai dai fuskarta a mugun hade tamkar hadarin gabas


Mutane sai kalonta suke suna al'ajabin wanan mai ke damunta? Wasun kuwa har tambayarta suke , aman ina ita ba ta tasu take ba


Tun da ta fito yake biye da bayanta a hankali yana son sanin inda zata je , tafiyar yaga ba mai karewa bace hakan yasa ya samu ya shiga gabanta da motarsa daidai wani dan karamin gida na laka

Kasa take kalo ganin mota ta shiga gabanta ya saka ta juya ta fada cikin kofar gidan nan ita duk a tunaninta hanya ce

Da Sauri ya sauko yana kokarin cire Babar rigarsa domin ji yayi kwatakwata tayi masa nauyi , cikin nutsuwa ya kutsa cikin gidan nan inda ya tarar da Yar Mahaukaciya da wata mata tana yi mata tambayar wa take nema , ita kuwa kawai ta tsura mata ido tamkar sabuwar halita


Cikin nutsuwa ya karasa yana fadin " salam kiyi hakuri kanwata ce bata tayi ne


Matar nan ta ce" oyo sanu kinji kiyi hakuri ga yayanki


Yar Mahaukaciya ta dago idanuwanta ta sauke su a fuskar *MUBASSHIR* Wanda shima a lokacin ita yake kalo , suka yi ido hudu da shi

A hankali ya furta " mu tafi yana nuna mata kofa

Tamkar wata karamar yarinya Yar Mahaukaciya ta make kafada tana nufin ba inda zata je


Mubasshir ya hade rai yayi iya yinsa aman firr ta kafe ita fa ba inda zata tafi

Matar nan ta fito itama ta saka baki ake baiwa Yar Mahaukaciya hakuri kan ta shige su tafi aman kamar da kurma suke magana


Mubasshir ya hade rai tamkar bai taba yin dariya ba ya umarci Yar Mahaukaciya da ta fice su tafi , aman ina abinka da Wanda bai iya fushi ba , ita duk gani take idan fa ta bishi za'a koma ne a kuma ci mata mutunci kamar yanda akayi mata yanzu KO ma fin hakan , shi yasa sam ta kasa daga kafarta kuma bata ga abinda zai Sakata daga kafar tata


Mubzsshir ya lumshe ido a ransa ya ce" Ya Allahna ka yafe min taimako zanyi ka fini sanin ba dan wani abin zan tabata ba ,
Kawai sai gani nayi yana tatare hanun rigarsa ya CIRA Yar Mahaukaciya sama ya nufi motarsa da ita , Wace ta zaro ido tana wutsil wutsil din ya sauketa tana yakushinsa tamkar sabon kamu






Shin ina Mubasshir honorable zai nufa da Yar Mahaukaciya? Zata amince ne KO aa? ❤❤❤
🇳🇪Belles écrivaines du Niger



*'YAR 👧🏻*

*MAHAUKACIYA👹*

*_Na SAJIDA_*




32


Tunda ya sakata cikin motar ya zagaya ya shiga ya dauki hanya ita kuwa tsananin tsoro ya hanata dagowa ta kale shi balatana ta tambaye shi inda zai kaita dan haka kawai sai ta hade kanta da gwuiwar ta tana ta sheshekar kuka


Tafiyar da sukayi ta kai ta minti talatin gaba dayanta ta hada zufa domin du ta dababaye jikin nata da katon hijab dinta na makaranta ,


Ji tayi ya ja ya tsaya ta kasa dago fuskarta kawai jiran jin duka take KO wulakanci dan tasan gidan su Idriss din ne kawai ya maidota , ta kai kamar minti biyar a zaune bayan tsayuwar motar tana ta sheshekar kukanta , wani sanyi kamar na busawar iskar Allah du da hijabinta sanan taji wani lalausan hanu wanda da ba dan taji yatsitsai ba da KO ya za'ayi da ita ba zata yarda cewar hanu ne ba , cikin Sauri ta dago kanta dan ganin wanda ya dora hanunsa saman kafadunta

Hajiya Fatimatu Mahaifiyar Mubasshir ce tsaye sai kyali take , ga kwaliya ta sha ga sarka mai kyanli, ga farar fata ga kuma hasken gari hakan ya hadu ya haska fuskarta a idanuwan Yar Mahaukaciya Wace nan take ta gane wanan mata KO ya take ta hada alaka da Dan Aljannah da tsabar kamar da suka yi har ta baci , aman sam bata kawowa ranta cewar ta haife shi ba saboda ita bata da banban jiki sanan du da daga fuskarta zaka gane ta manyanta aman hutu ya hana a gane shekarunta ,


Hajiya Fadimatu ta katsewa Yar Mahaukaciya tinaninta ta hanyar sakar mata murmushi sanan ta kamo hanayenta cikin nutsuwa ta ce " Marhababiki yata , ta juya fuskarta cike da fara'ar da Mubasshir har ya fara kishi ta ce " Son kaga Adu'ata ta karbu KO Allah ya bani ya daidai lokacin da na aurar da dana ,


Mubasshir yayi Murmushin shima ya ce" Maman Mubasshir aure fa kika yiwa Mubasshir ba mutuwa yayi ba , dan haka kar a maye gurbin Mubasshir a zuciyar Maman Mubasshir dan kuwa ba zai taba yarda ba



Mahaifiyar Mubasshir tayi murmushi ta lakaci Hancin Mubasshir ta ce " Kishi? Au kishi kake? To ka zage dantse dan kuwa aiki ya sameka jan aiki kuwa , ta kama Hanun Yar Mahaukaciya wace KO takalmi babu a kafarta sanan jikinta yayi busu busu da kura ta bi wani lungu da ita saboda taron jama'ar gidan ta nufi dakin Mubasshir da ita dan kuwa ita bangarenta jama'ar sunyi yawa sosai



Suna shiga wayar dakin ta fara ringin ta daga tayi salama


Mubasshir ya ce " Maman Mubasshir hajiya ce tayi kira na hadaku kuyi magana tace tana son sanin idan har da gaske kin karbi sha lelenta


Hajiya Fadimatu tayi murmushi jin yanda ya karasa maganar sanan ta amsa Kiran Hajiya Hawau , sun jima suna zantawa sanan hajiya Fadimatu cikin wani irin farin ciki ta ce" Haba , haba Hajiya ai yarda daya ce , da kuma na kowa , sanan tunda ta zamto musulma koda yayanta ashirin ai bai haramta ba , dan haka ina so insha Allah kiyi kokari nan da kwana uku ki zo mu hadu da shi Aban tun kafin ya juya sai ayi KO?



Hajiya Hawau cikin Hamdallah da godiyar ubangiji ta ce " Allah ya saka miki da mafificin alkhairin dake nan gidan duniya da kuma na kiyama, Allah ya sa ki gama da duniya lafiya, Yanda kika kudurci aikata Alkhairi a kan marainiya Allah ya jibanci lamuranki


Hajiya Fadimatu tayi saurin fadin" Amin hajiya aman plz ki dena Gode min na fada miki yiwa kai ne na yarda da ke da zuciya daya , haka suka datse Kiran su dukansu suna farin cikin abinda suka yanke Wanda a tinaninsu hakan shine banban gudumuwar da zasu yi dan taimakon marainiyar Allah wato Yar Mahaukaciya



Cikin nutsuwa ta juyo wajen Yar Mahaukaciya Wace gaba dayanta take tsorace da wanan dakin, ita tunda ta wayi gari ta ganta a gidan duniya bata taba , no bata taba kawowa kusan ranta cewar wai a nan gidan duniya za'a iya tsantsara wanan tsarin haka , Dakin ciki daya ne wani wawakeke sanan du madubi ne ya gewaye dakin sai gadon dake tsakiyar dakin kasan ba kafet jikin tils din kasan hoton Mubasshir ne aka zana da sajensa yana murmushi gaba daya wata kunya ta kamata gani take kawai kalonta ne yake ta kuwa tatare siket dinta ta matse ita kar yaga jikinta ( lol ) aman kuma mamakin da take Wai ina bayi? Sanan ina wajen kaya? Ita tsoroma ya mugun kamata da ace ita kadaice da ba abinda zai hanata ta zare a dakin nan



Hajiya Fadimatu ta kamo hanunta cikin nutsuwa ta jata saman gadon Mubasshir suka zauna a gefen gadon sanan cikin sanyinta da kwarewa wajen kontarwa da mutun hankali ta ce" Rahma, Rahmatullah, mai yayi zafi da aka manta Kiran inalilahi wa'ina ilaihi raj'une ake kukan nan? Shin kin manta fadar Ma'aiki idan ka ga abinda ya kayar maka da gaba KO ya bata maka rai kayi ta maimaita sunayen Allah kana tazbihi kana kusanta da ubangijinka dan samun saukin zuciyar ka ? Domin kinsan ita zuciya a jikin dan Adam Mugun nama ce idan har zuciyar Dan Adam ta baci to fa ba mutun, sai ki ga mutun yana aikata abubuwa irin Wanda KO daba ba zai aikata ba dan kuwa cikin aikinsa tsabar kin Allah zaiyi yawa a ciki , shi kuwa wanan Halaka ne Rahma Tabas Halaka ne



Cikin nutsuwa Yar Mahaukaciya ke kalon Bakin Mahaifiyar Mubasshir wata irin nutsuwa taji tana ratsata wace bata taba jinta cikinta ba hadi da kunya Wace ta rasa ta maicece, da sauri ta sada kanta kasa tana dan murza yatsuntsanta tana raurau da ido



Hajiya Fadimatu tayi murmushi ganin Yar Mahaukaciya tana da kunya ta dago kanta ta ce" Ni sunana Nana Fadimatu sanan ni Mahaifiyar Mubasshir ce kuma ina son zama mahaifiyarki , shin zaki bani wanan damar?


Idanuwan Yar Mahaukaciya suka ciciko da kwallah tana kokarin zubar da hawayen shaukin wanan kalma ta Mahaifiyar Mubasshir


Hajiya Fadimatu tayi Saurin girgiza mata kai ta ce " AF sanan idan abu ya faranta ranta kayi hamdallah ba kayi kuka ba
Ta cire hijabin Yar Mahaukaciya ta dora kanta saman cinyarta a hankali tana yi mata labari har barci mai dadi yayi awon gaba da Yar Mahaukaciya cike da farin cikin wanan rayuwa sabuwa tare da adu'ar Allah ya sa mai dorewa ce








To fa shin mainene abinda su Hajiya Hawau suka yanke ne? Muje zuwa 😘
🇳🇪Belles écrivaines du Niger



*'YAR 👧🏻*

*MAHAUKACIYA👹*

*_Na SAJIDA_*




33


Sosai take bacin ta hankali konce harda ajiyar zuciya, Hajiya Fadimatu ta gyara mata konciya ta Mike a hankali gudun kar ta tashe ta ta koma wajen bakin ta





Bayan wanan tarzomar kowa ya watse aka bar Hajiya Hawau ita kadai domin gaba daya bakin nata sunyi tafiyar su gudun kar a makala musu Yar Mahaukaciya

A boye ta samu wayarta har tayi magana da mahaifiyar Mubasshir , bayan ta gama ne ta fito dan ta tatare tabarmin da ta shinfidawa bakin ta , tana fitowa ta tarar da Fati kawar Yar Mahaukaciya rakube kanta a kasa tana ta tinane tinane


Hajiya Hawau ta karaso a hankali ta zauna kusa da ita ta ce" Fati tinanin mai kike?


Fati ta dago kanta ta kali hajiya sanan cikin gargadar murya ta ce" shin Hajiya ina sister ne? Hajiya dan Allah ki cireni daga cikin duhu cos ina cikin duhu ta karashe zancen da kuka

A hankali hajiya Hawau ta dafa kafadarta ta ce" RAHMA ba mazinaciya bace , sanan mafaifiyarta ba mahaukaciya ba ce, kuma ita marainiya ce sanan ni kakarta ce, Kuma Dan Aljannah yayanta ne , wanene baki fahimta ba a ciki?


Fati ta ce" Kenan AA jikanki ne shima?


Hajiya Hawau kawai ta daga kanta alamar eh

Fati ta sauke nanauyar ajiyar zuciya sanan ta ce" yanzu tana ina Ita din?


Hajiya Hawau ta ce" Tana gidan su Mubasshir dan haka ki mike kiyi wanka zan saka a rakaki wajenta , ki tafiyan mata da kayanta gaba daya kin ji?

Fati ta daga kanta tana farin cikin jin Rahma na gidan su AA Mubasshir ,
Hakan kuwa akayi Hajiya Hawau tayi kira ta shaidawa Mubasshir yayi Kiran securites ya shaida idan za'a kawo wata budurwa baka mai dan tsayi da kaya a shiga da ita ta baya , sanan ya shaidawa Mahaifiyarsa , ita kuwa sai murna ta karu dan Hajiya Fadimatu akoy son yaya mata shi yasa kulun adu'arta Allah ya bata kafin rasuwar mahaifin Mubasshir to bayan rasuwar tasa ma bata daina ba tana fatan Allah ya baiwa Mubasshir sai a bata ta rike sai gashi yau Allah ya bata ya mai kyau haka tayi murmushi tana adu'ar Allah ya tayata riko



Cikin bacinta taji an kankame mata jiki firgigit ta farka tana zare ido domin bata san tayi baci har haka ba , idanuwanta ta shiga murzawa dan gaskatawa kanta Wanda take gani


Fati tayi dariya ta ce" ni ce sis

Yar Mahaukaciya tayi musrmushi ta ce" wa ya kawoki? Ya akayi kika zo ? Kinga abinda ya sameni ko ? A ina..........cikin sauri Fati ta ce" ke ki dan huta da tambayoyin mana , Hajiya ta fada min komai dena daga hankalinki haka kinji


Yar mahaukaciya tayi shiru tana tinanin mai Hajiyar ta fada mata , aman sai ta share bata ce mata komai ba ,

Suna nan zaune Mahaifiyar Mubasshir ta kuma shigowa ta ce" Yar Fadimatu kin farka? A taso ayi wanka domin yama tayi


Yar Mahaukaciya ta ce " ohk mamana tana murmushi


A hankali Mahaifiyar Mubasshir ta nufi daidai wani madubi ta mika hanunta a nitse ta dan shafa wani farin abu , abin mamaki kofa ta bude daga Yar Mahaukaciya har Fati da kalo suka bi Hajiya Fadimatu baki sake uwa zararu sanan ta kuma taba wani bayi biyu suka bude a cikin dakin cikin nutsuwa ta taho ta kuma taba wani abin sai dirowa ta bude ta zaro tapi ta nufi wajen tiraruka ta dauko kala uku du ta zube musu ta ce" kuyi wankan ga salaya, ga kuma wanan kafin ku gama kimtsawa za'a kawo muku kayanku ku saka


Su duka suka amsa mata

Har ta kusa FITA ta dawo ta ce" zaku tafi diner ne?


Fati ta ce" Eh

Yar Mahaukaciya ta ce" aa

Suka kali juna a tare

Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" Kuyi shawara idan kun yanke shawarar sai na turo mai shirya ku


Suka amsa mata da to ta juya ta fita

Tana fita Fati ta zarowa Yar Mahaukaciya ido ta ce " hey😳, for what zaki ce ba zamu tafi ba?


Yar Mahaukaciya ta ce" ki gane sisi idan na tafi kinga abinda ya faru da safe bana so ya kuma faruwa


Fati ta ce" auren yayanki ne , auren gidanku ne, dan kawai wata nonsence bata sonki a wajen sai ki ki tafiya? Sis harda mai shiryamu fa waouh har ina tinanin yanda zamu dawo idan aka shiryamu plz ki amince mu je muma


Haka dai suka zauna suna ta musanyar yawu kan su je KO kar su je








Eyah fans shin Su je din ne KO kar su je??????🤷🏿‍♀
🇳🇪Belles écrivaines du Niger



*'YAR 👧🏻*

*MAHAUKACIYA👹*

*_Na SAJIDA_*




34

Wanka suka shiga kowace ta dau lokacinta , ita dai Fati tana gamawa ta dauro alwalah ta zo ta gabatar da salar Magarib, tana nan zaune tana lazumi Yar Mahaukaciya ta fito ta nufi Jakarta ta buda ta dauki pad ta juya cikin bayin ta saka ta kuma fitowa kanta daure da tawul karami ta lulube jikinta da hijabinta


Sai da Fati tayi sallar Isha sanan ta mike daga saman dardumar ta ninke ta ta tsaya ta zubawa hoton Mubasshir dake zane saman terrace din


Yar Mahaukaciya ta ce" mai kike kalo?


Fati ta ce" sis kinsan Allah gaskiya banga laifin matan da suka yanyanka hanayensu lokacin annabi yusuf , ki duba ki ga irin kyan AA fa sis ni KO da AA kadai aka barni sai nayanyanke hanuna


Yar Mahaukaciya ta bushe da dariya ganin yanda Fati tsakaninta da Allah take bayaninta har cikin zuciyarta yanayin yanda take fitar da zancen

Ta ce" sisi kinsan wani Abu? Ni sam kyan mutun baya rudata wly ke wani lokacin nafi son mutun mai bakar fata cos yafi kyau


Fati tayi mata kalon kin raina ni sanan ta ce" to tayaya kyau zai rude ki ? Ai dan kinsan kina da shi

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login